< 1 Sama’ila 6 >

1 Lokacin da akwatin alkawarin Ubangiji ya kai wata bakwai a ƙasar Filistiyawa.
Kovčeg Jahvin bijaše sedam mjeseci u zemlji Filistejaca.
2 Filistiyawa suka kira firistoci da bokaye suka ce, “Me za mu yi da akwatin alkawarin Ubangiji? Ku gaya mana yadda za mu komar da shi inda ya fito.”
Tada Filistejci sazvaše svećenike i vrače i zapitaše ih: “Što da radimo s Kovčegom Jahvinim? Poučite nas kako da ga pošaljemo natrag na njegovo mjesto.”
3 Suka ce, in za ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra’ila kada ku komar da shi hannu wofi; amma ku tabbata kun aika da hadaya don laifi zuwa wurinsa. Sa’an nan za ku warke ku kuma san dalilin da ya sa bai cire hannunsa a kanku ba.
Oni odgovoriše: “Ako hoćete vratiti Kovčeg Boga Izraelova, ne šaljite ga natrag prazna nego uza nj pošaljite i naknadnicu. Tada ćete se izliječiti i znat ćete zašto se njegova ruka nije okrenula od vas.”
4 Filistiyawa suka ce, “Wace irin hadaya don laifi za mu aika masa?” Suka ce, “Marurai biyar na zinariya da ɓeraye biyar na zinariya bisa ga yawan sarakunan Filistiyawa. Saboda annoba iri ɗaya ce ta buga ku da shugabanninku.
Oni zapitaše: “Kakvu naknadnicu treba da mu pošaljemo?” Oni odgovoriše: “Prema broju filistejskih knezova, pet zlatnih čireva i pet zlatnih štakora, jer je ista nevolja na vama i na vašim knezovima.
5 Ku yi siffofin marurai da na ɓeraye da suke hallaka gari, ku ba da girma ga Allah na Isra’ila. Wataƙila zai ɗauke hukuncinsa daga gare ku da allolinku da kuma ƙasarku.
Načinite, dakle, likove svojih čireva i likove svojh štakora, koji vam zatiru zemlju, i dajte slavu Bogu Izraelovu. Možda će dignuti ruku svoju od vas, od vaših bogova i od vaše zemlje.
6 Me ya sa kun taurare kanku kamar yadda Masarawa da Fir’auna suka yi? Da ya ba su matsanancin wahala, ba su bar Isra’ilawa suka tafi hanyarsu ba?
Zašto hoćete da vam srce otvrdne kao što je bilo otvrdnulo Egipćanima i faraonu? Kad ih je Bog pritisnuo, nisu li ih onda pustili da odu?
7 “Yanzu fa ku shirya sabon keken shanu da shanu biyu masu ba wa’ya’yansu nono, waɗanda ba a taɓa sa musu karkiya ba. Ku daure keken shanu wa shanun, amma ku tsare’yan maruƙansu a gida.
Pripremite sada jedna nova kola i uzmite dvije krave dojilice koje još nisu nosile jarma: upregnite krave u kola, a njihovu telad odvedite natrag u staju.
8 Ku ɗauki wani akwati ku sa siffofin zinariyan nan a ciki, waɗanda za su zama kyautai na shafen laifi, ku ajiye kusa da Akwati na UBANGIJI. Bayan haka sai ku sa keken shanun da akwatin a hanya, ku bar shi yă tafi.
Tada ćete uzeti Kovčeg Jahvin i staviti ga na kola. Zlatne predmete koje mu prinosite kao žrtvu naknadnicu stavit ćete u kovčežić kraj njega i tako neka pođe.
9 Amma ku zuba ido ku ga in ya haura zuwa yankinsa, zuwa Bet-Shemesh, to, Ubangiji ne ya kawo mana babban masifar a kanmu. Amma in bai bi ta nan ba, za mu san cewa ba shi ne ya buge mu ba, tsautsayi ne kawai.”
Zatim gledajte: ako krene prema svome kraju, put Bet Šemeša, onda je sigurno da nam je on zadao ovo veliko zlo; ako li ne krene tako, znat ćemo da nas nije udarila njegova ruka, nego da nam se to dogodilo slučajno.”
10 Suka yi haka. Suka ɗauki shanun tatsa guda biyu suka ɗaura musu keken shanu, suka tsare’yan maruƙansu a gida.
Ljudi učiniše tako: uzeše dvije krave dojilice i upregoše ih u kola, a njihovu telad zadržaše u staji.
11 Suka aza akwatin alkawarin Ubangiji a bisa keken shanun tare da akwatin siffofin ɓerayen zinariya da siffofin maruran.
Kovčeg Jahvin staviše na kola i kovčežić sa zlatnim štakorima i s likovima svojih čireva.
12 Sai shanun suka miƙe zuwa Bet-Shemesh. Suka bi hanya daidai, ba su juya dama ko hagu ba. Shugabannin Filistiyawa suka bi har zuwa iyakar ƙasar Bet-Shemesh.
Krave udariše ravno cestom prema Bet Šemešu i jednako su išle istim putem, mukale su idući, a nisu skretale ni desno ni lijevo. Filistejski knezovi pratili su ih do granice Bet Šemeša.
13 A lokacin kuwa mutanen Bet-Shemesh suna girbin alkamansu a kwari da suka ɗaga ido suka hangi akwatin alkawarin Ubangiji, sai suka yi farin ciki ganinsa.
Stanovnici Bet Šemeša upravo su bili zabavljeni žetvom pšenice u dolini. Digavši oči, ugledaše Kovčeg i potrčaše mu s veseljem u susret.
14 Keken shanun ya zo filin Yoshuwa a Bet-Shemesh ya tsaya a gefen wani babban dutse. Mutanen suka faskare keken shanun suka miƙa shanun hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
Kad su kola stigla na polje Jošue iz Bet Šemeša, zaustaviše se. Ondje bijaše velik kamen. Tada iscijepaše drvo od kola i prinesoše krave kao žrtvu paljenicu Jahvi.
15 Lawiyawa suka saukar da akwatin alkawarin Ubangiji tare da babban akwati mai siffofin zinariya na ɓeraye da marurai suka ajiye su a kan ƙaton dutse. A wannan rana mutanen Bet-Shemesh suka miƙa hadaya ta ƙonawa da waɗansu hadayu ga Ubangiji.
Leviti bijahu skinuli Kovčeg Jahvin i kovčežić što je bio kraj njega i u kojem su bili zlatni predmeti i sve bijahu stavili na onaj veliki kamen. Stanovnici Bet Šemeša prinosili su toga dana žrtve paljenice i klali žrtve klanice Jahvi.
16 Shugabanni biyar na Filistiyawan nan suka ga duk abin da ya faru, suka koma zuwa Ekron a ranar.
Kad je to vidjelo pet filistejskih knezova, vratiše se u Ekron isti dan.
17 Waɗannan su ne siffofi marurai na zinariya waɗanda Filistiyawa suka aika domin miƙa hadaya don laifi ga Ubangiji, ɗaya domin Ashdod, ɗaya domin Gaza, ɗaya domin Ashkelon, ɗaya domin Gat, ɗaya kuma domin Ekron.
A ovo je pet zlatnih čireva što su ih Filistejci poslali kao žrtvu naknadnicu Jahvi: za Ašdod jedan, za Gazu jedan, za Aškelon jedan, za Gat jedan, za Ekron jedan.
18 Filistiyawa kuma suka aika da siffofin ɓeraye biyar na zinariya. Yawan ɓerayen sun yi daidai da yawan garuruwan sarakunan nan biyar na Filistiyawa. Garuruwan sun ƙunshi waɗanda aka gina katangar birni kewaye da su, da kuma ƙauyukansu. Babban dutsen da suka ajiye akwatin alkawarin Ubangiji, ya zama shaida har wa yau a filin Yoshuwa a Bet-Shemesh.
A zlatnih je štakora bilo toliko koliko svih gradova filistejskih, u svih pet kneževina, od utvrđenih gradova do otvorenih sela. Svjedok je veliki kamen na koji su položili Kovčeg Jahvin i koji još i danas stoji na polju Jošue iz Bet Šemeša.
19 Amma Allah ya kashe waɗansu mutum saba’in na mutanen Bet-Shemesh domin sun leƙa cikin akwatin alkawarin Ubangiji. Mutane kuwa suka yi makoki domin Ubangiji ya hallaka mutane da yawa.
Sinovi Jekonijini nisu se radovali sa stanovnicima Bet Šemeša kad su vidjeli Kovčeg Jahvin. Zato je Jahve pobio sedamdeset ljudi među njima. Narod je tugovao zbog toga što ga je Jahve tako teško iskušao.
20 Mutanen Bet-Shemesh suka yi tambaya suka ce, wa zai iya tsaya a gaban Ubangiji Allah Mai Tsarki? Wurin wa akwatin alkawari zai je daga nan?
Tada ljudi u Bet Šemešu rekoše: “Tko bi mogao opstati pred Jahvom, ovim Svetim Bogom? Kome će otići sada od nas?”
21 Sai suka aiki manzanni zuwa Kiriyat Yeyarim suka ce, “Filistiyawa sun komo da akwatin alkawarin Ubangiji, ku zo ku ɗauka ku kai wajenku.”
I poslaše poslanike stanovnicima Kirjat Jearima i poručiše im: “Filistejci su vratili Kovčeg Jahvin. Dođite i odnesite ga sebi.”

< 1 Sama’ila 6 >