< 1 Sama’ila 3 >

1 Yaron nan Sama’ila ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli. A waɗannan kwanaki kuwa jin magana daga wurin Ubangiji ba safai ba, babu kuma wahayi da yawa.
Now the child Samuel ministered to the Lord before Heli, and the word of the Lord was precious in those days, there was no manifest vision.
2 Wata rana da dare Eli da idanunsa sun kusa makancewa har ba ya iya gani sosai yana kwance a inda ya saba.
And it came to pass one day when Heli lay in his place, and his eyes were grown dim, that he could not see:
3 Fitilar Allah kuwa tana ci, ba tă mutu ba tukuna, Sama’ila kuma na kwance a haikali na Ubangiji inda akwai akwatin Allah.
Before the lamp of God went out, Samuel slept in the temple of the Lord, where the ark of God was.
4 Sai Ubangiji ya kira Sama’ila. Sama’ila ya amsa ya ce, “Ga ni.”
And the Lord called Samuel. And he answered: Here am I.
5 Sai ya ruga wajen Eli ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Eli ya ce, “Ɗana ban kira ba, je ka kwanta”. Saboda haka ya tafi ya kwanta.
And he ran to Heli and said: Here am I: for thou didst call me. He said: I did not call: go back and sleep. And he went and slept.
6 Ubangiji ya sāke kiransa ya ce, “Sama’ila!” Sama’ila ya tashi kuma ya je wurin Eli ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Amma Eli ya ce, “Ban kira ka ba, ɗana koma ka kwanta.”
And the Lord called Samuel again. And Samuel arose and went to Heli, and said: Here am I: for thou calledst me. He answered: I did not call thee, my son: return and sleep.
7 Sama’ila dai bai riga ya san Ubangiji ba tukuna. Ba a kuma taɓa bayyana maganar Ubangiji a gare shi ba tukuna ba.
Now Samuel did not yet know the Lord, neither had the word of the Lord been revealed to him.
8 Ubangiji ya kira Sama’ila sau na uku, Sama’ila kuma ya tashi ya tafi wurin Eli, “Ga ni, gama ka kira ni.” Sai Eli ya gane cewa Ubangiji ne ke kira yaron.
And the Lord called Samuel again the third time. And he arose up and went to Heli.
9 Saboda haka, Eli ya gaya wa Sama’ila cewa, “Je ka kwanta, in kuma ya kira ka, ka ce masa, ‘Ya Ubangiji ka yi magana gama bawanka yana saurara.’” Sama’ila ya koma ya kwanta a wurin kwanciyarsa.
And said: Here am I: for thou didst call me. Then Heli understood that the Lord called the child, and he said to Samuel: Go, and sleep: and if he shall call thee any more, thou shalt say: Speak, Lord, for thy servant heareth. So Samuel went and slept in his place.
10 Ubangiji kuma ya zo ya tsaya a wurin, yana kira ya ce, “Sama’ila, Sama’ila!” Kamar yadda ya kira a lokutan baya. Sai Sama’ila ya ce, “Yi magana gama bawanka yana saurara.”
And the Lord came and stood: and he called, as he had called the other times: Samuel, Samuel. And Samuel said: Speak, Lord, for thy servant heareth.
11 Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Duba ina dab da yin wani abu a Isra’ila da zai sa kunne kowa da yake ji, yă ji tsoro.
And the Lord said to Samuel: Behold I do a thing in Israel: and whosoever shall hear it, both his ears shall tingle.
12 A ranar zan cika dukan maganar da na yi game da Eli da iyalinsa, daga farko har ƙarshe.
In that day I will raise up against Heli all the things I have spoken concerning his house: I will begin, and I will make an end.
13 Gama na gaya masa zan hukunta gidansa har abada saboda zunubin da yake sane da shi;’ya’yansa sun wulaƙantar da kansu, shi kuma bai tsawata musu ba.
For I have foretold unto him, that I will judge his house for ever, for iniquity, because he knew that his sons did wickedly, and did not chastise them.
14 Saboda haka na rantse a kan gidan Eli, ‘Ba za a taɓa shafe laifin gidan Eli da hadaya ko baiko ba.’”
Therefore have I sworn to the house of Heli, that the iniquity of his house shall not be expiated with victims nor offerings for ever.
15 Sama’ila kuwa ya kwanta har safe, sa’an nan ya buɗe ƙofofin gidan Ubangiji. Ya ji tsoro yă gaya wa Eli wahayin,
And Samuel slept till morning, and opened the doors of the house of the Lord. And Samuel feared to tell the vision to Heli.
16 amma Eli ya kira shi ya ce, “Sama’ila, ɗana.” Sama’ila ya ce, “Ga ni.”
Then Heli called Samuel, and said: Samuel, my son. And he answered: Here am I.
17 Eli ya ce, mene ne ya ce maka? Kada ka ɓoye mini. Allah ya yi da kai har ma fiye in ka ɓoye mini kome da ya ce maka.
And he asked him: What is the word that the Lord hath spoken to thee? I beseech thee hide it not from me. May God do so and so to thee, and add so and so, if thou hide from me one word of all that were said to thee.
18 Don haka sai Sama’ila ya gaya masa kome bai ɓoye masa kome ba. Sa’an nan Eli ya ce, “Shi ne Ubangiji bari yă yi abin da ya yi kyau a gare shi.”
So Samuel told him all the words, and did not hide them from him. And he answered: It is the Lord: let him do what is good in his sight.
19 Ubangiji kuwa yana tare da Sama’ila har girmansa bai kuma bar ko ɗaya daga maganarsa ta kāsa cika ba.
And Samuel grew, and the Lord was with him, and not one of his words fell to the ground.
20 Dukan Isra’ila daga Dan har Beyersheba suka shaida amincin Sama’ila annabi ne na Ubangiji.
And all Israel from Dan to Bersabee, knew that Samuel was a faithful prophet of the Lord.
21 Ubangiji kuwa ya dinga bayyana a Shilo, a nan ya bayyana kansa ga Sama’ila ta wurin maganarsa.
And the Lord again appeared in Silo, for the Lord revealed himself to Samuel in Silo, according to the word of the Lord. And the word of Samuel came to pass to all Israel.

< 1 Sama’ila 3 >