< 1 Sama’ila 5 >

1 Bayan Filistiyawa sun ƙwace akwatin alkawarin Allah, sai suka ɗauke shi daga Ebenezer suka kai shi Ashdod.
Filistejci so vzeli Božjo skrinjo in jo iz Eben Ezerja prinesli v Ašdód.
2 Sa’an nan suka ɗauki akwatin alkawarin suka kai shi cikin haikalin gunkinsu Dagon, suka ajiye kusa da Dagon.
Ko so Filistejci vzeli Božjo skrinjo, so jo prinesli v Dagónovo hišo in jo postavili poleg Dagóna.
3 Kashegari da safe da mutanen Ashdod suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a gaban akwatin alkawarin Ubangiji. Sai suka ɗauki Dagon suka ajiye a wurin zamansa.
Ko so tisti iz Ašdóda naslednji dan zgodaj vstali, glej, Dagón je bil zvrnjen dol k zemlji, na svoj obraz, pred Gospodovo skrinjo. In prijeli so Dagóna in ga ponovno postavili na njegovo mesto.
4 Amma kashegari kuma da safe suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a ƙasa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji! Kansa ya fashe, hannuwansa kuma sun kakkarye sun zube a madogarar ƙofa; jikinsa ne kaɗai ya rage.
Ko so naslednji dan zgodaj zjutraj vstali, glej, Dagón je bil zvrnjen na svojem obrazu na tleh pred Gospodovo skrinjo, in Dagónova glava in obe dlani njegovih rok so bili odsekani na pragu. Samo Dagónov trup mu je preostal.
5 Saboda haka firistocin Dagon da waɗanda suke sujada a haikalin Dagon ba sa taka bakin ƙofar Dagon a Ashdod har wa yau.
Zato niti Dagónovi duhovniki niti kdorkoli, ki pride v Dagónovo hišo, do današnjega dne, ne stopajo na Dagónov prag v Ašdódu.
6 Hannun Ubangiji kuwa ya yi nauyi a bisa Ashdod da kewayenta. Ya kawo hallaka ga dukansu, ya kuma buga su da marurai.
Toda Gospodova roka je bila težka nad tistimi iz Ašdóda in uničeval jih je in jih udaril s hemoroídi, torej Ašdód in njegova mesta.
7 Da mutanen Ashdod suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Lalle Akwatin Alkawarin Allah na Isra’ila ba zai kasance da mu ba, domin hannunsa yana da nauyi a kanmu da bisan Dagon allahnmu.”
Ko so možje iz Ašdóda videli, da je bilo tako, so rekli: »Skrinja Izraelovega Boga naj ne ostane z nami, kajti njegova roka je boleče nad nami in nad našim bogom Dagónom.«
8 Saboda haka suka kira duka shugabannin Filistiyawa suka tambaye su, suka ce, “Me za mu da akwatin alkawarin Allahn Isra’ila?” Sai suka amsa suka ce, “A ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila a kai shi Gat.” Sai suka ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila.
Zato so poslali in k sebi zbrali vse filistejske kneze ter rekli: »Kaj naj storimo s skrinjo Izraelovega Boga?« Odgovorili so: »Naj bo skrinja Izraelovega Boga prenesena v Gat.« In tja so prenesli skrinjo Izraelovega Boga.
9 Amma bayan sun kai shi can, sai hannun Ubangiji ya yi gāba da birnin, aka jefa shi cikin wani mawuyacin hali. Ya buga mutanen birnin da marurai, babba da yaro.
To je bilo tako, da potem, ko so jo odnesli, je bila Gospodova roka zoper mesto z zelo velikim uničenjem in udaril je može iz mesta, tako male, kakor velike in imeli so hemoroíde v svojih skritih delih.
10 Sai suka aika da akwatin alkawarin Allah zuwa Ekron. Yayinda akwatin alkawarin Allah yana shiga cikin Ekron, mutanen Ekron suka yi ihu, suka ce, “An kawo mana akwatin alkawarin Allah na Isra’ila domin yă kashe mu da mutanenmu.”
Zato so Božjo skrinjo poslali v Ekrón. Pripetilo se je, ko je Božja skrinja prišla v Ekrón, da so Ekrónci zavpili, rekoč: »K nam so privedli skrinjo Izraelovega Boga, da ubije nas in naše ljudstvo.«
11 Saboda haka suka kira ga dukan shugabannin Filistiyawa suka ce, “Ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra’ila inda ya fito; in ba haka ba zai kashe mu da mutanenmu.” Gama mutuwa ta cika garin da tsoro. Hannun Allah ya yi nauyi a kansa.
Tako so poslali in zbrali skupaj vse filistejske kneze in rekli: »Pošljite proč skrinjo Izraelovega Boga in naj ponovno gre na svoj kraj, da ne ubije nas in našega ljudstva, « kajti tam je bilo v vsem mestu smrtonosno uničenje. Božja roka je bila tam zelo težka.
12 Waɗanda ba su mutu ba kuwa, sun kamu da marurai. Kukan birnin kuwa ta hau har zuwa sama.
Možje, ki niso umrli, so bili udarjeni s hemoroídi in krik mesta je šel gor do neba.

< 1 Sama’ila 5 >