< 1 Sama’ila 31 >

1 Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra’ilawa, sai Isra’ilawa suka gudu a gaban Filistiyawa, aka kuma karkashe da yawa a dutsen Gilbowa.
Now the Philistines fought against Israel; and the men of Israel fled from before the Philistines, and there fell down [many] slain on mount Gilboa'.
2 Filistiyawa suka abka wa Shawulu da’ya’yansa maza, suka kashe’ya’yan Shawulu. Yonatan da Abinadab da Malki-Shuwa.
And the Philistines overtook Saul and his sons; and the Philistines smote Jonathan, and Abinadab, and Malkishua', the sons of Saul.
3 Yaƙin ya yi zafi ƙwarai kewaye da Shawulu, har maharba suka ji masa ciwo sosai bayan sun sha ƙarfinsa.
And the battle was heavy against Saul, and he was found by the archers, the men with bows; and he was greatly in dread of the archers.
4 Sai Shawulu ya ce wa mai ɗauka masa makami, “Ka zare takobinka ka soke ni, kada waɗannan marasa kaciya su zo su ci mini mutunci, su kashe ni.” Amma mai ɗaukan makaman bai yarda ba don ya ji tsoro sosai. Sai Shawulu ya zāre takobinsa ya soki kansa.
And Saul said unto his armor-bearer, Draw thy sword, and thrust me through therewith; lest these uncircumcised come and thrust me through, and wantonly ill-use me. But his armor-bearer would not; for he was greatly afraid; wherefore Saul took the sword, and fell upon it.
5 Da mai ɗaukar makamai ya ga Shawulu ya mutu, sai shi ma ya zāre takobinsa ya soki kansa ya mutu.
And when his armor-bearer saw that Saul was dead, then fell he likewise upon his sword, and died with him.
6 Shawulu da yaransa uku da mai ɗaukar makamansa da dukan mutanensa suka mutu a rana ɗaya.
Thus died Saul, and his three sons, and his armor-bearer, also all his men, on that same day together.
7 Sa’ad da Isra’ilawa na bakin kwari da waɗanda suke hayin Urdun suka ga sojojin Isra’ila suna gudu, Shawulu da yaransa uku kuma duk sun mutu, sai suka bar mallakansu suka sheƙa da gudu. Filistiyawa kuwa suka zo suka mamaye wuraren.
And when the men of Israel that were on the other side of the valley, and those that were on the other side of the Jordan, saw that the men of Israel had fled, and that Saul and his sons had died: they forsook the cities, and fled away; and the Philistines came and dwelt in them.
8 Kashegari, da Filistiyawa suka zo domin su washe kayan matattun, sai suka tarar Shawulu da’ya’yansa uku duk sun mutu, a dutsen Gilbowa.
And it came to pass on the morrow, that the Philistines came to strip the slain; and they found Saul and his three sons fallen on mount Gilboa'.
9 Suka sare kansa suka tuɓe makamansa, suka aika manzanni a dukan ƙasar Filistiyawa, su ba da labarin a haikalin allolinsu da cikin mutanensu.
And they cut off his head, and stripped off his armor, and sent it into the land of the Philistines round about, to publish it in the house of their idols, and among the people.
10 Suka ajiye makaman Shawulu a cikin haikalin gumakan Ashtarot. Suka kafa gawarsa a kan katanga Bet-Shan.
And they put his armor in the house of 'Ashtaroth; and his body they fastened to the wall of Beth-shan.
11 Sa’ad da mutanen Yabesh Gileyad suka sami labarin abin da Filistiyawa suka yi wa Shawulu.
And when the inhabitants of Yabeshgil'ad heard concerning him that which the Philistines had done to Saul:
12 Sai dukan jarumawansu suka tashi cikin dare suka tafi Bet-Shan suka saukar da gawar Shawulu da na’ya’yansa daga kan katangan Bet-Shan suka tafi Yabesh inda suka ƙone su.
Then arose all the valiant men, and walked all the night, and took the body of Saul and the bodies of his sons from the wall of Beth-shan, and they came to Yabesh, and burnt them there.
13 Sai suka kwashi ƙasusuwansu suka binne a gindin itace tsamiya a Yabesh, suka kuma yi azumi kwana bakwai.
And they took their bones, and buried them under the tamarisk-tree at Yabesh, and they fasted seven days.

< 1 Sama’ila 31 >