< 1 Sama’ila 4 >
1 Duk sa’ad da Sama’ila ya yi magana dukan Isra’ila sukan saurare shi. Isra’ilawa suka fita yaƙi da Filistiyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani a Ebenezer, Filistiyawa kuma a Afek.
And it was doon in tho daies Filisteis camen to gidere in to batel; for Israel yede out ayens Filisteis in to batel, and settiden tentis bisidis the stoon of help. Forsothe Filisteis camen in to Aphet,
2 Filistiyawa suka tunƙuro mayaƙansu domin su sadu da Isra’ilawa, yaƙi kuwa ya yi tsanani har Isra’ilawa suka sha kashi a hannun Filistiyawa. Filistiyawa suka kashe Isra’ilawa kusan mutum dubu huɗu a bakin dāgā.
and maden redi scheltrun ayens Israel. Sotheli whanne the batel was bigunnun, Israel turned backis to Filisteis; and as foure thousynde of men weren slayn in that batel `euery where bi feeldis;
3 Lokacin da mayaƙan suka komo sansani, dattawan Isra’ilawa suka yi tambaya suka ce, “Me ya sa Ubangiji ya sa muka sha ɗibga a hannun Filistiyawa? Bari mu kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Shilo. Domin yă tafi tare da mu yă ba mu nasara kan abokan gābanmu.”
and the puple of Israel turnede ayen to tentis. And the grettere men in birthe of Israel seiden, Whi hath the Lord smyte vs to dai bifore Filisteis? Brynge we to vs fro Silo the arke of boond of pees of the Lord, and come it in to the myddis of vs, that it saue vs fro the hond of oure enemyes.
4 Saboda haka mutanen suka aika waɗansu maza zuwa Shilo, suka kuwa tafi suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji Maɗaukaki wanda yake zaune tsakanin Kerubobi.’Ya’yan Eli biyun nan Hofni da Finehas suna wurin tare da akwatin alkawarin Ubangiji.
Therfor the puple sente in to Silo, and thei token fro thennus the arke of boond of pees of the Lord of oostis, `that sat on cherubyn. And Ophym and Fynees, twei sones of Heli, weren with the arke of boond of pees of the Lord.
5 Da aka shigo da akwatin alkawarin Ubangiji a cikin sansani, sai Isra’ilawa suka tā da babbar murya har ƙasa ta jijjiga.
And whanne the arke of boond of pees of the Lord hadde come in to the castels, al Israel criede with grete cry, and the erthe sownede.
6 Da jin wannan, Filistiyawa suka yi tambaya suka ce, “Me ke kawo wannan ihu mai ƙarfi haka a sansanin Isra’ilawa?” Da suka gane cewa akwatin alkawarin Ubangiji ne ya shiga sansanin,
And Filisteis herden the vois of cry, and seiden, What is this vois of greet cry in the castels of Ebrews? And thei knewen, that the arke of boond of pees of the Lord hadde come in to castels.
7 sai Filistiyawa suka ji tsoro, suka ce, “Wani allah ya shiga cikin sansanin. Mun shiga uku! Ba a taɓa yin wani abu haka ba.
And Filisteis dredden, and seiden, God is come in to `the castels; and thei weiliden, and seiden, Wo to vs!
8 Kaiton mu! Wa zai kuɓutar da mu daga hannun waɗannan manyan alloli? Su ne allolin da suka buga Masarawa da irin annoba masu yawa a jeji.
for so greet ful ioiyng was not yistirdai, and the thridde day passid; wo to vs! who schal kepe vs fro the hond of `these hiye goddis? these ben the goddis, that smytiden Egipt with al veniaunce in deseert.
9 Ku yi ƙarfin hali, ku yi mazantaka, ku Filistiyawa, domin kada ku zama bayin Ibraniyawa kamar yadda suke a gare ku. Ku yi mazantaka, ku yi yaƙi.”
Filisteis, be ye coumfortid, and be ye men, serue ye not Ebrews, as thei serueden vs; be ye coumfortid, and fiyte ye.
10 Saboda haka Filistiyawa suka yi yaƙi, Isra’ilawa kuwa suka sha ɗibga, kowane mutum kuwa ya gudu zuwa tentinsa. Kisan kuwa ya yi muni ƙwarai. Isra’ilawa sun rasa mayaƙa dubu talatin.
Therfor Filisteis fouyten, and Israel was slayn, and ech man flei in to his tabernacle; and a ful greet veniaunce was maad, and thretti thousynde of foot men of Israel felden doun.
11 Aka ƙwace akwatin alkawarin Ubangiji. Aka kuma kashe’ya’yan Eli biyu, Hofni da Finehas.
And the arke of God was takun; and, twei sones of Heli, Ophym and Fynees, weren deed.
12 A wannan rana wani mutumin Benyamin ya ruga da bakin dāgā ya shigo Shilo, taguwarsa a yage, kansa kuma a rufe da ƙasa.
Sotheli a man of Beniamyn ran fro the scheltrun, and cam in to Silo in that dai, with his cloth torent and his heed bispreynt with dust; and whanne he was comen,
13 Da ya iso sai ga Eli zaune a kujera kusa da hanya yana kallo, domin tsoron da yake da shi saboda akwatin alkawarin Allah. Da mutumin ya shigo a garin ya ba da labarin abin da ya faru sai dukan gari ya ruɗe da ihu.
Heli sat `on an hiye seete, `and bihelde ayens the weie; for his herte was dredyng for the arke of the Lord. Sotheli aftir that thilke man entride, he telde to the citee, and al the citee yellide.
14 Eli ya ji ihun ya yi tambaya ya ce, mene ne dalilin wannan ihu? Mutumin ya rugo wurin Eli,
And Heli herde the soun of cry, and seide, What is this sown of this noise? And he hastide, and cam, and telde to Heli.
15 wanda yake da shekaru tasa’in da takwas da haihuwa, idanunsa kuma ƙarfi ya ƙare, baya iya gani.
Forsothe Heli was of foure score yeer and eiytene, and hise iyen dasiwiden, and he myyte not se.
16 Mutumin ya gaya wa Eli cewa, “Shigowata ke nan daga bakin dāgā. Na kuɓuce daga can yau ɗin nan.” Eli ya ce, “Me ya faru da’ya’yana?”
And he seide to Heli, Y am that cam fro batel, and Y am that flei to dai fro the scheltrun. To whom Ely seide, My sone, what is doon?
17 Mutumin da ya kawo labarin ya ce, “Isra’ilawa sun gudu a gaban Filistiyawa, mayaƙan kuma sun sha mummunar ɗibga.’Ya’yanka Hofni da Finehas su ma sun mutu. Aka kuma ƙwace akwatin alkawarin Allah.”
Forsothe he that telde answeride, and seide, Israel flei bifor Filisteis, and a greet fal is maad in the puple; ferthermore and thi twey sones, Ophym and Fynees, ben deed, and the arke of God is takun.
18 Da ya ambaci akwatin alkawarin Allah, sai Eli ya fāɗi da baya daga kujeransa kusa da ƙofa, wuyarsa ta karye, ya kuma mutu domin ya tsufa ƙwarai. Ya yi shugabancin Isra’ila shekaru arba’in.
And whanne he hadde nemyd the arke of God, Hely felde fro `the hiye seete bacward bisidis the dore, and `was deed; for the nollis weren brokun. For he was an eld man, and of greet age; and he demyde Israel bi fourti yeer.
19 Matar Finehas, ɗansa tana da ciki a lokacin ta kuma kusa haihuwa. Sa’ad da ta ji labari cewa an ƙwace akwatin alkawarin Allah, ta kuma labarin surukinta da mijinta sun mutu, sai ta shiga naƙuda, ta kuma haihu. Amma naƙuda ta sha ƙarfinta.
Forsothe his douyter in lawe, `the wijf of Finees, was with childe, and niy the child bering; and whanne `the message was herd that the arke of God was takun, and that hir fadir in lawe was deed, and hir hosebonde, sche bowide hir silf, and childide; for sodeyn sorewis felden in to hir.
20 Da tana mutuwa, matan da suke lura da ita suka ce, “Kada ki karaya kin haifi ɗa namiji.” Amma ba tă ba da amsa ko tă kula ba.
Sotheli in that moment of hir deeth, wymmen that stoden aboute hir, seiden to hir, Drede thou not, for thou hast childid a sone. And sche answeride not to hem, for nether `sche perseyuede.
21 Ta ba wa yaron suna Ikabod, ma’ana “Ɗaukaka ta rabu da Isra’ila”, domin an ƙwace akwatin alkawarin Allah, domin kuma mutuwar surukinta da na mijinta.
And sche clepide the child Ichaboth, and seide, The glorie of the Lord is translatid fro Israel, for the arke of God is takun; and for hir fadir in lawe and for hir hosebonde sche seide,
22 Ta ce, “Ɗaukaka ta rabu da Isra’ila, gama an ƙwace akwatin alkawarin Allah.”
The glorie of God is translatid fro Israel, for the arke of God is takun.