< 1 Sama’ila 4 >

1 Duk sa’ad da Sama’ila ya yi magana dukan Isra’ila sukan saurare shi. Isra’ilawa suka fita yaƙi da Filistiyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani a Ebenezer, Filistiyawa kuma a Afek.
La parole de Samuel fut adressée à tout Israël. Israël sortit contre les Philistins pour combattre, et il campa près d'Ébénézer; les Philistins campèrent à Aphek.
2 Filistiyawa suka tunƙuro mayaƙansu domin su sadu da Isra’ilawa, yaƙi kuwa ya yi tsanani har Isra’ilawa suka sha kashi a hannun Filistiyawa. Filistiyawa suka kashe Isra’ilawa kusan mutum dubu huɗu a bakin dāgā.
Les Philistins se rangèrent en bataille contre Israël. Lorsqu'ils se battirent, Israël fut vaincu par les Philistins, qui tuèrent en campagne environ quatre mille hommes de l'armée.
3 Lokacin da mayaƙan suka komo sansani, dattawan Isra’ilawa suka yi tambaya suka ce, “Me ya sa Ubangiji ya sa muka sha ɗibga a hannun Filistiyawa? Bari mu kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Shilo. Domin yă tafi tare da mu yă ba mu nasara kan abokan gābanmu.”
Lorsque le peuple fut rentré dans le camp, les anciens d'Israël dirent: « Pourquoi Yahvé nous a-t-il vaincus aujourd'hui devant les Philistins? Allons chercher l'arche de l'alliance de Yahvé à Silo et apportons-la à nous, afin qu'elle vienne au milieu de nous et nous sauve de la main de nos ennemis. »
4 Saboda haka mutanen suka aika waɗansu maza zuwa Shilo, suka kuwa tafi suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji Maɗaukaki wanda yake zaune tsakanin Kerubobi.’Ya’yan Eli biyun nan Hofni da Finehas suna wurin tare da akwatin alkawarin Ubangiji.
Et le peuple envoya à Silo, et l'on apporta de là l'arche de l'alliance de Yahvé des armées, qui est assis au-dessus des chérubins; et les deux fils d'Eli, Hophni et Phinées, étaient là avec l'arche de l'alliance de Dieu.
5 Da aka shigo da akwatin alkawarin Ubangiji a cikin sansani, sai Isra’ilawa suka tā da babbar murya har ƙasa ta jijjiga.
Lorsque l'arche de l'alliance de Yahvé entra dans le camp, tout Israël poussa de grands cris, au point que la terre en résonna.
6 Da jin wannan, Filistiyawa suka yi tambaya suka ce, “Me ke kawo wannan ihu mai ƙarfi haka a sansanin Isra’ilawa?” Da suka gane cewa akwatin alkawarin Ubangiji ne ya shiga sansanin,
Lorsque les Philistins entendirent le bruit de ce cri, ils dirent: « Que signifie le bruit de ce grand cri dans le camp des Hébreux? ». Ils comprirent que l'arche de Yahvé était entrée dans le camp.
7 sai Filistiyawa suka ji tsoro, suka ce, “Wani allah ya shiga cikin sansanin. Mun shiga uku! Ba a taɓa yin wani abu haka ba.
Les Philistins eurent peur, car ils disaient: « Dieu est entré dans le camp. » Ils dirent: « Malheur à nous! Car il n'y a jamais eu de chose semblable auparavant.
8 Kaiton mu! Wa zai kuɓutar da mu daga hannun waɗannan manyan alloli? Su ne allolin da suka buga Masarawa da irin annoba masu yawa a jeji.
Malheur à nous! Qui nous délivrera de la main de ces dieux puissants? Ce sont ces dieux qui ont frappé les Égyptiens de toutes sortes de plaies dans le désert.
9 Ku yi ƙarfin hali, ku yi mazantaka, ku Filistiyawa, domin kada ku zama bayin Ibraniyawa kamar yadda suke a gare ku. Ku yi mazantaka, ku yi yaƙi.”
Fortifiez-vous et comportez-vous comme des hommes, Philistins, pour ne pas être les esclaves des Hébreux, comme ils l'ont été pour vous. Fortifiez-vous comme des hommes, et combattez! »
10 Saboda haka Filistiyawa suka yi yaƙi, Isra’ilawa kuwa suka sha ɗibga, kowane mutum kuwa ya gudu zuwa tentinsa. Kisan kuwa ya yi muni ƙwarai. Isra’ilawa sun rasa mayaƙa dubu talatin.
Les Philistins combattirent, Israël fut vaincu, et chacun s'enfuit dans sa tente. Il y eut un très grand carnage, car trente mille fantassins d'Israël tombèrent.
11 Aka ƙwace akwatin alkawarin Ubangiji. Aka kuma kashe’ya’yan Eli biyu, Hofni da Finehas.
L'arche de Dieu fut prise, et les deux fils d'Eli, Hophni et Phinées, furent tués.
12 A wannan rana wani mutumin Benyamin ya ruga da bakin dāgā ya shigo Shilo, taguwarsa a yage, kansa kuma a rufe da ƙasa.
Un homme de Benjamin sortit de l'armée et arriva à Silo le même jour, les vêtements déchirés et la tête couverte de terre.
13 Da ya iso sai ga Eli zaune a kujera kusa da hanya yana kallo, domin tsoron da yake da shi saboda akwatin alkawarin Allah. Da mutumin ya shigo a garin ya ba da labarin abin da ya faru sai dukan gari ya ruɗe da ihu.
Lorsqu'il arriva, voici qu'Eli était assis sur son siège, au bord du chemin, à regarder, car son cœur tremblait pour l'arche de Dieu. Lorsque l'homme entra dans la ville et en fit le récit, toute la ville poussa des cris.
14 Eli ya ji ihun ya yi tambaya ya ce, mene ne dalilin wannan ihu? Mutumin ya rugo wurin Eli,
Lorsque Eli entendit le bruit des cris, il dit: « Que signifie le bruit de ce tumulte? » L'homme se hâta, et vint le dire à Eli.
15 wanda yake da shekaru tasa’in da takwas da haihuwa, idanunsa kuma ƙarfi ya ƙare, baya iya gani.
Or, Eli était âgé de quatre-vingt-dix-huit ans. Ses yeux étaient fixes, de sorte qu'il ne pouvait pas voir.
16 Mutumin ya gaya wa Eli cewa, “Shigowata ke nan daga bakin dāgā. Na kuɓuce daga can yau ɗin nan.” Eli ya ce, “Me ya faru da’ya’yana?”
L'homme dit à Eli: « Je suis celui qui est sorti de l'armée, et je me suis enfui aujourd'hui de l'armée. » Il a dit: « Comment ça s'est passé, mon fils? »
17 Mutumin da ya kawo labarin ya ce, “Isra’ilawa sun gudu a gaban Filistiyawa, mayaƙan kuma sun sha mummunar ɗibga.’Ya’yanka Hofni da Finehas su ma sun mutu. Aka kuma ƙwace akwatin alkawarin Allah.”
Celui qui apportait la nouvelle répondit: « Israël a fui devant les Philistins, et il y a aussi eu un grand massacre parmi le peuple. Tes deux fils aussi, Hophni et Phinées, sont morts, et l'arche de Dieu a été capturée. »
18 Da ya ambaci akwatin alkawarin Allah, sai Eli ya fāɗi da baya daga kujeransa kusa da ƙofa, wuyarsa ta karye, ya kuma mutu domin ya tsufa ƙwarai. Ya yi shugabancin Isra’ila shekaru arba’in.
Lorsqu'il parla de l'arche de Dieu, Eli tomba de son siège en arrière, du côté de la porte; son cou se brisa, et il mourut, car il était vieux et pesant. Il avait jugé Israël pendant quarante ans.
19 Matar Finehas, ɗansa tana da ciki a lokacin ta kuma kusa haihuwa. Sa’ad da ta ji labari cewa an ƙwace akwatin alkawarin Allah, ta kuma labarin surukinta da mijinta sun mutu, sai ta shiga naƙuda, ta kuma haihu. Amma naƙuda ta sha ƙarfinta.
Sa belle-fille, la femme de Phinées, était enceinte, sur le point d'accoucher. Lorsqu'elle apprit la nouvelle de la prise de l'arche de Dieu et de la mort de son beau-père et de son mari, elle se courba et accoucha, car ses douleurs la surprirent.
20 Da tana mutuwa, matan da suke lura da ita suka ce, “Kada ki karaya kin haifi ɗa namiji.” Amma ba tă ba da amsa ko tă kula ba.
Vers le moment où elle mourut, les femmes qui se tenaient près d'elle lui dirent: « N'aie pas peur, car tu as donné naissance à un fils. » Mais elle ne répondit pas et n'y fit pas attention.
21 Ta ba wa yaron suna Ikabod, ma’ana “Ɗaukaka ta rabu da Isra’ila”, domin an ƙwace akwatin alkawarin Allah, domin kuma mutuwar surukinta da na mijinta.
Elle donna à l'enfant le nom d'Ichabod, en disant: « La gloire s'est retirée d'Israël », parce que l'arche de Dieu avait été prise, et à cause de son beau-père et de son mari.
22 Ta ce, “Ɗaukaka ta rabu da Isra’ila, gama an ƙwace akwatin alkawarin Allah.”
Elle dit: « La gloire a disparu d'Israël, car l'arche de Dieu a été prise. »

< 1 Sama’ila 4 >