< 1 Sama’ila 30 >

1 A rana ta uku, Dawuda da mutanensa suka isa Ziklag, sai suka tarar Amalekawa sun riga sun kawo wa Negeb da Ziklag hari. Suka cinye Ziklag, suka ƙone ta,
And it came to pass when David and his men came to Ziklag on the third day, that the 'Amalekites had invaded the south, and Ziklag, and smitten Ziklag, and burnt it with fire;
2 suka kwashe mata, yara da tsofaffi da dukan abubuwan da suke cikin garin. Ba su kashe kowa ba, amma suka kwashe su, suka tafi.
And had taken captive the women that were therein, both great and small: they had not slain any one, but had led them off, and gone on their way.
3 Da Dawuda da mutanensa suka isa Ziklag suka tarar an ƙone garin, an kuma kwashe matansu, da’ya’yansu mata, da kuma’ya’yansu maza ganima,
When therefore David and his men came to the city, behold, it was burnt with fire; and their wives, and their sons, and their daughters, had been taken captive.
4 sai Dawuda da mutanensa suka yi kuka, suka yi ta kuka har sai da ƙarfinsu ya ƙare.
And David and the people that were with him lifted up their voice and wept, until they had no more power to weep.
5 An kama matan Dawuda, wato, Ahinowam daga Yezireyel da Abigiyel matar Nabal mutumin Karmel wanda ya rasu.
And the two wives of David were also taken captive, Achino'am the Yizre'elitess, and Abigayil the wife of Nabal the Carmelite.
6 Dawuda kuwa ya damu ƙwarai domin mutanensa suna niyyar su jajjefe shi da duwatsu, kowannensu ransa ya ɓace saboda’ya’yansa maza da mata, amma Dawuda ya sami ƙarfafawa a cikin Ubangiji Allahnsa.
And David was greatly distressed; for the people spoke of stoning him, because the soul of all the people was imbittered, every man for his sons and for his daughters; but David fortified himself in the Lord his God.
7 Sai Dawuda ya ce wa Abiyatar firist, ɗan Ahimelek, “Kawo mini efod.” Sai Abiyatar ya kawo masa.
And David said to Ebyathar the priest, the son of Achimelech, Bring hither, I pray thee, unto me the ephod. And Ebyathar brought the ephod near unto David.
8 Dawuda kuwa ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In bi bayan’yan harin nan? Zan ci musu?” Ubangiji ya ce, “Bi su, gama za ka ci musu, ka ƙwato abin da suka kwashe.”
And David asked counsel of the Lord, saying, Shall I pursue after this troop! shall I overtake them? And he said to him, Pursue; for thou wilt surely overtake them, and certainly recover [all].
9 Dawuda da mutanensa ɗari shida suka kama hanya, da suka kai Kwarin Besor, waɗansunsu suka tsaya a can.
So David went, he and the six hundred men that were with him, and came up to the brook Bessor, where those that were left behind stayed.
10 Dawuda ya ci gaba da mutane ɗari huɗu, don mutane ɗari biyu sun gaji sosai har sun kāsa ƙetare rafin Besor.
But David pursued on, he and four hundred men; and there stayed behind two hundred men, who were too fatigued to go over the brook Bessor.
11 Suka sami wani mutumin Masar a fili suka kawo shi wurin Dawuda. Suka ba shi abinci ya ci, suka kuma ba shi ruwa ya sha.
And they found an Egyptian man in the field, and took him to David, and gave him bread, and he did eat; and they made him drink water;
12 Suka ba shi saura wainan’ya’yan ɓaure da kuma wainan’ya’yan inabi, ya ci ya sami ƙarfi. Gama bai ci ba, bai sha ba, har yini uku da dare uku.
And they gave him a piece of a cake of figs, and two clusters of raisins, and he ate, and then his spirit returned to him; for he had not eaten any bread, nor drunk any water, three days and three nights.
13 Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Wane ne ubangidanka, kuma daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni mutumin Masar ne, bawan wani mutumin Amalek. Maigidana ya ƙyale ni sa’ad da na yi rashin lafiya kwanaki ukun da suka wuce.
And David said unto him, To whom belongest thou? and whence art thou? And he said, I am a young Egyptian man, the servant to an 'Amalekite; and my master left me behind, because I fell sick, today three days ago.
14 Mun kai hari a Negeb ta Keretawa ta Yahuda, da Negeb ta Kaleb, muka kuma ƙone Ziklag.”
We made an invasion upon the south of the Kerethites, and upon that which belongeth to Judah, and upon the south of Caleb; and Ziklag did we burn with fire.
15 Dawuda ya ce masa, “Za ka iya kai ni wurin maharan nan?” Ya ce, “Idan ka rantse mini da Allah, ba za ka kashe ni ba, ba kuwa za ka mai da ni wurin ubangidana ba, sai in kai ka inda maharan suke.”
And David said to him, Wilt thou bring me down to this troop? And he said, Swear unto me by God, that thou wilt not kill me, and that thou wilt not surrender me into the hand of my master, and then will I bring thee down to this troop.
16 Ya bi da Dawuda har zuwa can, sai ga su a baje ko’ina a ƙasa, suna ci, suna sha, suna annashuwa saboda yawan ganimar da suka kwashe daga ƙasar Filistiyawa da ƙasar Yahuda.
And he brought him down; and behold, they were scattered over the face of all the country, eating and drinking, and dancing for joy, because of all the great spoil which they had taken out of the land of the Philistines, and out of the land of Judah.
17 Dawuda ya yaƙe su tun daga fāɗuwar rana har yammar kashegari. Ba ko ɗaya da ya tsira sai samari ɗari huɗu waɗanda suka tsere a kan raƙuma.
And David smote them from the twilight even unto the evening of the next day; and there escaped not a man of them, save four hundred young men, who rode upon camels, and fled.
18 Dawuda ya ƙwato kome da Amalekawa suka kwashe tare da matarsa biyu.
And David recovered all that the 'Amalekites had taken away; and his two wives also did David rescue.
19 Babu abin da ya ɓace, Dawuda ya dawo da kowa, manya da ƙanana,’yan maza da’yan mata duka, da dukan abubuwan da Amalekawa suka kwashe.
And there was nothing missing to them, from small to great, as also sons and daughters, and spoil, down to every thing that they had taken from them: the whole did David bring back.
20 Ya kuma ƙwato garkunan tumaki, da na awaki, da na shanu. Mutanensa suka koro shanun, suka yi gaba, suka ce, “Wannan shi ne ganimar Dawuda.”
And David took all the flocks and the herds: these they drove before those other cattle, and said, This is David's spoil.
21 Da Dawuda ya zo wurin mutum ɗari biyu ɗin nan waɗanda suka tafke, suka kāsa binsa, waɗanda aka bari a bakin Kwarin Besor, sai suka taryi Dawuda da mutanensa da suka tafi tare da shi. Sa’ad da Dawuda ya zo kusa da su, sai ya gaishe su.
And David came to the two hundred men, who had been too fatigued to follow after David, and whom they had left to remain at the brook Bessor: and they went forth to meet David, and to meet the people that were with him; and David came near to the people, and asked them after their well-being.
22 Sai dukan mugaye da marasa kirki daga cikin mutanen da suka tafi tare da Dawuda suka ce, “Tun da yake ba su tafi tare da mu ba, ba za mu ba su kome daga cikin ganimar da muka ƙwato ba, sai dai kowane mutum yă ɗauki matarsa da’ya’yansa yă tafi.”
Then exclaimed every wicked and worthless man, of those that had gone with David, and said, Because they went not with us, we will not give them aught of the spoil that we have recovered, save to every man his wife and his children, and these they may lead away, and go.
23 Dawuda ya ce, “A’a,’yan’uwana ba za ku yi haka da abin da Ubangiji ya ba mu ba. Ya tsare mu, ya kuma bashe sojojin da suka yi gāba da mu a hannuwanmu.
Then said David, Ye must not do so, my brethren; since the Lord hath given us this, and guarded us, and delivered the troop that came against us into our hand.
24 Wa zai goyi bayanku a kan wannan al’amari? Wanda ya tafi wurin yaƙi da wanda ya zauna wurin kaya, rabonsu zai zama daidai.”
And who will hearken unto you in this matter? but as is the part of him that went down to the battle, so shall be the part of him that remained with the baggage: together must they share.
25 Dawuda ya sa wannan tă zama dawwammamiyar farilla ga Isra’ila tun daga wannan rana har yă zuwa yau.
And it happened from that day and forward, that he made it a statute and an ordinance for Israel until this day.
26 Da Dawuda ya iso Ziklag, sai ya aika wa abokansa, dattawan Yahuda da rabo daga cikin ganimar ya ce, “Ga kyauta dominku, daga cikin ganimar maƙiyan Ubangiji.”
And when David came to Ziklag, he sent of the spoil unto the elders of Judah, to his friends, saying, Behold, here is a present for you from the spoil of the enemies of the Lord:
27 Kyautar domin waɗanda suke a Betel, da Ramot ta Negeb, da Yattir,
To those who were in Beth-el, and to those who were in south Ramoth, and to those who were in Yattir,
28 da Arower, da Sifmot, da Eshtemowa,
And to those who were in 'Aro'er, and to those who were in Siphmoth, and to those who were in Eshtemoa',
29 da Rakal, da garuruwan Yerameyelawa, da garuruwan Keniyawa,
And to those who were in Rachal, and to those who were in the cities of Yerach-meelites, and to those who were in the cities of the Kenites,
30 da Horma, da Bor-Ashan, da Atak,
And to those who were in Chormah, and to those who were in Kor-'ashan, and to those who were in 'Athach,
31 da Hebron, da dukan wuraren da Dawuda da mutanensa suka taɓa zagawa.
And to those who were in Hebron, and to all the places where David himself and his men had wandered about.

< 1 Sama’ila 30 >