< 1 Sama’ila 29 >

1 Filistiyawa suka tattara dukan rundunoninsu a Afek. Isra’ila kuwa suka yi sansani kusa da maɓulɓular da take Yezireyel.
Or les Philistins assemblèrent toutes leurs armées à Aphek; et les Israëlites étaient campés près de la fontaine de Jizréhel.
2 Sa’ad da sarakuna Filistiyawa suke wucewa da rundunarsu na mutum ɗari-ɗari da na dubu-dubu. Dawuda da mutanensa suna biye a baya tare da Akish.
Et les Gouverneurs des Philistins passèrent par [leurs] centaines et par [leurs] milliers; et David et ses gens passèrent sur l'arrière-garde avec Akis.
3 Komandodin Filistiyawa suka ce, “Waɗannan Ibraniyawa kuma fa?” Akish ya ce, “Wannan shi ne Dawuda hafsan Shawulu, sarkin Isra’ila. Yana nan tare da ni shekara guda ke nan. Ban kuwa taɓa samunsa da wani lahani ba tun daga ranar da ya bar Shawulu.”
Et les chefs des Philistins dirent: Qu'est-ce que ces Hébreux-là? Et Akis répondit aux chefs des Philistins: N'est-ce pas ici ce David, serviteur de Saül Roi d'Israël, qui a déjà été avec moi quelque temps, même quelques années? et je n'ai rien trouvé à redire en lui depuis le jour qu'il s'est rendu [à moi], jusqu'à ce jour.
4 Amma komandodin Filistiyawa suka yi fushi, suka ce, “Ka sa mutumin nan yă koma zuwa wurin da ka ba shi yă zauna. Ba zai bi mu zuwa wurin yaƙi ba. Yana iya juya a kanmu lokacin yaƙin. Zai iya yin amfani da wannan zarafi yă ciccire kawunanmu don yă faranta wa maigidansa rai?
Mais les chefs des Philistins se mirent en colère contre lui, et lui dirent: Renvoie cet homme, et qu'il s'en retourne dans le lieu où tu l'as établi, et qu'il ne descende point avec nous dans la bataille, de peur qu'il ne se tourne contre nous dans la bataille; car comment pourrait-il se remettre en grâce avec son Seigneur? ne serait-ce pas par le moyen des têtes de ces hommes-ci?
5 Tuna fa, ba shi ne Dawuda ɗin da ake girmama da rawa da waƙoƙi ana cewa, “‘Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa dubbun dubbai ba’?”
N'est-ce pas ici ce David, duquel on s'entre-répondait aux danses, en disant? Saül en a frappé ses mille et David ses dix mille?
6 Saboda haka Akish ya kira Dawuda ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, na amince da kai tun daga ranar da ka zo wurina har yă zuwa yau, ban same ka da wani laifi ba, na kuma yi farin ciki in sa ka a cikin sojojina don ka yi mini aiki. Amma masu mulki nawa ba su yarda da kai ba.
Akis donc appela David, et lui dit: L'Eternel est vivant, que tu es certainement un homme droit, et que ta conduite au camp m'a paru bonne, car je n'ai point trouvé de mal en toi, depuis le jour que tu es venu à moi jusqu'à ce jour; mais tu ne plais point aux Gouverneurs.
7 Sai ka juya ka koma ka isa lafiya ba tare da ɓata wa masu mulkin Filistiyawa rai ba.”
Maintenant donc retourne-t'en, et t'en va en paix, afin que tu ne fasses aucune chose qui déplaise aux Gouverneurs des Philistins.
8 Dawuda ya ce wa Akish, “Me na yi? Ka taɓa samun bawanka da laifi tun daga ranar da na zo har zuwa yanzu? Ina dalilin da ba zan tafi tare da kai in yaƙi maƙiyin ranka yă daɗe, sarki ba?”
Et David dit à Akis: Mais qu'ai-je fait? et qu'as-tu trouvé en ton serviteur depuis le jour que j'ai été avec toi jusqu'à ce jour, que je n'aille point combattre contre les ennemis du Roi mon Seigneur?
9 Akish ya ce, “A ganina kai marar laifi ne kamar mala’ikan Allah, duk da haka shugabannin sojojin Filistiyawa sun ce, ‘Ba zai tafi yaƙi tare da mu ba.’
Et Akis répondit et dit à David: Je le sais: car tu es agréable à mes yeux, comme un Ange de Dieu; mais c'est seulement que les chefs des Philistins ont dit: Il ne montera point avec nous dans la bataille.
10 Ka tashi da sassafe, kai da bayin shugabanka da suka zo tare da kai. Da gari ya waye sai ku kama hanya.”
C'est pourquoi lève-toi de bon matin, avec les serviteurs de ton Seigneur qui sont venus avec toi; et étant levés de bon matin, sitôt que vous verrez le jour, allez-vous-en.
11 Gari na wayewa tun da sassafe Dawuda da mutanensa suka tashi suka kama hanyar komawa ƙasar Filistiyawa. Filistiyawa kuwa suka haura zuwa Yezireyel.
Ainsi David se leva de bon matin, lui et ses gens, pour partir dès le matin, [et] s'en retourner au pays des Philistins; mais les Philistins montèrent à Jizréhel.

< 1 Sama’ila 29 >