< 1 Sama’ila 4 >

1 Duk sa’ad da Sama’ila ya yi magana dukan Isra’ila sukan saurare shi. Isra’ilawa suka fita yaƙi da Filistiyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani a Ebenezer, Filistiyawa kuma a Afek.
Now at that time the Philistines came together to make war against Israel, and the men of Israel went out to war against the Philistines and took up their position at the side of Eben-ezer: and the Philistines put their forces in position in Aphek.
2 Filistiyawa suka tunƙuro mayaƙansu domin su sadu da Isra’ilawa, yaƙi kuwa ya yi tsanani har Isra’ilawa suka sha kashi a hannun Filistiyawa. Filistiyawa suka kashe Isra’ilawa kusan mutum dubu huɗu a bakin dāgā.
And the Philistines put their forces in order against Israel, and the fighting was hard, and Israel was overcome by the Philistines, who put to the sword about four thousand of their army in the field.
3 Lokacin da mayaƙan suka komo sansani, dattawan Isra’ilawa suka yi tambaya suka ce, “Me ya sa Ubangiji ya sa muka sha ɗibga a hannun Filistiyawa? Bari mu kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Shilo. Domin yă tafi tare da mu yă ba mu nasara kan abokan gābanmu.”
And when the people came back to their tents, the responsible men of Israel said, Why has the Lord let the Philistines overcome us today? Let us get the ark of the Lord's agreement here from Shiloh, so that it may be with us and give us salvation from the hands of those who are against us.
4 Saboda haka mutanen suka aika waɗansu maza zuwa Shilo, suka kuwa tafi suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji Maɗaukaki wanda yake zaune tsakanin Kerubobi.’Ya’yan Eli biyun nan Hofni da Finehas suna wurin tare da akwatin alkawarin Ubangiji.
So the people sent to Shiloh and got the ark of the agreement of the Lord of armies whose resting-place is between the winged ones; and Hophni and Phinehas, the two sons of Eli, were there with the ark of God's agreement.
5 Da aka shigo da akwatin alkawarin Ubangiji a cikin sansani, sai Isra’ilawa suka tā da babbar murya har ƙasa ta jijjiga.
And when the ark of the Lord's agreement came into the tent-circle, all Israel gave a great cry, so that the earth was sounding with it.
6 Da jin wannan, Filistiyawa suka yi tambaya suka ce, “Me ke kawo wannan ihu mai ƙarfi haka a sansanin Isra’ilawa?” Da suka gane cewa akwatin alkawarin Ubangiji ne ya shiga sansanin,
And the Philistines, hearing the noise of their cry, said, What is this great cry among the tents of the Hebrews? Then it became clear to them that the ark of the Lord had come to the tent-circle.
7 sai Filistiyawa suka ji tsoro, suka ce, “Wani allah ya shiga cikin sansanin. Mun shiga uku! Ba a taɓa yin wani abu haka ba.
And the Philistines, full of fear, said, God has come into their tents. And they said, Trouble is ours! for never before has such a thing been seen.
8 Kaiton mu! Wa zai kuɓutar da mu daga hannun waɗannan manyan alloli? Su ne allolin da suka buga Masarawa da irin annoba masu yawa a jeji.
Trouble is ours! Who will give us salvation from the hands of these great gods? These are the gods who sent all sorts of blows on the Egyptians in the waste land.
9 Ku yi ƙarfin hali, ku yi mazantaka, ku Filistiyawa, domin kada ku zama bayin Ibraniyawa kamar yadda suke a gare ku. Ku yi mazantaka, ku yi yaƙi.”
Be strong, O Philistines, be men! Do not be servants to the Hebrews as they have been to you: go forward to the fight without fear.
10 Saboda haka Filistiyawa suka yi yaƙi, Isra’ilawa kuwa suka sha ɗibga, kowane mutum kuwa ya gudu zuwa tentinsa. Kisan kuwa ya yi muni ƙwarai. Isra’ilawa sun rasa mayaƙa dubu talatin.
So the Philistines went to the fight, and Israel was overcome, and every man went in flight to his tent: and great was the destruction, for thirty thousand footmen of Israel were put to the sword.
11 Aka ƙwace akwatin alkawarin Ubangiji. Aka kuma kashe’ya’yan Eli biyu, Hofni da Finehas.
And the ark of God was taken; and Hophni and Phinehas, the sons of Eli, were put to the sword.
12 A wannan rana wani mutumin Benyamin ya ruga da bakin dāgā ya shigo Shilo, taguwarsa a yage, kansa kuma a rufe da ƙasa.
And a man of Benjamin went running from the fight and came to Shiloh the same day with his clothing out of order and earth on his head.
13 Da ya iso sai ga Eli zaune a kujera kusa da hanya yana kallo, domin tsoron da yake da shi saboda akwatin alkawarin Allah. Da mutumin ya shigo a garin ya ba da labarin abin da ya faru sai dukan gari ya ruɗe da ihu.
And when he came, Eli was seated by the wayside watching: and in his heart was fear for the ark of God. And when the man came into the town and gave the news, there was a great outcry.
14 Eli ya ji ihun ya yi tambaya ya ce, mene ne dalilin wannan ihu? Mutumin ya rugo wurin Eli,
And Eli, hearing the noise and the cries, said, What is the reason of this outcry? And the man came quickly and gave the news to Eli.
15 wanda yake da shekaru tasa’in da takwas da haihuwa, idanunsa kuma ƙarfi ya ƙare, baya iya gani.
Now Eli was ninety-eight years old, and his eyes were fixed so that he was not able to see.
16 Mutumin ya gaya wa Eli cewa, “Shigowata ke nan daga bakin dāgā. Na kuɓuce daga can yau ɗin nan.” Eli ya ce, “Me ya faru da’ya’yana?”
And the man said to Eli, I have come from the army and have come in flight today from the fight. And he said, How did it go, my son?
17 Mutumin da ya kawo labarin ya ce, “Isra’ilawa sun gudu a gaban Filistiyawa, mayaƙan kuma sun sha mummunar ɗibga.’Ya’yanka Hofni da Finehas su ma sun mutu. Aka kuma ƙwace akwatin alkawarin Allah.”
And the man said, Israel went in flight from the Philistines, and there has been great destruction among the people, and your two sons, Hophni and Phinehas, are dead, and the ark of God has been taken.
18 Da ya ambaci akwatin alkawarin Allah, sai Eli ya fāɗi da baya daga kujeransa kusa da ƙofa, wuyarsa ta karye, ya kuma mutu domin ya tsufa ƙwarai. Ya yi shugabancin Isra’ila shekaru arba’in.
And at these words about the ark of God, Eli, falling back off his seat by the side of the doorway into the town, came down on the earth so that his neck was broken and death overtook him, for he was an old man and of great weight. He had been judging Israel for forty years.
19 Matar Finehas, ɗansa tana da ciki a lokacin ta kuma kusa haihuwa. Sa’ad da ta ji labari cewa an ƙwace akwatin alkawarin Allah, ta kuma labarin surukinta da mijinta sun mutu, sai ta shiga naƙuda, ta kuma haihu. Amma naƙuda ta sha ƙarfinta.
And his daughter-in-law, the wife of Phinehas, was with child and near the time when she would give birth; and when she had the news that the ark of God had been taken and that her father-in-law and her husband were dead, her pains came on her suddenly and she gave birth.
20 Da tana mutuwa, matan da suke lura da ita suka ce, “Kada ki karaya kin haifi ɗa namiji.” Amma ba tă ba da amsa ko tă kula ba.
And when she was very near death the women who were with her said, Have no fear, for you have given birth to a son. But she made no answer and gave no attention to it.
21 Ta ba wa yaron suna Ikabod, ma’ana “Ɗaukaka ta rabu da Isra’ila”, domin an ƙwace akwatin alkawarin Allah, domin kuma mutuwar surukinta da na mijinta.
And she gave the child the name of Ichabod, saying, The glory has gone from Israel: because the ark of God was taken and because of her father-in-law and her husband.
22 Ta ce, “Ɗaukaka ta rabu da Isra’ila, gama an ƙwace akwatin alkawarin Allah.”
And she said, The glory is gone from Israel, for the ark of God has been taken.

< 1 Sama’ila 4 >