< 1 Sama’ila 5 >

1 Bayan Filistiyawa sun ƙwace akwatin alkawarin Allah, sai suka ɗauke shi daga Ebenezer suka kai shi Ashdod.
Og Filisterne toge Guds Ark, og de førte den fra Eben-Ezer til Asdod.
2 Sa’an nan suka ɗauki akwatin alkawarin suka kai shi cikin haikalin gunkinsu Dagon, suka ajiye kusa da Dagon.
Og Filisterne toge Guds Ark og førte den ind i Dagons Hus, og de satte den hos Dagon.
3 Kashegari da safe da mutanen Ashdod suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a gaban akwatin alkawarin Ubangiji. Sai suka ɗauki Dagon suka ajiye a wurin zamansa.
Men Asdoditerne stode tidlig op den næste Dag, og se, Dagon var falden paa sit Ansigt til Jorden foran Herrens Ark; og de toge Dagon og satte ham paa sit Sted igen.
4 Amma kashegari kuma da safe suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a ƙasa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji! Kansa ya fashe, hannuwansa kuma sun kakkarye sun zube a madogarar ƙofa; jikinsa ne kaɗai ya rage.
Og de stode den næste Dag tidlig op om Morgenen, og se, Dagon var falden paa sit Ansigt til Jorden foran Herrens Ark; og Dagons Hoved og begge hans Hænder laa afhugne paa Dørtærskelen, kun Dagons Krop stod der endnu.
5 Saboda haka firistocin Dagon da waɗanda suke sujada a haikalin Dagon ba sa taka bakin ƙofar Dagon a Ashdod har wa yau.
Derfor træde hverken Dagons Præster eller nogen af dem, som gaa ind i Dagons Hus, paa Dagons Dørtærskel i Asdod indtil denne Dag.
6 Hannun Ubangiji kuwa ya yi nauyi a bisa Ashdod da kewayenta. Ya kawo hallaka ga dukansu, ya kuma buga su da marurai.
Og Herrens Haand blev svar over Asdoditerne, og han ødelagde dem; og han slog Folket i Asdod og i dens Landemærker med Bylder.
7 Da mutanen Ashdod suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Lalle Akwatin Alkawarin Allah na Isra’ila ba zai kasance da mu ba, domin hannunsa yana da nauyi a kanmu da bisan Dagon allahnmu.”
Der Folket i Asdod saa, at det gik saaledes til, da sagde de: Israels Guds Ark skal ikke blive hos os; thi hans Haand er svar over os og over Dagon, vor Gud.
8 Saboda haka suka kira duka shugabannin Filistiyawa suka tambaye su, suka ce, “Me za mu da akwatin alkawarin Allahn Isra’ila?” Sai suka amsa suka ce, “A ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila a kai shi Gat.” Sai suka ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila.
Og de sendte hen og samlede alle Filisternes Fyrster til sig og sagde: Hvad skulle vi gøre med Israels Guds Ark? Og de sagde: Lader Israels Guds Ark flyttes om til Gath; og de bragte Israels Guds Ark om.
9 Amma bayan sun kai shi can, sai hannun Ubangiji ya yi gāba da birnin, aka jefa shi cikin wani mawuyacin hali. Ya buga mutanen birnin da marurai, babba da yaro.
Og det skete, efter at de havde bragt den om, da var Herrens Haand mod Staden med en saare stor Forstyrrelse, og han slog Folket i Staden, baade smaa og store, og der brød Bylder ud paa dem.
10 Sai suka aika da akwatin alkawarin Allah zuwa Ekron. Yayinda akwatin alkawarin Allah yana shiga cikin Ekron, mutanen Ekron suka yi ihu, suka ce, “An kawo mana akwatin alkawarin Allah na Isra’ila domin yă kashe mu da mutanenmu.”
Da sendte de Guds Ark til Ekron; og det skete, der Guds Ark kom til Ekron, da raabte Ekroniterne og sagde: De have baaret Israels Guds Ark om til mig for at slaa mig og mit Folk ihjel.
11 Saboda haka suka kira ga dukan shugabannin Filistiyawa suka ce, “Ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra’ila inda ya fito; in ba haka ba zai kashe mu da mutanenmu.” Gama mutuwa ta cika garin da tsoro. Hannun Allah ya yi nauyi a kansa.
Saa sendte de hen og samlede alle Filisternes Fyrster og sagde: Sender Israels Guds Ark hen, at den kan komme igen til sit Sted og ikke slaa mig og mit Folk ihjel; thi der var en døds Forstyrrelse i hele Staden; Guds Haand var der meget svar.
12 Waɗanda ba su mutu ba kuwa, sun kamu da marurai. Kukan birnin kuwa ta hau har zuwa sama.
Og de Mennesker, som ikke døde, bleve slagne med Bylder; og Skriget fra Staden steg op til Himmelen.

< 1 Sama’ila 5 >