< 1 Sama’ila 29 >

1 Filistiyawa suka tattara dukan rundunoninsu a Afek. Isra’ila kuwa suka yi sansani kusa da maɓulɓular da take Yezireyel.
Or, les Philistins assemblèrent toutes leurs armées à Aphek; et les Israélites étaient campés près de la fontaine qui est à Jizréel.
2 Sa’ad da sarakuna Filistiyawa suke wucewa da rundunarsu na mutum ɗari-ɗari da na dubu-dubu. Dawuda da mutanensa suna biye a baya tare da Akish.
Et les princes des Philistins marchèrent avec leurs centaines et avec leurs milliers; et David et ses gens marchaient à l'arrière-garde avec Akish.
3 Komandodin Filistiyawa suka ce, “Waɗannan Ibraniyawa kuma fa?” Akish ya ce, “Wannan shi ne Dawuda hafsan Shawulu, sarkin Isra’ila. Yana nan tare da ni shekara guda ke nan. Ban kuwa taɓa samunsa da wani lahani ba tun daga ranar da ya bar Shawulu.”
Alors les chefs des Philistins dirent: Que font ici ces Hébreux? Et Akish répondit aux chefs des Philistins: N'est-ce pas David, serviteur de Saül, roi d'Israël, qui a déjà été avec moi quelque temps, ou plutôt quelques années? Or je n'ai rien trouvé à redire en lui, depuis le jour où il est passé à nous jusqu'à ce jour-ci?
4 Amma komandodin Filistiyawa suka yi fushi, suka ce, “Ka sa mutumin nan yă koma zuwa wurin da ka ba shi yă zauna. Ba zai bi mu zuwa wurin yaƙi ba. Yana iya juya a kanmu lokacin yaƙin. Zai iya yin amfani da wannan zarafi yă ciccire kawunanmu don yă faranta wa maigidansa rai?
Mais les chefs des Philistins se mirent en colère contre lui, et lui dirent: Renvoie cet homme, et qu'il s'en retourne au lieu où tu l'as établi, et qu'il ne descende point avec nous au combat, de peur qu'il ne se tourne contre nous dans la bataille. Car comment pourrait-il rentrer en grâce auprès de son seigneur? Ne serait-ce pas au moyen des têtes de nos gens?
5 Tuna fa, ba shi ne Dawuda ɗin da ake girmama da rawa da waƙoƙi ana cewa, “‘Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa dubbun dubbai ba’?”
N'est-ce pas ce David dont on disait, en chantant dans les danses: Saül a frappé ses mille, et David ses dix mille?
6 Saboda haka Akish ya kira Dawuda ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, na amince da kai tun daga ranar da ka zo wurina har yă zuwa yau, ban same ka da wani laifi ba, na kuma yi farin ciki in sa ka a cikin sojojina don ka yi mini aiki. Amma masu mulki nawa ba su yarda da kai ba.
Akish appela donc David, et lui dit: L'Éternel est vivant! tu es un homme droit, et j'aimerais à te voir sortir et entrer au camp avec moi; car je n'ai point trouvé de mal en toi, depuis le jour où tu vins vers moi jusqu'à ce jour-ci; mais tu ne plais point aux princes.
7 Sai ka juya ka koma ka isa lafiya ba tare da ɓata wa masu mulkin Filistiyawa rai ba.”
Maintenant donc retourne et va-t'en en paix, afin que tu ne fasses rien qui déplaise aux princes des Philistins.
8 Dawuda ya ce wa Akish, “Me na yi? Ka taɓa samun bawanka da laifi tun daga ranar da na zo har zuwa yanzu? Ina dalilin da ba zan tafi tare da kai in yaƙi maƙiyin ranka yă daɗe, sarki ba?”
Et David dit à Akish: Mais qu'ai-je fait, et qu'as-tu trouvé en ton serviteur, depuis le jour où j'ai été auprès de toi jusqu'à maintenant, pour que je n'aille point combattre contre les ennemis de mon seigneur le roi?
9 Akish ya ce, “A ganina kai marar laifi ne kamar mala’ikan Allah, duk da haka shugabannin sojojin Filistiyawa sun ce, ‘Ba zai tafi yaƙi tare da mu ba.’
Et Akish répondit et dit à David: Je le sais, car tu m'es agréable comme un ange de Dieu; mais les chefs des Philistins ont dit: Il ne montera point avec nous au combat.
10 Ka tashi da sassafe, kai da bayin shugabanka da suka zo tare da kai. Da gari ya waye sai ku kama hanya.”
C'est pourquoi lève-toi de bon matin, avec les serviteurs de ton seigneur qui sont venus avec toi; et levez-vous de bon matin, et sitôt que vous verrez le jour, allez-vous en.
11 Gari na wayewa tun da sassafe Dawuda da mutanensa suka tashi suka kama hanyar komawa ƙasar Filistiyawa. Filistiyawa kuwa suka haura zuwa Yezireyel.
Ainsi David se leva de bonne heure, lui et ses gens, pour partir dès le matin, pour retourner au pays des Philistins; mais les Philistins montèrent à Jizréel.

< 1 Sama’ila 29 >