< 1 Sama’ila 28 >

1 Filistiyawa suka tattara sojojinsu domin su yaƙi Isra’ila. Akish ya ce wa Dawuda, “Sai ka sani fa, kai da mutanenka za ku tafi tare da ni da sojojina.”
O sırada Filistliler İsrail'le savaşmak için askeri birliklerini topladılar. Akiş Davut'a, “Adamlarınla birlikte benim yanımda savaşacağını bilmelisin” dedi.
2 Dawuda ya ce, “Kai da kanka za ka ga abin da bawanka zai yi.” Akish ya ce, “Da kyau, zan sa ka zama mai kāre ni.”
Davut, “O zaman sen de kulunun neler yapabileceğini göreceksin!” diye karşılık verdi. Akiş, “İyi!” dedi, “Yaşadığın sürece seni kendime koruma görevlisi atayacağım.”
3 Sama’ila dai ya riga ya rasu, dukan Isra’ila suka yi makokinsa suka binne shi a garinsa a Rama. Shawulu kuma ya kori duk masu duba da masu maitanci daga ƙasar.
Samuel ölmüş, bütün İsrail halkı onun için yas tutmuştu. Onu kendi kenti Rama'da gömmüşlerdi. Saul da cincilerle ruhlara danışanları ülkeden kovmuştu.
4 Filistiyawa suka tattaru suka yi sansani a Shunem. Shawulu ya tattara dukan Isra’ila suka yi sansani a Gilbowa.
Filistliler toplanıp Şunem'e gittiler ve orada ordugah kurdular. Saul da bütün İsrailliler'i toplayıp Gilboa Dağı'nda ordugah kurdu.
5 Da Shawulu ya ga sojojin Filistiyawa sai ya ji tsoro, ya firgita ƙwarai.
Saul Filist ordusunu görünce korkup büyük dehşete kapıldı.
6 Ya nemi nufin Ubangiji amma bai sami amsa daga wurin Ubangiji ko ta wurin mafarki, ko ta wurin Urim, ko ta wurin annabawa ba.
RAB'be danıştıysa da, RAB ona ne düşlerle, ne Urim, ne de peygamberler aracılığıyla yanıt verdi.
7 Shawulu ya ce wa fadawansa, “Ku nemo mini wata mace mai duba domin in tafi wurinta in yi tambaya.” Suka ce, “Akwai guda a En Dor.”
Bunun üzerine Saul görevlilerine, “Bana bir cinci kadın bulun da varıp ona danışayım” diye buyruk verdi. Görevliler, “Eyn-Dor'da bir cinci kadın var” dediler.
8 Sai Shawulu ya sa waɗansu tufafi ya ɓad da kama, shi da waɗansu mutum biyu suka tafi wurin matar da dare, ya ce mata, “Ki yi mini duba ta hanyar sihiri, ki hawar mini duk wanda zan faɗa miki.”
Böylece Saul başka giysilere bürünüp kılığını değiştirdi. Geceleyin yanına iki kişi alıp kadının yaşadığı yere gitti. Kadına, “Lütfen benim için ruhlara danış ve sana söyleyeceğim kişiyi çağır” dedi.
9 Amma matar ta ce masa, “Tabbatacce ka dai san abin da Shawulu ya yi, ya karkashe masu duba da masu maitanci a ƙasar. Me ya sa kake sa mini tarko, don ka sa a kashe ni?”
Ama kadın ona şu karşılığı verdi: “Saul'un neler yaptığını, cincilerle ruhlara danışanları ülkeden kovduğunu biliyorsun. Öyleyse neden beni öldürmek için tuzak kuruyorsun?”
10 Shawulu ya rantse mata da Ubangiji. Ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a hukunta ki a kan wannan ba.”
Saul, “Yaşayan RAB'bin adıyla derim ki, bundan sana bir kötülük gelmeyecek” diye ant içti.
11 Sai matar ta ce, “Wa kake so in hauro maka?” Sai ya ce, “Ki hauro mini da Sama’ila.”
Bunun üzerine kadın, “Sana kimi çağırayım?” diye sordu. Saul, “Bana Samuel'i çağır” dedi.
12 Da matar ta ga Sama’ila sai ta yi ihu da ƙarfi ta ce wa Shawulu, “Me ya sa ka ruɗe ni? Kai ne Shawulu!”
Kadın, Samuel'i görünce çığlık atarak, “Sen Saul'sun! Neden beni kandırdın?” dedi.
13 Sai sarki ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Me kika gani?” Matar ta ce, “Na ga wani kurwa tana fitowa daga ƙasa.”
Kral ona, “Korkma!” dedi, “Ne görüyorsun?” Kadın, “Yerin altından çıkan bir ilah görüyorum” diye karşılık verdi.
14 Ya ce, “Yaya kamanninsa yake?” Ta ce, “Wani tsoho sanye da taguwa ne yake haurawa.” Shawulu ya gane cewa Sama’ila ne, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
Saul, “Neye benziyor?” diye sordu. Kadın, “Cüppe giymiş yaşlı bir adam yukarıya çıkıyor” dedi. O zaman Saul onun Samuel olduğunu anladı; eğilip yüzüstü yere kapandı.
15 Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Don me ka dame ni, ta wurin hauro da ni?” Shawulu ya ce, “Ina cikin babban damuwa ce, Filistiyawa sun fāɗa mini, Allah kuma ya juya mini baya. Bai amsa mini, ko ta mafarki, ko kuma ta annabawa ba, saboda haka na kira ka don ka gaya mini abin yi.”
Samuel Saul'a, “Neden beni çağırtıp rahatsız ettin?” dedi. Saul, “Büyük sıkıntı içindeyim” diye yanıtladı, “Filistliler bana karşı savaşıyor ve Tanrı da beni terk etti. Artık bana ne peygamberler aracılığıyla, ne de düşlerle yanıt veriyor. Bu yüzden, ne yapmam gerektiğini bana bildirmen için seni çağırttım.”
16 Sama’ila ya ce, “Don me kake tambayata bayan Ubangiji ya rabu da kai? Ya zama maƙiyinka?
Samuel, “RAB seni terk edip sana düşman olduğuna göre, neden bana danışıyorsun?” dedi,
17 Ubangiji ya cika abin da ya yi magana ta wurina. Ubangiji ya fizge mulki daga hannunka, ya ba maƙwabcinka Dawuda.
“RAB benim aracılığımla söylediğini yaptı, krallığı senden alıp soydaşın Davut'a verdi.
18 Gama ba ka yi biyayya ga Ubangiji ba, ba ka zartar da hukuncinsa mai zafi a kan Amalekawa ba. Saboda haka Ubangiji ya yi maka haka yau.
Çünkü sen RAB'bin buyruğuna uymadın, O'nun alevlenen öfkesini Amalekliler'e uygulamadın. RAB bugün bunları bu yüzden başına getirdi.
19 Ubangiji zai ba da Isra’ila da kuma kai ga Filistiyawa, gobe kuwa da kai da’ya’yanka za ku kasance tare da ni. Ubangiji kuma zai ba da sojojin Isra’ila a hannun Filistiyawa.”
RAB seni de, İsrail halkını da Filistliler'in eline teslim edecek. Yarın sen ve oğulların bana katılacaksınız. RAB İsrail ordusunu da Filistliler'in eline teslim edecek.”
20 Da jin maganar Sama’ila sai Shawulu ya faɗi ƙasa warwas. Tsoro ya kama shi ƙwarai. Ba shi kuma da ƙarfi domin bai ci kome ba dukan yini da kuma dukan dare.
Saul birden boylu boyunca yere düştü. Samuel'in sözlerinden ötürü büyük korkuya kapıldı. Gücü de kalmamıştı; çünkü bütün gün, bütün gece yemek yememişti.
21 Da matar ta zo wurin Shawulu, ta ga shi a firgice, sai ta ce masa, “Duba baranyarka ta yi maka biyayya ta yi kasai da ranta, ta yi abin da ka ce ta yi.
Kadın Saul'a yaklaştı. Onun büyük şaşkınlık içinde olduğunu görünce, “Bak, kölen sözünü dinledi” dedi, “Canımı tehlikeye atarak benden istediğini yaptım.
22 To, kai ma ka kasa kunne ga baranyarka, zan ba ka abinci ka ci don ka sami ƙarfin tafiya.”
Şimdi lütfen kölenin söyleyeceğini dinle. İzin ver de, önüne biraz yemek koyayım. Yoluna devam edecek gücün olması için yemek yemelisin.”
23 Sai ya ƙi. Ya ce, “Ba zan ci abinci ba.” Sai da bayinsa da matar suka roƙe shi, sa’an nan ya ji maganarsu, ya tashi daga ƙasa, ya zauna a bakin gado.
Ama Saul, “Yemem” diyerek reddetti. Ancak hizmetkârlarıyla kadın zorlayınca, onların dediğini yaptı. Yerden kalkıp yatağın üzerine oturdu.
24 Matar kuwa tana da maraƙin da take kiwo a gida, sai ta ɗauke shi nan da nan ta yanka. Ta ɗauki garin fulawa ta kwaɓa, ta yi waina marar yisti.
Kadının evinde besili bir dana vardı. Kadın onu hemen kesti. Un alıp yoğurdu ve mayasız ekmek pişirdi.
25 Sai ta kawo wa Shawulu da bayinsa suka kuwa ci. A daren nan suka tashi suka tafi.
Sonra Saul'la görevlilerinin önüne koydu. Onlar da yediler. Sonra o gece kalkıp gittiler.

< 1 Sama’ila 28 >