< 1 Sama’ila 6 >

1 Lokacin da akwatin alkawarin Ubangiji ya kai wata bakwai a ƙasar Filistiyawa.
The people of Philistia kept God’s sacred chest in their area for seven months.
2 Filistiyawa suka kira firistoci da bokaye suka ce, “Me za mu yi da akwatin alkawarin Ubangiji? Ku gaya mana yadda za mu komar da shi inda ya fito.”
Then they summoned their priests and their (diviners/men who practice rituals to find out what would happen in the future). They asked them, “What should we do with the sacred chest of Yahweh? Tell us how we should send it back to its own land.”
3 Suka ce, in za ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra’ila kada ku komar da shi hannu wofi; amma ku tabbata kun aika da hadaya don laifi zuwa wurinsa. Sa’an nan za ku warke ku kuma san dalilin da ya sa bai cire hannunsa a kanku ba.
Those men replied, “Send with it an offering [to show Yahweh that you know that you are] guilty [for having captured the chest], in order that the plague will stop. If you do that, and then if you are healed, you will know that Yahweh is the one who caused you to experience the plague.”
4 Filistiyawa suka ce, “Wace irin hadaya don laifi za mu aika masa?” Suka ce, “Marurai biyar na zinariya da ɓeraye biyar na zinariya bisa ga yawan sarakunan Filistiyawa. Saboda annoba iri ɗaya ce ta buga ku da shugabanninku.
The people of Philistia asked, “What kind of offering should we send?” The men replied, “Make five gold models of the tumors on your skin, and five gold models of rats. Make five of each because that is the same number as the number of your kings, and because the plague has struck both you people and your five kings.
5 Ku yi siffofin marurai da na ɓeraye da suke hallaka gari, ku ba da girma ga Allah na Isra’ila. Wataƙila zai ɗauke hukuncinsa daga gare ku da allolinku da kuma ƙasarku.
Make models that represent the rats and the tumors that are ruining your land. Make them in order to honor the god of the Israeli people. If you do that, perhaps he will stop punishing [IDM] you, and your gods, and your land.
6 Me ya sa kun taurare kanku kamar yadda Masarawa da Fir’auna suka yi? Da ya ba su matsanancin wahala, ba su bar Isra’ilawa suka tafi hanyarsu ba?
Do not be [RHQ] stubborn [IDM] like the Egyptians and their king were. [They did not do what the Israelis’ god told them to do, so he punished them]. After the Israelis’ god finished punishing them very severely, they were glad to allow the Israelis to leave their country [RHQ].
7 “Yanzu fa ku shirya sabon keken shanu da shanu biyu masu ba wa’ya’yansu nono, waɗanda ba a taɓa sa musu karkiya ba. Ku daure keken shanu wa shanun, amma ku tsare’yan maruƙansu a gida.
“So you must build a new cart. Then get two cows that have very recently given birth to calves. They must be cows that have never been hitched to a cart [MTY]. Hitch those cows to the new cart, and take the calves away from their mothers.
8 Ku ɗauki wani akwati ku sa siffofin zinariyan nan a ciki, waɗanda za su zama kyautai na shafen laifi, ku ajiye kusa da Akwati na UBANGIJI. Bayan haka sai ku sa keken shanun da akwatin a hanya, ku bar shi yă tafi.
Put the Israelis’ god’s sacred chest on the cart. Also put in the cart the five gold models of the tumors on your skin and the five gold models of rats. Put them in a small box alongside the sacred chest. They will be an offering to show that you know that you deserved to be punished [for capturing the sacred chest]. Then send [the cows] down the road, [pulling] the cart.
9 Amma ku zuba ido ku ga in ya haura zuwa yankinsa, zuwa Bet-Shemesh, to, Ubangiji ne ya kawo mana babban masifar a kanmu. Amma in bai bi ta nan ba, za mu san cewa ba shi ne ya buge mu ba, tsautsayi ne kawai.”
[Watch the cart as the cows pull it]. If they pull it to Beth-Shemesh [town] in Israel, we will know that it was the Israelis’ god who caused us to experience this plague. But if they do not take it there, we will know that it was not the god [MTY] of the Israelis who has punished us. We will know that it just happened.”
10 Suka yi haka. Suka ɗauki shanun tatsa guda biyu suka ɗaura musu keken shanu, suka tsare’yan maruƙansu a gida.
So the people did what the priests and men who predicted what would happen in the future told them to do. They [made] a cart [and] hitched two cows to it. They took the calves from their mothers.
11 Suka aza akwatin alkawarin Ubangiji a bisa keken shanun tare da akwatin siffofin ɓerayen zinariya da siffofin maruran.
They put in the cart Yahweh’s sacred chest and the box with the models of the gold rats and the tumors.
12 Sai shanun suka miƙe zuwa Bet-Shemesh. Suka bi hanya daidai, ba su juya dama ko hagu ba. Shugabannin Filistiyawa suka bi har zuwa iyakar ƙasar Bet-Shemesh.
Then the cows started walking, and they went straight toward Beth-Shemesh. They stayed on the road, and were mooing all the time. They did not turn to the left or to the right. The five kings of the Philistia area followed the cows until they reached the edge of Beth-Shemesh.
13 A lokacin kuwa mutanen Bet-Shemesh suna girbin alkamansu a kwari da suka ɗaga ido suka hangi akwatin alkawarin Ubangiji, sai suka yi farin ciki ganinsa.
At that time, the people of Beth-Shemesh were harvesting wheat in the valley [outside the city]. [When the cows came along the road], they looked up and saw the sacred chest. They were extremely happy to see it.
14 Keken shanun ya zo filin Yoshuwa a Bet-Shemesh ya tsaya a gefen wani babban dutse. Mutanen suka faskare keken shanun suka miƙa shanun hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
The cows pulled the cart into the field of a man named Joshua, and they stopped alongside a large rock. Several men from the tribe of Levi lifted from the cart the sacred chest and the box containing the gold models of the rats and the tumors, and they put them all on the large rock. Then the people smashed the cart and kindled a fire with the wood [from which the cart had been made]. They slaughtered the cows and burned their bodies/carcasses on the fire to be an offering for Yahweh that would be completely burned. That day the people of Beth-Shemesh offered to Yahweh [many] sacrifices that were completely burned, and [other] sacrifices.
15 Lawiyawa suka saukar da akwatin alkawarin Ubangiji tare da babban akwati mai siffofin zinariya na ɓeraye da marurai suka ajiye su a kan ƙaton dutse. A wannan rana mutanen Bet-Shemesh suka miƙa hadaya ta ƙonawa da waɗansu hadayu ga Ubangiji.
16 Shugabanni biyar na Filistiyawan nan suka ga duk abin da ya faru, suka koma zuwa Ekron a ranar.
The five kings from the Philistia area watched all this, and then they returned to Ekron, that same day.
17 Waɗannan su ne siffofi marurai na zinariya waɗanda Filistiyawa suka aika domin miƙa hadaya don laifi ga Ubangiji, ɗaya domin Ashdod, ɗaya domin Gaza, ɗaya domin Ashkelon, ɗaya domin Gat, ɗaya kuma domin Ekron.
The five gold models of tumors that they sent to be an offering to Yahweh to show that they knew that they deserved to be punished were gifts from [those five kings who were rulers of] Ashdod, Gaza, Ashkelon, Gath, and Ekron [cities].
18 Filistiyawa kuma suka aika da siffofin ɓeraye biyar na zinariya. Yawan ɓerayen sun yi daidai da yawan garuruwan sarakunan nan biyar na Filistiyawa. Garuruwan sun ƙunshi waɗanda aka gina katangar birni kewaye da su, da kuma ƙauyukansu. Babban dutsen da suka ajiye akwatin alkawarin Ubangiji, ya zama shaida har wa yau a filin Yoshuwa a Bet-Shemesh.
The models of the five gold rats were gifts from the people of those five cities and the surrounding towns. The large rock at Beth-Shemesh, on which the [men of the tribe of Levi] set the sacred chest, is still there in the field that belonged to Joshua. When people see it, they remember [what happened there].
19 Amma Allah ya kashe waɗansu mutum saba’in na mutanen Bet-Shemesh domin sun leƙa cikin akwatin alkawarin Ubangiji. Mutane kuwa suka yi makoki domin Ubangiji ya hallaka mutane da yawa.
But seventy men from Beth-Shemesh looked into Yahweh’s sacred chest, and because of that, Yahweh caused them to die. Then the people mourned very much because Yahweh punished [IDM] those men like that.
20 Mutanen Bet-Shemesh suka yi tambaya suka ce, wa zai iya tsaya a gaban Ubangiji Allah Mai Tsarki? Wurin wa akwatin alkawari zai je daga nan?
They said, “No one [RHQ] can (resist the power of/stand in the presence of) Yahweh, our holy God, [and remain alive]! Where can we send the sacred chest?”
21 Sai suka aiki manzanni zuwa Kiriyat Yeyarim suka ce, “Filistiyawa sun komo da akwatin alkawarin Ubangiji, ku zo ku ɗauka ku kai wajenku.”
They sent messengers to the people of Kiriath-Jearim [city] to tell them, “The people of Philistia have returned Yahweh’s sacred chest to us! Come here and take it away!”

< 1 Sama’ila 6 >