< 1 Sama’ila 5 >

1 Bayan Filistiyawa sun ƙwace akwatin alkawarin Allah, sai suka ɗauke shi daga Ebenezer suka kai shi Ashdod.
LAWE aku la ko Pilisetia i ka pahu o ke Akua, a halihali aku la mai Ebenezera aku a hiki i Asedoda.
2 Sa’an nan suka ɗauki akwatin alkawarin suka kai shi cikin haikalin gunkinsu Dagon, suka ajiye kusa da Dagon.
A lawe ae la ko Pilisetia i ka pahu o ke Akua, a hali aku la iloko o ka hale o Dagona, a waiho ma ka aoao o Dagona.
3 Kashegari da safe da mutanen Ashdod suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a gaban akwatin alkawarin Ubangiji. Sai suka ɗauki Dagon suka ajiye a wurin zamansa.
Ia la iho, ala ae la ko Asedoda i kakahiaka nui, aia hoi, ua hina iho la o Dagona ilalo ke alo ma ka honua imua o ka pahu o Iehova. Lawe aku la lakou ia Dagona, a hooku hou ia ia ma kona wahi.
4 Amma kashegari kuma da safe suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a ƙasa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji! Kansa ya fashe, hannuwansa kuma sun kakkarye sun zube a madogarar ƙofa; jikinsa ne kaɗai ya rage.
A ia la ae, ala hou ae la lakou i kakahiaka nui, aia hoi, ua hina iho la o Dagona ilalo ke alo ma ka honua imua o ka pahu o Iehova; a o ke poo o Dagona, a me kona mau lima elua, ua hemo ma ka paepae, a o ka ia wale no i koe ia ia.
5 Saboda haka firistocin Dagon da waɗanda suke sujada a haikalin Dagon ba sa taka bakin ƙofar Dagon a Ashdod har wa yau.
No ia mea, o na kahuna a Dagona, a me na mea a pau e hele maloko o ka hale o Dagona, aole lakou e hehi maluna o ka paepae o Dagona ma Asedoda, a hiki i keia wa.
6 Hannun Ubangiji kuwa ya yi nauyi a bisa Ashdod da kewayenta. Ya kawo hallaka ga dukansu, ya kuma buga su da marurai.
A ua kaumaha ka lima o Iehova maluna o ko Asedoda, a luku mai oia ia lakou, a hahau mai ia lakou i ka mai hikoko, i ko Asedoda a me ko laila wahi a puni.
7 Da mutanen Ashdod suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Lalle Akwatin Alkawarin Allah na Isra’ila ba zai kasance da mu ba, domin hannunsa yana da nauyi a kanmu da bisan Dagon allahnmu.”
A ike aku la na kanaka o Asedoda i ka mea i hanaia pela, i ae la lakou, Aole e noho me kakou ka pahu o ke Akua o ka Iseraela: no ka mea, ua kaumaha kona lima maluna o kakou, a maluna o Dagona ko kakou akua.
8 Saboda haka suka kira duka shugabannin Filistiyawa suka tambaye su, suka ce, “Me za mu da akwatin alkawarin Allahn Isra’ila?” Sai suka amsa suka ce, “A ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila a kai shi Gat.” Sai suka ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila.
Hoouna aku la lakou e houluulu i na haku a pau o ko Pilisetia io lakou la, ninau aku la ia lakou, Heaha ka makou e hana aku ai i ka pahu o ke Akua o ka Iseraela? I mai la lakou, E laweia'ku ka pahu o ke Akua o ka Iseraela ma Gata. A lawe aku la lakou i ka pahu o ke Akua o ka Iseraela ilaila.
9 Amma bayan sun kai shi can, sai hannun Ubangiji ya yi gāba da birnin, aka jefa shi cikin wani mawuyacin hali. Ya buga mutanen birnin da marurai, babba da yaro.
A mahope o ka lakou lawe ana ku ia mea malaila, ku e mai la ka lima o Iehova i ua kulanakauhale la me ka luku nui loa; a hahau mai ia i ua kanaka o ke kulanakauhale, i ka mea uuku, a me ka mea nui, a poha iho la ko lakou puupuu koko.
10 Sai suka aika da akwatin alkawarin Allah zuwa Ekron. Yayinda akwatin alkawarin Allah yana shiga cikin Ekron, mutanen Ekron suka yi ihu, suka ce, “An kawo mana akwatin alkawarin Allah na Isra’ila domin yă kashe mu da mutanenmu.”
No ia mea, lawe aku la lakou i ka pahu o ke Akua i Ekerona. A hiki aku la ka pahu o ke Akua ma Ekerona, auwe iho la ko Ekerona, i ka i ana ae, Ua lawe mai lakou i ka pahu o ke Akua o ka Iseraela io kakou nei e pepehi ia kakou a me ko kakou poe kanaka.
11 Saboda haka suka kira ga dukan shugabannin Filistiyawa suka ce, “Ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra’ila inda ya fito; in ba haka ba zai kashe mu da mutanenmu.” Gama mutuwa ta cika garin da tsoro. Hannun Allah ya yi nauyi a kansa.
No ia hoi, hoouna aku la lakou e houluulu i na haku a pau o ko Pilisetia, i aku la, E lawe aku i ka pahu o ke Akua o ka Iseraela, a e hoihoi aku ma kona wahi, i ole ai ia e pepehi mai ia makou a me ko makou poe kanaka: no ka mea, he make nui ma ke kulanakauhale a pau; ua kaumaha loa ka lima o ke Akua malaila.
12 Waɗanda ba su mutu ba kuwa, sun kamu da marurai. Kukan birnin kuwa ta hau har zuwa sama.
A o na kanaka aole i make, loohia lakou e ka mai hikoko; a pii ae la ka uwe o ua kulanakauhale la i ka lani.

< 1 Sama’ila 5 >