< 1 Sama’ila 29 >

1 Filistiyawa suka tattara dukan rundunoninsu a Afek. Isra’ila kuwa suka yi sansani kusa da maɓulɓular da take Yezireyel.
Les Philistins rassemblèrent toutes leurs troupes à Aphec, et Israël était campé près de la source, en Jezraël.
2 Sa’ad da sarakuna Filistiyawa suke wucewa da rundunarsu na mutum ɗari-ɗari da na dubu-dubu. Dawuda da mutanensa suna biye a baya tare da Akish.
Pendant que les princes des Philistins s'avançaient en tête des centaines et des milliers, et que David et ses gens marchaient à l'arrière-garde avec Achis,
3 Komandodin Filistiyawa suka ce, “Waɗannan Ibraniyawa kuma fa?” Akish ya ce, “Wannan shi ne Dawuda hafsan Shawulu, sarkin Isra’ila. Yana nan tare da ni shekara guda ke nan. Ban kuwa taɓa samunsa da wani lahani ba tun daga ranar da ya bar Shawulu.”
les chefs des Philistins dirent: « Qu'est-ce que ces Hébreux? » Achis répondit aux chefs des Philistins: « N'est-ce pas ce David, serviteur de Saül, roi d'Israël, qui est avec moi depuis des jours et depuis des années, sans que j'aie trouvé en lui la moindre chose à reprocher, depuis qu'il a passé vers nous jusqu'à ce jour. »
4 Amma komandodin Filistiyawa suka yi fushi, suka ce, “Ka sa mutumin nan yă koma zuwa wurin da ka ba shi yă zauna. Ba zai bi mu zuwa wurin yaƙi ba. Yana iya juya a kanmu lokacin yaƙin. Zai iya yin amfani da wannan zarafi yă ciccire kawunanmu don yă faranta wa maigidansa rai?
Mais les chefs des Philistins s'irritèrent contre Achis, et les chefs des Philistins lui dirent: « Renvoie cet homme, et qu'il retourne dans le lieu où tu l'as établi; qu'il ne descende pas avec nous à la bataille, de peur qu'il ne soit pour nous un adversaire pendant le combat. Et comment pourrait-il rentrer en grâce auprès de son maître, si ce n'est en lui offrant les têtes de ces hommes?
5 Tuna fa, ba shi ne Dawuda ɗin da ake girmama da rawa da waƙoƙi ana cewa, “‘Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa dubbun dubbai ba’?”
N'est-ce pas ce David pour qui l'on chantait en dansant: Saül a tué ses mille, et David ses dix mille. »
6 Saboda haka Akish ya kira Dawuda ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, na amince da kai tun daga ranar da ka zo wurina har yă zuwa yau, ban same ka da wani laifi ba, na kuma yi farin ciki in sa ka a cikin sojojina don ka yi mini aiki. Amma masu mulki nawa ba su yarda da kai ba.
Achis appela David et lui dit: « Aussi vrai que Yahweh est vivant! tu es un homme droit, et je vois de bon œil toute ta conduite avec moi dans le camp, car je n'ai rien trouvé de mauvais en toi, depuis le jour où tu es venu vers moi jusqu'à ce jour; mais tu déplais aux yeux des princes.
7 Sai ka juya ka koma ka isa lafiya ba tare da ɓata wa masu mulkin Filistiyawa rai ba.”
Retourne donc et va-t-en en paix, pour ne rien faire de désagréable aux yeux des princes des Philistins. »
8 Dawuda ya ce wa Akish, “Me na yi? Ka taɓa samun bawanka da laifi tun daga ranar da na zo har zuwa yanzu? Ina dalilin da ba zan tafi tare da kai in yaƙi maƙiyin ranka yă daɗe, sarki ba?”
David dit à Achis: « Mais qu'ai-je fait, et qu'as-tu trouvé en ton serviteur, depuis le jour où je suis venu auprès de toi jusqu'à ce jour, pour que je n'aille pas combattre les ennemis de mon seigneur le roi? »
9 Akish ya ce, “A ganina kai marar laifi ne kamar mala’ikan Allah, duk da haka shugabannin sojojin Filistiyawa sun ce, ‘Ba zai tafi yaƙi tare da mu ba.’
Achis répondit et dit à David: « Je sais que tu as été bon à mon égard comme un ange de Dieu; mais les chefs des Philistins disent: il ne montera point avec nous à la bataille.
10 Ka tashi da sassafe, kai da bayin shugabanka da suka zo tare da kai. Da gari ya waye sai ku kama hanya.”
Ainsi lève-toi de bon matin, toi et les serviteurs de ton seigneur qui sont venus avec toi; levez-vous de bon matin, et dès qu'il fera jour, partez. »
11 Gari na wayewa tun da sassafe Dawuda da mutanensa suka tashi suka kama hanyar komawa ƙasar Filistiyawa. Filistiyawa kuwa suka haura zuwa Yezireyel.
David et ses gens se levèrent de bonne heure, pour partir dès le matin et retourner au pays des Philistins; et les Philistins montèrent à Jezraël.

< 1 Sama’ila 29 >