< 1 Sama’ila 3 >

1 Yaron nan Sama’ila ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli. A waɗannan kwanaki kuwa jin magana daga wurin Ubangiji ba safai ba, babu kuma wahayi da yawa.
Den unge Samuel gjorde saa Tjeneste for HERREN under Elis Tilsyn. HERRENS Ord var sparsomt i de Dage, et Syn var sjældent.
2 Wata rana da dare Eli da idanunsa sun kusa makancewa har ba ya iya gani sosai yana kwance a inda ya saba.
Ved den Tid — engang da Eli, hvis Øjne var begyndt at blive svage, saa han ikke kunde se, laa paa sin vante Plads,
3 Fitilar Allah kuwa tana ci, ba tă mutu ba tukuna, Sama’ila kuma na kwance a haikali na Ubangiji inda akwai akwatin Allah.
og Guds Lampe endnu ikke var gaaet ud, og Samuel laa og sov i HERRENS Helligdom, hvor Guds Ark stod —
4 Sai Ubangiji ya kira Sama’ila. Sama’ila ya amsa ya ce, “Ga ni.”
kaldte HERREN: »Samuel, Samuel!« Han svarede: »Her er jeg!«
5 Sai ya ruga wajen Eli ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Eli ya ce, “Ɗana ban kira ba, je ka kwanta”. Saboda haka ya tafi ya kwanta.
Og han løb hen til Eli og sagde: »Her er jeg, du kaldte paa mig!« Men han sagde: »Jeg kaldte ikke; læg dig kun hen igen!« Og han gik hen og lagde sig.
6 Ubangiji ya sāke kiransa ya ce, “Sama’ila!” Sama’ila ya tashi kuma ya je wurin Eli ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Amma Eli ya ce, “Ban kira ka ba, ɗana koma ka kwanta.”
Da kaldte HERREN atter: »Samuel, Samuel!« Og han gik hen til Eli og sagde: »Her er jeg, du kaldte paa mig!« Men han sagde: »Jeg kaldte ikke, min Søn; læg dig kun hen igen!«
7 Sama’ila dai bai riga ya san Ubangiji ba tukuna. Ba a kuma taɓa bayyana maganar Ubangiji a gare shi ba tukuna ba.
Samuel havde nemlig endnu ikke lært HERREN at kende, og HERRENS Ord var endnu ikke aabenbaret ham.
8 Ubangiji ya kira Sama’ila sau na uku, Sama’ila kuma ya tashi ya tafi wurin Eli, “Ga ni, gama ka kira ni.” Sai Eli ya gane cewa Ubangiji ne ke kira yaron.
Da kaldte HERREN atter for tredje Gang paa Samuel, og han stod op, gik hen til Eli og sagde: »Her er jeg, du kaldte paa mig!« Saa skønnede Eli, at det var HERREN, der kaldte paa Drengen.
9 Saboda haka, Eli ya gaya wa Sama’ila cewa, “Je ka kwanta, in kuma ya kira ka, ka ce masa, ‘Ya Ubangiji ka yi magana gama bawanka yana saurara.’” Sama’ila ya koma ya kwanta a wurin kwanciyarsa.
Og Eli sagde til Samuel: »Læg dig hen igen, og hvis han kalder paa dig, saa sig: Tal, HERRE, din Tjener hører!« Saa gik Samuel hen og lagde sig paa sin Plads.
10 Ubangiji kuma ya zo ya tsaya a wurin, yana kira ya ce, “Sama’ila, Sama’ila!” Kamar yadda ya kira a lokutan baya. Sai Sama’ila ya ce, “Yi magana gama bawanka yana saurara.”
Da kom HERREN og traadte hen til ham og kaldte ligesom de forrige Gange: »Samuel, Samuel!« Og Samuel svarede: »Tal, din Tjener hører!«
11 Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Duba ina dab da yin wani abu a Isra’ila da zai sa kunne kowa da yake ji, yă ji tsoro.
Saa sagde HERREN til Samuel: »Se, jeg vil lade noget ske i Israel, som skal faa det til at ringe for begge Ører paa enhver, som hører derom.
12 A ranar zan cika dukan maganar da na yi game da Eli da iyalinsa, daga farko har ƙarshe.
Paa den Dag vil jeg lade alt, hvad jeg har talt om Elis Slægt, opfyldes paa ham, alt fra først til sidst.
13 Gama na gaya masa zan hukunta gidansa har abada saboda zunubin da yake sane da shi;’ya’yansa sun wulaƙantar da kansu, shi kuma bai tsawata musu ba.
Du skal kundgøre ham, at jeg har dømt hans Slægt for evigt, fordi han vidste, at hans Sønner ringeagtede Gud, og dog ikke talte dem alvorligt til.
14 Saboda haka na rantse a kan gidan Eli, ‘Ba za a taɓa shafe laifin gidan Eli da hadaya ko baiko ba.’”
Derfor har jeg svoret over Elis Hus: Visselig, Elis Hus's Brøde skal aldrig i Evighed sones ved Slagtofre eller Afgrødeofre!«
15 Sama’ila kuwa ya kwanta har safe, sa’an nan ya buɗe ƙofofin gidan Ubangiji. Ya ji tsoro yă gaya wa Eli wahayin,
Samuel blev nu liggende til Morgen, og tidligt næste Morgen aabnede han Døren til HERRENS Hus; men Samuel turde ikke omtale Synet for Eli.
16 amma Eli ya kira shi ya ce, “Sama’ila, ɗana.” Sama’ila ya ce, “Ga ni.”
Da kaldte Eli paa Samuel og sagde: »Min Søn Samuel!« Han svarede: »Her er jeg!«
17 Eli ya ce, mene ne ya ce maka? Kada ka ɓoye mini. Allah ya yi da kai har ma fiye in ka ɓoye mini kome da ya ce maka.
Da sagde han: »Hvad var det, han sagde til dig? Dølg det ikke for mig! Gud ramme dig baade med det ene og det andet, hvis du dølger noget af, hvad han sagde!«
18 Don haka sai Sama’ila ya gaya masa kome bai ɓoye masa kome ba. Sa’an nan Eli ya ce, “Shi ne Ubangiji bari yă yi abin da ya yi kyau a gare shi.”
Saa fortalte Samuel ham det hele uden at dølge noget. Da sagde han: »Han er HERREN; han gøre, hvad ham tykkes bedst!«
19 Ubangiji kuwa yana tare da Sama’ila har girmansa bai kuma bar ko ɗaya daga maganarsa ta kāsa cika ba.
Samuel voksede nu til og HERREN var med ham og lod ikke et eneste af sine Ord falde til Jorden.
20 Dukan Isra’ila daga Dan har Beyersheba suka shaida amincin Sama’ila annabi ne na Ubangiji.
Og hele Israel fra Dan til Be'ersjeba forstod, at Samuel virkelig var kaldet til HERRENS Profet.
21 Ubangiji kuwa ya dinga bayyana a Shilo, a nan ya bayyana kansa ga Sama’ila ta wurin maganarsa.
Og HERREN vedblev at lade sig til Syne i Silo; thi HERREN aabenbarede sig for Samuel.

< 1 Sama’ila 3 >