< 1 Sama’ila 29 >

1 Filistiyawa suka tattara dukan rundunoninsu a Afek. Isra’ila kuwa suka yi sansani kusa da maɓulɓular da take Yezireyel.
Toutes les troupes des Philistins s’assemblèrent donc à Aphec; mais Israël aussi campa près de la fontaine de Jezraël.
2 Sa’ad da sarakuna Filistiyawa suke wucewa da rundunarsu na mutum ɗari-ɗari da na dubu-dubu. Dawuda da mutanensa suna biye a baya tare da Akish.
Or, les satrapes des Philistins marchaient avec des compagnies de cent et de mille hommes; mais David et ses hommes étaient à l’arrière-garde avec Achis.
3 Komandodin Filistiyawa suka ce, “Waɗannan Ibraniyawa kuma fa?” Akish ya ce, “Wannan shi ne Dawuda hafsan Shawulu, sarkin Isra’ila. Yana nan tare da ni shekara guda ke nan. Ban kuwa taɓa samunsa da wani lahani ba tun daga ranar da ya bar Shawulu.”
Les princes des Philistins dirent à Achis: Que veulent dire ces Hébreux? Et Achis répondit aux princes des Philistins: Est-ce que vous ne connaissez pas David, qui a été serviteur de Saül, roi d’Israël, qui est avec moi depuis nombre de jours et même d’années, et dans lequel je n’ai rien trouvé, depuis le jour qu’il s’est réfugié auprès de moi jusqu’à ce jour-ci?
4 Amma komandodin Filistiyawa suka yi fushi, suka ce, “Ka sa mutumin nan yă koma zuwa wurin da ka ba shi yă zauna. Ba zai bi mu zuwa wurin yaƙi ba. Yana iya juya a kanmu lokacin yaƙin. Zai iya yin amfani da wannan zarafi yă ciccire kawunanmu don yă faranta wa maigidansa rai?
Mais les princes des Philistins s’irritèrent contre lui, et lui dirent: Que cet homme s’en retourne; qu’il demeure dans son lieu, dans lequel vous l’avez établi, et qu’il ne descende pas avec nous au combat, afin qu’il ne devienne point notre ennemi, lorsque nous aurons commencé à combattre; car comment pourra-t-il apaiser son seigneur autrement qu’avec nos têtes?
5 Tuna fa, ba shi ne Dawuda ɗin da ake girmama da rawa da waƙoƙi ana cewa, “‘Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa dubbun dubbai ba’?”
N’est-ce pas ce David, en l’honneur duquel on chantait dans les chœurs: Saül a frappé sur ses mille, et David sur ses dix mille?
6 Saboda haka Akish ya kira Dawuda ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, na amince da kai tun daga ranar da ka zo wurina har yă zuwa yau, ban same ka da wani laifi ba, na kuma yi farin ciki in sa ka a cikin sojojina don ka yi mini aiki. Amma masu mulki nawa ba su yarda da kai ba.
Achis donc appela David, et lui dit: Le Seigneur vit! tu es droit et bon en ma présence, et ta sortie et ton entrée est avec moi dans le camp; et je n’ai trouvé en toi rien de mal, depuis le jour que tu es venu vers moi jusqu’à ce jour-ci; mais tu ne plais pas aux satrapes.
7 Sai ka juya ka koma ka isa lafiya ba tare da ɓata wa masu mulkin Filistiyawa rai ba.”
Retourne-t’en donc, et va en paix, et n’offense pas les yeux des satrapes des Philistins.
8 Dawuda ya ce wa Akish, “Me na yi? Ka taɓa samun bawanka da laifi tun daga ranar da na zo har zuwa yanzu? Ina dalilin da ba zan tafi tare da kai in yaƙi maƙiyin ranka yă daɗe, sarki ba?”
Et David demanda à Achis: Qu’ai-je donc fait, et qu’avez-vous trouvé en moi, votre serviteur, depuis le jour que j’ai été en votre présence jusqu’à ce jour-ci, pour que je ne vienne point, et que je ne combatte point contre les ennemis de mon seigneur roi?
9 Akish ya ce, “A ganina kai marar laifi ne kamar mala’ikan Allah, duk da haka shugabannin sojojin Filistiyawa sun ce, ‘Ba zai tafi yaƙi tare da mu ba.’
Mais répondant, Achis dit à David: Je sais que tu es bon à mes yeux comme un ange de Dieu; mais les princes des Philistins ont dit: Il ne montera point avec nous au combat.
10 Ka tashi da sassafe, kai da bayin shugabanka da suka zo tare da kai. Da gari ya waye sai ku kama hanya.”
Ainsi lève-toi, dès le matin, toi et les serviteurs de ton seigneur qui sont venus avec toi; et lorsque vous vous serez levés pendant la nuit, et qu’il aura commencé à faire jour, partez.
11 Gari na wayewa tun da sassafe Dawuda da mutanensa suka tashi suka kama hanyar komawa ƙasar Filistiyawa. Filistiyawa kuwa suka haura zuwa Yezireyel.
C’est pourquoi David se leva pendant la nuit, lui et ses hommes, pour partir dès le matin, et retourner dans la terre des Philistins; mais les Philistins montèrent à Jezraël.

< 1 Sama’ila 29 >