< 1 Sama’ila 31 >
1 Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra’ilawa, sai Isra’ilawa suka gudu a gaban Filistiyawa, aka kuma karkashe da yawa a dutsen Gilbowa.
Now the Philistines fought against Israel. The men of Israel fled from before the Philistines and fell down dead on Mount Gilboa.
2 Filistiyawa suka abka wa Shawulu da’ya’yansa maza, suka kashe’ya’yan Shawulu. Yonatan da Abinadab da Malki-Shuwa.
The Philistines closely pursued Saul and his sons. The Philistines killed Jonathan, Abinadab, and Malki-Shua, his sons.
3 Yaƙin ya yi zafi ƙwarai kewaye da Shawulu, har maharba suka ji masa ciwo sosai bayan sun sha ƙarfinsa.
The battle went heavily against Saul, and the archers overtook him. He was in severe pain because of them.
4 Sai Shawulu ya ce wa mai ɗauka masa makami, “Ka zare takobinka ka soke ni, kada waɗannan marasa kaciya su zo su ci mini mutunci, su kashe ni.” Amma mai ɗaukan makaman bai yarda ba don ya ji tsoro sosai. Sai Shawulu ya zāre takobinsa ya soki kansa.
Then Saul said to his armor bearer, “Draw your sword and thrust me through with it. Otherwise, these uncircumcised will come and abuse me.” But his armor bearer would not, for he was very afraid. So Saul took his own sword and fell on it.
5 Da mai ɗaukar makamai ya ga Shawulu ya mutu, sai shi ma ya zāre takobinsa ya soki kansa ya mutu.
When his armor bearer saw that Saul was dead, he likewise fell on his sword and died with him.
6 Shawulu da yaransa uku da mai ɗaukar makamansa da dukan mutanensa suka mutu a rana ɗaya.
So Saul died, his three sons, and his armor bearer—these men all died together that same day.
7 Sa’ad da Isra’ilawa na bakin kwari da waɗanda suke hayin Urdun suka ga sojojin Isra’ila suna gudu, Shawulu da yaransa uku kuma duk sun mutu, sai suka bar mallakansu suka sheƙa da gudu. Filistiyawa kuwa suka zo suka mamaye wuraren.
When the men of Israel who were on the other side of the valley, and those beyond the Jordan, saw that the men of Israel had fled, and that Saul and his sons were dead, they abandoned their cities and fled, and the Philistines came and lived in them.
8 Kashegari, da Filistiyawa suka zo domin su washe kayan matattun, sai suka tarar Shawulu da’ya’yansa uku duk sun mutu, a dutsen Gilbowa.
It came about on the next day, when the Philistines came to strip the dead, that they found Saul and his three sons fallen on Mount Gilboa.
9 Suka sare kansa suka tuɓe makamansa, suka aika manzanni a dukan ƙasar Filistiyawa, su ba da labarin a haikalin allolinsu da cikin mutanensu.
They cut off his head and stripped off his armor, and sent messengers into the land of the Philistines throughout to carry the news to their idols' temples and to the people.
10 Suka ajiye makaman Shawulu a cikin haikalin gumakan Ashtarot. Suka kafa gawarsa a kan katanga Bet-Shan.
They put his armor in the temple of the Ashtoreths, and they fastened his body to the city wall of Beth Shan.
11 Sa’ad da mutanen Yabesh Gileyad suka sami labarin abin da Filistiyawa suka yi wa Shawulu.
When the inhabitants of Jabesh Gilead heard of what the Philistines had done to Saul,
12 Sai dukan jarumawansu suka tashi cikin dare suka tafi Bet-Shan suka saukar da gawar Shawulu da na’ya’yansa daga kan katangan Bet-Shan suka tafi Yabesh inda suka ƙone su.
all the fighting men arose and went all night and took the body of Saul and the bodies of his sons from the wall of Beth Shan. They went to Jabesh and burned them there.
13 Sai suka kwashi ƙasusuwansu suka binne a gindin itace tsamiya a Yabesh, suka kuma yi azumi kwana bakwai.
Then they took their bones and buried them under a tamarisk tree in Jabesh, and fasted for seven days.