< 1 Sama’ila 3 >
1 Yaron nan Sama’ila ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli. A waɗannan kwanaki kuwa jin magana daga wurin Ubangiji ba safai ba, babu kuma wahayi da yawa.
And the lad Samuel [was] serving Yahweh before Eli and [the] word of Yahweh it was rare in the days those not vision [was] spread out.
2 Wata rana da dare Eli da idanunsa sun kusa makancewa har ba ya iya gani sosai yana kwance a inda ya saba.
And it was on the day that and Eli [was] lying in place his (and eyes his *Q(K)*) they began dim not he was able to see.
3 Fitilar Allah kuwa tana ci, ba tă mutu ba tukuna, Sama’ila kuma na kwance a haikali na Ubangiji inda akwai akwatin Allah.
And [the] lamp of God not yet it was extinguished and Samuel [was] lying in [the] temple of Yahweh where [was] there [the] ark of God.
4 Sai Ubangiji ya kira Sama’ila. Sama’ila ya amsa ya ce, “Ga ni.”
And he called Yahweh to Samuel and he said here [am] I.
5 Sai ya ruga wajen Eli ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Eli ya ce, “Ɗana ban kira ba, je ka kwanta”. Saboda haka ya tafi ya kwanta.
And he ran to Eli and he said here [am] I for you summoned me and he said not I summoned return lie down and he went and he lay down.
6 Ubangiji ya sāke kiransa ya ce, “Sama’ila!” Sama’ila ya tashi kuma ya je wurin Eli ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Amma Eli ya ce, “Ban kira ka ba, ɗana koma ka kwanta.”
And he repeated Yahweh to call again Samuel and he rose Samuel and he went to Eli and he said here [am] I for you summoned me and he said not I summoned O son my return lie down.
7 Sama’ila dai bai riga ya san Ubangiji ba tukuna. Ba a kuma taɓa bayyana maganar Ubangiji a gare shi ba tukuna ba.
And Samuel not yet he knew Yahweh and not yet it was revealed to him [the] word of Yahweh.
8 Ubangiji ya kira Sama’ila sau na uku, Sama’ila kuma ya tashi ya tafi wurin Eli, “Ga ni, gama ka kira ni.” Sai Eli ya gane cewa Ubangiji ne ke kira yaron.
And he repeated Yahweh to call Samuel at the third [time] and he rose and he went to Eli and he said here [am] I for you summoned me and he understood Eli that Yahweh [was] summoning the lad.
9 Saboda haka, Eli ya gaya wa Sama’ila cewa, “Je ka kwanta, in kuma ya kira ka, ka ce masa, ‘Ya Ubangiji ka yi magana gama bawanka yana saurara.’” Sama’ila ya koma ya kwanta a wurin kwanciyarsa.
And he said Eli to Samuel go lie down and it will be that [if] he will call to you and you will say speak O Yahweh for [is] listening servant your and he went Samuel and he lay down in place his.
10 Ubangiji kuma ya zo ya tsaya a wurin, yana kira ya ce, “Sama’ila, Sama’ila!” Kamar yadda ya kira a lokutan baya. Sai Sama’ila ya ce, “Yi magana gama bawanka yana saurara.”
And he came Yahweh and he stood and he called as time on time O Samuel - O Samuel and he said Samuel speak for [is] listening servant your.
11 Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Duba ina dab da yin wani abu a Isra’ila da zai sa kunne kowa da yake ji, yă ji tsoro.
And he said Yahweh to Samuel here! I [am] about to do a thing in Israel which every [one who] hears it they will tingle [the] two ears his.
12 A ranar zan cika dukan maganar da na yi game da Eli da iyalinsa, daga farko har ƙarshe.
On the day that I will carry out against Eli all that I have spoken against house his beginning and ending.
13 Gama na gaya masa zan hukunta gidansa har abada saboda zunubin da yake sane da shi;’ya’yansa sun wulaƙantar da kansu, shi kuma bai tsawata musu ba.
And I tell to him that [am] about to judge I house his until perpetuity for [the] iniquity which he knew that [were] bringing a curse to themselves sons his and not he rebuked them.
14 Saboda haka na rantse a kan gidan Eli, ‘Ba za a taɓa shafe laifin gidan Eli da hadaya ko baiko ba.’”
And therefore I swear to [the] house of Eli if it will be atoned for [the] iniquity of [the] house of Eli by sacrifice and by an offering until perpetuity.
15 Sama’ila kuwa ya kwanta har safe, sa’an nan ya buɗe ƙofofin gidan Ubangiji. Ya ji tsoro yă gaya wa Eli wahayin,
And he lay Samuel until the morning and he opened [the] doors of [the] house of Yahweh and Samuel he was afraid from telling the vision to Eli.
16 amma Eli ya kira shi ya ce, “Sama’ila, ɗana.” Sama’ila ya ce, “Ga ni.”
And he called Eli Samuel and he said O Samuel son my and he said here [am] I.
17 Eli ya ce, mene ne ya ce maka? Kada ka ɓoye mini. Allah ya yi da kai har ma fiye in ka ɓoye mini kome da ya ce maka.
And he said what? [was] the word which he spoke to you may not please you hide [it] from me thus may he do to you God and thus may he add if you will hide from me a word from all the word which he spoke to you.
18 Don haka sai Sama’ila ya gaya masa kome bai ɓoye masa kome ba. Sa’an nan Eli ya ce, “Shi ne Ubangiji bari yă yi abin da ya yi kyau a gare shi.”
And he told to him Samuel all the words and not he hid [them] from him and he said [is] Yahweh he the good (in eyes his *Q(K)*) let him do.
19 Ubangiji kuwa yana tare da Sama’ila har girmansa bai kuma bar ko ɗaya daga maganarsa ta kāsa cika ba.
And he grew up Samuel and Yahweh he was with him and not he made fall any of all words his [the] ground towards.
20 Dukan Isra’ila daga Dan har Beyersheba suka shaida amincin Sama’ila annabi ne na Ubangiji.
And it knew all Israel from Dan and to Beer Sheba that [was being] established Samuel to a prophet of Yahweh.
21 Ubangiji kuwa ya dinga bayyana a Shilo, a nan ya bayyana kansa ga Sama’ila ta wurin maganarsa.
And he repeated Yahweh to appear at Shiloh for he revealed himself Yahweh to Samuel at Shiloh by [the] word of Yahweh.