< 1 Sama’ila 3 >

1 Yaron nan Sama’ila ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli. A waɗannan kwanaki kuwa jin magana daga wurin Ubangiji ba safai ba, babu kuma wahayi da yawa.
And the lad Samuel was ministering unto the Lord before 'Eli. And the word of the Lord was scarce in those days: prophecy was not extended.
2 Wata rana da dare Eli da idanunsa sun kusa makancewa har ba ya iya gani sosai yana kwance a inda ya saba.
And it came to pass one day, when 'Eli was lying down in his place, and his eyes had begun to grow dim, he could not see;
3 Fitilar Allah kuwa tana ci, ba tă mutu ba tukuna, Sama’ila kuma na kwance a haikali na Ubangiji inda akwai akwatin Allah.
And the lamp of God had not yet gone out, while Samuel was lying down in [the hall of] the temple of the Lord, where the ark of God was;
4 Sai Ubangiji ya kira Sama’ila. Sama’ila ya amsa ya ce, “Ga ni.”
That the Lord called Samuel: and he said, Here am I.
5 Sai ya ruga wajen Eli ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Eli ya ce, “Ɗana ban kira ba, je ka kwanta”. Saboda haka ya tafi ya kwanta.
And he ran unto 'Eli, and said, Here am I; for thou didst call me. And he said, I did not call: lie down again. And he went and lay down.
6 Ubangiji ya sāke kiransa ya ce, “Sama’ila!” Sama’ila ya tashi kuma ya je wurin Eli ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Amma Eli ya ce, “Ban kira ka ba, ɗana koma ka kwanta.”
And the Lord continued to call again, Samuel. And Samuel arose and went to 'Eli, and said, Here am I; for thou didst call me. And he answered, I did not call, my son: lie down again.
7 Sama’ila dai bai riga ya san Ubangiji ba tukuna. Ba a kuma taɓa bayyana maganar Ubangiji a gare shi ba tukuna ba.
And Samuel knew not yet the Lord, nor had the word of the Lord been as yet revealed unto him.
8 Ubangiji ya kira Sama’ila sau na uku, Sama’ila kuma ya tashi ya tafi wurin Eli, “Ga ni, gama ka kira ni.” Sai Eli ya gane cewa Ubangiji ne ke kira yaron.
And the Lord continued to call, Samuel, the third time; and he arose and went to 'Eli, and said, Here am I; for thou didst call me. And 'Eli then perceived that the Lord was calling the lad.
9 Saboda haka, Eli ya gaya wa Sama’ila cewa, “Je ka kwanta, in kuma ya kira ka, ka ce masa, ‘Ya Ubangiji ka yi magana gama bawanka yana saurara.’” Sama’ila ya koma ya kwanta a wurin kwanciyarsa.
And 'Eli said unto Samuel, Go, lie down; and it shall be, if he call thee, that thou shalt say, Speak, Lord; for thy servant heareth. And Samuel went and lay down in his place.
10 Ubangiji kuma ya zo ya tsaya a wurin, yana kira ya ce, “Sama’ila, Sama’ila!” Kamar yadda ya kira a lokutan baya. Sai Sama’ila ya ce, “Yi magana gama bawanka yana saurara.”
And the Lord came, and placed himself, and called as at previous times, Samuel, Samuel. And Samuel said, Speak; for thy servant heareth.
11 Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Duba ina dab da yin wani abu a Isra’ila da zai sa kunne kowa da yake ji, yă ji tsoro.
And the Lord said to Samuel, Behold, I will do a thing in Israel, at which both the ears of every one that heareth it shall tingle.
12 A ranar zan cika dukan maganar da na yi game da Eli da iyalinsa, daga farko har ƙarshe.
On that day will I fulfill on 'Eli all that I have spoken concerning his house: I will begin and finish.
13 Gama na gaya masa zan hukunta gidansa har abada saboda zunubin da yake sane da shi;’ya’yansa sun wulaƙantar da kansu, shi kuma bai tsawata musu ba.
And I tell him that I will judge his house for ever; for the iniquity that he knew that his sons were drawing a curse on themselves, and he restrained them not.
14 Saboda haka na rantse a kan gidan Eli, ‘Ba za a taɓa shafe laifin gidan Eli da hadaya ko baiko ba.’”
And therefore have I sworn unto the house of 'Eli, that the iniquity of 'Eli's house shall not be atoned for with sacrifice or meat-offering for ever.
15 Sama’ila kuwa ya kwanta har safe, sa’an nan ya buɗe ƙofofin gidan Ubangiji. Ya ji tsoro yă gaya wa Eli wahayin,
And Samuel lay until the morning, when he opened the doors of the house of the Lord; and Samuel feared to tell the vision unto 'Eli.
16 amma Eli ya kira shi ya ce, “Sama’ila, ɗana.” Sama’ila ya ce, “Ga ni.”
But 'Eli called Samuel, and said, Samuel, my son. And he said, Here am I.
17 Eli ya ce, mene ne ya ce maka? Kada ka ɓoye mini. Allah ya yi da kai har ma fiye in ka ɓoye mini kome da ya ce maka.
And he said, What is the word which he hath spoken unto thee? do not, I pray thee, conceal it from me: may God do to thee thus, and continue to do so, if thou conceal any thing from me of all the word that he hath spoken unto thee.
18 Don haka sai Sama’ila ya gaya masa kome bai ɓoye masa kome ba. Sa’an nan Eli ya ce, “Shi ne Ubangiji bari yă yi abin da ya yi kyau a gare shi.”
And Samuel told him all the words, and concealed nothing from him. And he said, He is the Lord: let him do what seemeth good in his eyes.
19 Ubangiji kuwa yana tare da Sama’ila har girmansa bai kuma bar ko ɗaya daga maganarsa ta kāsa cika ba.
And Samuel grew up, and the Lord was with him, and he did not let fall any one of all his words to the ground.
20 Dukan Isra’ila daga Dan har Beyersheba suka shaida amincin Sama’ila annabi ne na Ubangiji.
And thus knew all Israel from Dan even to Beer-sheba' that Samuel was accredited as a prophet of the Lord.
21 Ubangiji kuwa ya dinga bayyana a Shilo, a nan ya bayyana kansa ga Sama’ila ta wurin maganarsa.
And the Lord continued to appear in Shiloh; for the Lord revealed himself to Samuel in Shiloh by the word of the Lord.

< 1 Sama’ila 3 >