< 1 Sama’ila 5 >

1 Bayan Filistiyawa sun ƙwace akwatin alkawarin Allah, sai suka ɗauke shi daga Ebenezer suka kai shi Ashdod.
Filistrene tok Guds ark og førte den fra Eben-Eser til Asdod.
2 Sa’an nan suka ɗauki akwatin alkawarin suka kai shi cikin haikalin gunkinsu Dagon, suka ajiye kusa da Dagon.
Der tok filistrene Guds ark og førte den inn i Dagons hus og stilte den op ved siden av Dagon.
3 Kashegari da safe da mutanen Ashdod suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a gaban akwatin alkawarin Ubangiji. Sai suka ɗauki Dagon suka ajiye a wurin zamansa.
Tidlig den følgende dag fikk asdodittene se at Dagon var falt ned med ansiktet mot jorden foran Herrens ark; og de tok Dagon og satte ham igjen på hans plass.
4 Amma kashegari kuma da safe suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a ƙasa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji! Kansa ya fashe, hannuwansa kuma sun kakkarye sun zube a madogarar ƙofa; jikinsa ne kaɗai ya rage.
Men tidlig om morgenen den næste dag fikk de se at Dagon var falt ned med ansiktet mot jorden foran Herrens ark, og at Dagons hode og begge hans hender lå avhugget på dørtreskelen; bare kroppen var tilbake av Dagon.
5 Saboda haka firistocin Dagon da waɗanda suke sujada a haikalin Dagon ba sa taka bakin ƙofar Dagon a Ashdod har wa yau.
Derfor er det at Dagons prester og alle som går inn i Dagons hus, like til denne dag ikke treder på Dagons dørtreskel i Asdod.
6 Hannun Ubangiji kuwa ya yi nauyi a bisa Ashdod da kewayenta. Ya kawo hallaka ga dukansu, ya kuma buga su da marurai.
Og Herrens hånd lå tungt på asdodittene, og han ødela dem og slo dem med bylder, både i Asdod selv og i de omliggende bygder.
7 Da mutanen Ashdod suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Lalle Akwatin Alkawarin Allah na Isra’ila ba zai kasance da mu ba, domin hannunsa yana da nauyi a kanmu da bisan Dagon allahnmu.”
Da Asdods menn så at det gikk således, sa de: Israels Guds ark skal ikke bli hos oss; for hans hånd ligger hårdt på oss og på Dagon vår gud.
8 Saboda haka suka kira duka shugabannin Filistiyawa suka tambaye su, suka ce, “Me za mu da akwatin alkawarin Allahn Isra’ila?” Sai suka amsa suka ce, “A ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila a kai shi Gat.” Sai suka ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila.
Og de sendte bud og samlet alle filistrenes høvdinger hos sig og sa: Hvad skal vi gjøre med Israels Guds ark? De svarte: La Israels Guds ark bli flyttet til Gat! Så flyttet de Israels Guds ark dit.
9 Amma bayan sun kai shi can, sai hannun Ubangiji ya yi gāba da birnin, aka jefa shi cikin wani mawuyacin hali. Ya buga mutanen birnin da marurai, babba da yaro.
Men efterat de hadde flyttet den dit, kom Herrens hånd over byen og voldte stor forferdelse, og han slo byens folk, både små og store, så det brøt bylder ut på dem.
10 Sai suka aika da akwatin alkawarin Allah zuwa Ekron. Yayinda akwatin alkawarin Allah yana shiga cikin Ekron, mutanen Ekron suka yi ihu, suka ce, “An kawo mana akwatin alkawarin Allah na Isra’ila domin yă kashe mu da mutanenmu.”
Da sendte de Guds ark til Ekron. Men da Guds ark kom til Ekron, da skrek ekronittene: De har flyttet Israels Guds ark hit til mig for å drepe mig og mitt folk.
11 Saboda haka suka kira ga dukan shugabannin Filistiyawa suka ce, “Ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra’ila inda ya fito; in ba haka ba zai kashe mu da mutanenmu.” Gama mutuwa ta cika garin da tsoro. Hannun Allah ya yi nauyi a kansa.
Og de sendte bud og samlet alle filistrenes høvdinger og sa: Send Israels Guds ark bort, og la den komme tilbake til sin plass, så den ikke skal drepe mig og mitt folk! For det var kommet en dødsens forferdelse over hele byen; Herrens hånd lå meget tungt på den.
12 Waɗanda ba su mutu ba kuwa, sun kamu da marurai. Kukan birnin kuwa ta hau har zuwa sama.
De menn som ikke døde, blev slått med bylder, og skriket fra byen steg op til himmelen.

< 1 Sama’ila 5 >