< 1 Sama’ila 30 >

1 A rana ta uku, Dawuda da mutanensa suka isa Ziklag, sai suka tarar Amalekawa sun riga sun kawo wa Negeb da Ziklag hari. Suka cinye Ziklag, suka ƙone ta,
Le troisième jour, David et ses hommes arrivèrent à Tsiklag. Les Amalécites avaient fait une incursion dans le Sud et à Tsiklag, ils avaient frappé Tsiklag et l'avaient incendiée,
2 suka kwashe mata, yara da tsofaffi da dukan abubuwan da suke cikin garin. Ba su kashe kowa ba, amma suka kwashe su, suka tafi.
et ils avaient fait prisonniers les femmes et tous ceux qui s'y trouvaient, petits et grands. Ils n'en tuèrent aucun, mais les emportèrent et s'en allèrent.
3 Da Dawuda da mutanensa suka isa Ziklag suka tarar an ƙone garin, an kuma kwashe matansu, da’ya’yansu mata, da kuma’ya’yansu maza ganima,
Lorsque David et ses hommes arrivèrent à la ville, voici qu'elle était brûlée par le feu; leurs femmes, leurs fils et leurs filles avaient été emmenés captifs.
4 sai Dawuda da mutanensa suka yi kuka, suka yi ta kuka har sai da ƙarfinsu ya ƙare.
Alors David et le peuple qui était avec lui élevèrent la voix et pleurèrent jusqu'à ce qu'ils n'aient plus la force de pleurer.
5 An kama matan Dawuda, wato, Ahinowam daga Yezireyel da Abigiyel matar Nabal mutumin Karmel wanda ya rasu.
Les deux femmes de David furent emmenées en captivité: Ahinoam, la Jizreelite, et Abigaïl, la femme de Nabal, le Carmélite.
6 Dawuda kuwa ya damu ƙwarai domin mutanensa suna niyyar su jajjefe shi da duwatsu, kowannensu ransa ya ɓace saboda’ya’yansa maza da mata, amma Dawuda ya sami ƙarfafawa a cikin Ubangiji Allahnsa.
David était dans une grande angoisse, car le peuple parlait de le lapider, car l'âme de tout le peuple était affligée, chacun pour ses fils et pour ses filles; mais David se fortifiait en Yahvé, son Dieu.
7 Sai Dawuda ya ce wa Abiyatar firist, ɗan Ahimelek, “Kawo mini efod.” Sai Abiyatar ya kawo masa.
David dit au prêtre Abiathar, fils d'Ahimélec: « Apporte-moi l'éphod, je te prie. » Abiathar apporta l'éphod à David.
8 Dawuda kuwa ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In bi bayan’yan harin nan? Zan ci musu?” Ubangiji ya ce, “Bi su, gama za ka ci musu, ka ƙwato abin da suka kwashe.”
David consulta Yahvé en disant: « Si je poursuis cette troupe, l'atteindrai-je? » Il lui répondit: « Poursuis, car tu les rattraperas sûrement, et tu les récupéreras tous sans faute. »
9 Dawuda da mutanensa ɗari shida suka kama hanya, da suka kai Kwarin Besor, waɗansunsu suka tsaya a can.
Et David partit, lui et les six cents hommes qui étaient avec lui, et il arriva au torrent de Besor, où étaient restés ceux qui étaient restés en arrière.
10 Dawuda ya ci gaba da mutane ɗari huɗu, don mutane ɗari biyu sun gaji sosai har sun kāsa ƙetare rafin Besor.
David poursuivit sa route avec quatre cents hommes, car deux cents hommes restèrent en arrière, qui étaient si faibles qu'ils ne purent franchir le torrent de Besor.
11 Suka sami wani mutumin Masar a fili suka kawo shi wurin Dawuda. Suka ba shi abinci ya ci, suka kuma ba shi ruwa ya sha.
Ils trouvèrent un Égyptien dans les champs, l'amenèrent à David, lui donnèrent du pain, et il mangea, et lui donnèrent de l'eau à boire.
12 Suka ba shi saura wainan’ya’yan ɓaure da kuma wainan’ya’yan inabi, ya ci ya sami ƙarfi. Gama bai ci ba, bai sha ba, har yini uku da dare uku.
Ils lui donnèrent un morceau d'un gâteau de figues et deux grappes de raisins secs. Quand il eut mangé, son esprit revint à lui, car il n'avait pas mangé de pain ni bu d'eau depuis trois jours et trois nuits.
13 Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Wane ne ubangidanka, kuma daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni mutumin Masar ne, bawan wani mutumin Amalek. Maigidana ya ƙyale ni sa’ad da na yi rashin lafiya kwanaki ukun da suka wuce.
David lui demanda: « A qui appartiens-tu? D'où viens-tu? » Il dit: « Je suis un jeune homme d'Égypte, serviteur d'un Amalécite; mon maître m'a abandonné, car il y a trois jours, je suis tombé malade.
14 Mun kai hari a Negeb ta Keretawa ta Yahuda, da Negeb ta Kaleb, muka kuma ƙone Ziklag.”
Nous avons fait une incursion dans le sud des Kéréthiens, dans ce qui appartient à Juda et dans le sud de Caleb, et nous avons brûlé Ziklag par le feu. »
15 Dawuda ya ce masa, “Za ka iya kai ni wurin maharan nan?” Ya ce, “Idan ka rantse mini da Allah, ba za ka kashe ni ba, ba kuwa za ka mai da ni wurin ubangidana ba, sai in kai ka inda maharan suke.”
David lui dit: « Veux-tu me faire descendre dans cette troupe? » Il lui dit: « Jure-moi par Dieu que tu ne me tueras pas et que tu ne me livreras pas aux mains de mon maître, et je te ferai descendre dans cette troupe. »
16 Ya bi da Dawuda har zuwa can, sai ga su a baje ko’ina a ƙasa, suna ci, suna sha, suna annashuwa saboda yawan ganimar da suka kwashe daga ƙasar Filistiyawa da ƙasar Yahuda.
Quand il l'eut fait descendre, voici qu'ils se répandirent sur toute la surface du sol, mangeant, buvant et dansant, à cause de tout le grand butin qu'ils avaient enlevé du pays des Philistins et du pays de Juda.
17 Dawuda ya yaƙe su tun daga fāɗuwar rana har yammar kashegari. Ba ko ɗaya da ya tsira sai samari ɗari huɗu waɗanda suka tsere a kan raƙuma.
David les frappa depuis le crépuscule jusqu'au soir du jour suivant. Pas un seul d'entre eux n'en sortit, à l'exception de quatre cents jeunes gens qui montèrent sur des chameaux et s'enfuirent.
18 Dawuda ya ƙwato kome da Amalekawa suka kwashe tare da matarsa biyu.
David récupéra tout ce que les Amalécites avaient pris, et il sauva ses deux femmes.
19 Babu abin da ya ɓace, Dawuda ya dawo da kowa, manya da ƙanana,’yan maza da’yan mata duka, da dukan abubuwan da Amalekawa suka kwashe.
Il ne leur manquait rien, ni petit ni grand, ni fils ni filles, ni butin, ni rien de ce qu'ils avaient pris. David les ramena tous.
20 Ya kuma ƙwato garkunan tumaki, da na awaki, da na shanu. Mutanensa suka koro shanun, suka yi gaba, suka ce, “Wannan shi ne ganimar Dawuda.”
David prit tous les troupeaux de bœufs et de vaches, qu'ils conduisirent devant les autres bêtes, et il dit: « Voici le butin de David. »
21 Da Dawuda ya zo wurin mutum ɗari biyu ɗin nan waɗanda suka tafke, suka kāsa binsa, waɗanda aka bari a bakin Kwarin Besor, sai suka taryi Dawuda da mutanensa da suka tafi tare da shi. Sa’ad da Dawuda ya zo kusa da su, sai ya gaishe su.
David arriva auprès des deux cents hommes qui étaient si faibles qu'ils ne pouvaient pas suivre David, qu'ils avaient aussi fait séjourner au torrent de Besor; et ils sortirent à la rencontre de David et du peuple qui était avec lui. Lorsque David s'approcha du peuple, il le salua.
22 Sai dukan mugaye da marasa kirki daga cikin mutanen da suka tafi tare da Dawuda suka ce, “Tun da yake ba su tafi tare da mu ba, ba za mu ba su kome daga cikin ganimar da muka ƙwato ba, sai dai kowane mutum yă ɗauki matarsa da’ya’yansa yă tafi.”
Alors tous les méchants et les vauriens de ceux qui étaient allés avec David prirent la parole et dirent: « Parce qu'ils n'ont pas marché avec nous, nous ne leur donnerons rien du butin que nous avons récupéré, si ce n'est à chacun sa femme et ses enfants, afin qu'il les conduise et s'en aille. »
23 Dawuda ya ce, “A’a,’yan’uwana ba za ku yi haka da abin da Ubangiji ya ba mu ba. Ya tsare mu, ya kuma bashe sojojin da suka yi gāba da mu a hannuwanmu.
David dit alors: « N'agissez pas ainsi, mes frères, avec ce que l'Éternel nous a donné, qui nous a préservés et qui a livré entre nos mains la troupe qui était venue contre nous.
24 Wa zai goyi bayanku a kan wannan al’amari? Wanda ya tafi wurin yaƙi da wanda ya zauna wurin kaya, rabonsu zai zama daidai.”
Qui vous écoutera dans cette affaire? Car, de même que sa part est celle de celui qui descend au combat, de même sa part sera celle de celui qui reste avec les bagages. Ils auront la même part. »
25 Dawuda ya sa wannan tă zama dawwammamiyar farilla ga Isra’ila tun daga wannan rana har yă zuwa yau.
Il en fut ainsi à partir de ce jour, et il en fit une loi et une ordonnance pour Israël jusqu'à ce jour.
26 Da Dawuda ya iso Ziklag, sai ya aika wa abokansa, dattawan Yahuda da rabo daga cikin ganimar ya ce, “Ga kyauta dominku, daga cikin ganimar maƙiyan Ubangiji.”
Lorsque David arriva à Ziklag, il envoya une partie du butin aux anciens de Juda, même à ses amis, en disant: « Voici un présent pour vous, tiré du butin des ennemis de l'Éternel. »
27 Kyautar domin waɗanda suke a Betel, da Ramot ta Negeb, da Yattir,
Il l'envoya à ceux qui étaient à Béthel, à ceux qui étaient à Ramoth du Sud, à ceux qui étaient à Jattir,
28 da Arower, da Sifmot, da Eshtemowa,
à ceux qui étaient à Arœr, à ceux qui étaient à Siphmoth, à ceux qui étaient à Eshtemoa,
29 da Rakal, da garuruwan Yerameyelawa, da garuruwan Keniyawa,
à ceux qui étaient à Racal, à ceux qui étaient dans les villes des Jerahmeelites, à ceux qui étaient dans les villes des Kenites,
30 da Horma, da Bor-Ashan, da Atak,
à ceux qui étaient à Horma, à ceux qui étaient à Borashan, à ceux qui étaient à Athach,
31 da Hebron, da dukan wuraren da Dawuda da mutanensa suka taɓa zagawa.
à ceux qui étaient à Hébron, et à tous les endroits où David lui-même et ses hommes avaient l'habitude de séjourner.

< 1 Sama’ila 30 >