< 1 Sama’ila 29 >

1 Filistiyawa suka tattara dukan rundunoninsu a Afek. Isra’ila kuwa suka yi sansani kusa da maɓulɓular da take Yezireyel.
و فلسطینیان همه لشکرهای خود را درافیق جمع کردند، و اسرائیلیان نزدچشمه‌ای که در یزرعیل است، فرود آمدند.۱
2 Sa’ad da sarakuna Filistiyawa suke wucewa da rundunarsu na mutum ɗari-ɗari da na dubu-dubu. Dawuda da mutanensa suna biye a baya tare da Akish.
وسرداران فلسطینیان صدها و هزارها می‌گذشتند، و داود و مردانش با اخیش در دنباله ایشان می‌گذشتند.۲
3 Komandodin Filistiyawa suka ce, “Waɗannan Ibraniyawa kuma fa?” Akish ya ce, “Wannan shi ne Dawuda hafsan Shawulu, sarkin Isra’ila. Yana nan tare da ni shekara guda ke nan. Ban kuwa taɓa samunsa da wani lahani ba tun daga ranar da ya bar Shawulu.”
و سرداران فلسطینیان گفتند که «این عبرانیان کیستند؟» و اخیش به جواب سرداران فلسطینیان گفت: «مگر این داود، بنده شاول، پادشاه اسرائیل نیست که نزد من این‌روزهایا این سالها بوده است و از روزی که نزد من آمد تاامروز در او عیبی نیافتم.»۳
4 Amma komandodin Filistiyawa suka yi fushi, suka ce, “Ka sa mutumin nan yă koma zuwa wurin da ka ba shi yă zauna. Ba zai bi mu zuwa wurin yaƙi ba. Yana iya juya a kanmu lokacin yaƙin. Zai iya yin amfani da wannan zarafi yă ciccire kawunanmu don yă faranta wa maigidansa rai?
اما سرداران فلسطینیان بر وی غضبناک شدند، و سرداران فلسطینیان او را گفتند: «این مردرا باز گردان تا به‌جایی که برایش تعیین کرده‌ای برگردد، و با ما به جنگ نیاید، مبادا در جنگ دشمن ما بشود، زیرا این کس با چه چیز با آقای خود صلح کند آیا نه با سرهای این مردمان؟۴
5 Tuna fa, ba shi ne Dawuda ɗin da ake girmama da rawa da waƙoƙi ana cewa, “‘Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa dubbun dubbai ba’?”
آیااین داود نیست که درباره او با یکدیگر رقص کرده، می‌سراییدند و می‌گفتند: «شاول هزارهای خود و داود ده هزارهای خویش را کشته است.»۵
6 Saboda haka Akish ya kira Dawuda ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, na amince da kai tun daga ranar da ka zo wurina har yă zuwa yau, ban same ka da wani laifi ba, na kuma yi farin ciki in sa ka a cikin sojojina don ka yi mini aiki. Amma masu mulki nawa ba su yarda da kai ba.
آنگاه اخیش داود را خوانده، او را گفت: «به حیات یهوه قسم که تو مرد راست هستی و خروج و دخول تو با من در اردو به نظر من پسند آمد، زیرا از روز آمدنت نزد من تا امروز از تو بدی ندیده‌ام لیکن در نظر سرداران پسند نیستی.۶
7 Sai ka juya ka koma ka isa lafiya ba tare da ɓata wa masu mulkin Filistiyawa rai ba.”
پس الان برگشته، به سلامتی برو مبادا مرتکب عملی شوی که در نظر سرداران فلسطینیان ناپسند آید.»۷
8 Dawuda ya ce wa Akish, “Me na yi? Ka taɓa samun bawanka da laifi tun daga ranar da na zo har zuwa yanzu? Ina dalilin da ba zan tafi tare da kai in yaƙi maƙiyin ranka yă daɗe, sarki ba?”
و داود به اخیش گفت: «چه کرده‌ام و از روزی که به حضور تو بوده‌ام تا امروز در بنده ات چه یافته‌ای تا آنکه به جنگ نیایم و با دشمنان آقایم پادشاه جنگ ننمایم؟»۸
9 Akish ya ce, “A ganina kai marar laifi ne kamar mala’ikan Allah, duk da haka shugabannin sojojin Filistiyawa sun ce, ‘Ba zai tafi yaƙi tare da mu ba.’
اخیش در جواب داود گفت: «می‌دانم که تودر نظر من مثل فرشته خدا نیکو هستی لیکن سرداران فلسطینیان گفتند که با ما به جنگ نیاید.۹
10 Ka tashi da sassafe, kai da bayin shugabanka da suka zo tare da kai. Da gari ya waye sai ku kama hanya.”
پس الحال بامدادان با بندگان آقایت که همراه تو آمده‌اند، برخیز و چون بامدادان برخاسته باشید و روشنایی برای شما بشود، روانه شوید.»۱۰
11 Gari na wayewa tun da sassafe Dawuda da mutanensa suka tashi suka kama hanyar komawa ƙasar Filistiyawa. Filistiyawa kuwa suka haura zuwa Yezireyel.
پس داود با کسان خود صبح زود برخاستند تا روانه شده، به زمین فلسطینیان برگردند وفلسطینیان به یزرعیل برآمدند.۱۱

< 1 Sama’ila 29 >