< 1 Sama’ila 28 >

1 Filistiyawa suka tattara sojojinsu domin su yaƙi Isra’ila. Akish ya ce wa Dawuda, “Sai ka sani fa, kai da mutanenka za ku tafi tare da ni da sojojina.”
Mane gahbışil İzrailybışika səvxəsva, Filiştinaaşe con g'oşunbı sacigeeqa sa'a ıxha. Akişee Davuduk'le eyhen: – İn vak'le ats'axhxhe, ğunayiy yiğın insanar yizde sural, yişde g'oşunee vuxhes.
2 Dawuda ya ce, “Kai da kanka za ka ga abin da bawanka zai yi.” Akish ya ce, “Da kyau, zan sa ka zama mai kāre ni.”
Davudee Akişik'le eyhen: – Geed yugda! Zasse, yiğne nukarısse hucooyiy ha'as əxəva, vak'lecad g'acesın. Akişee Davuduk'le eyhen: – Geed yugda, zı vake, zı qik'asmee, yizda can gyuden ha'as.
3 Sama’ila dai ya riga ya rasu, dukan Isra’ila suka yi makokinsa suka binne shi a garinsa a Rama. Shawulu kuma ya kori duk masu duba da masu maitanci daga ƙasar.
Şamuel qık'uyng'a, gırgıne İzrailyne xalq'ın mang'us ak' avqu. Mana Ramayee, cune şahareecar, k'eyxhı. Mane gahıl Şaulee ölkeençe cadubı ha'anbıyiy hapt'ıynbışin rı'hbı qoot'alan gırgınbı ge'eepşı vuxha.
4 Filistiyawa suka tattaru suka yi sansani a Shunem. Shawulu ya tattara dukan Isra’ila suka yi sansani a Gilbowa.
Filiştinar sabı-qabı, Şunemee eyhene şaharee zastava giviyxhe. Şauleeyib gırgın İzrailybı sav'u, Gilboa eyhene suval zastava giviyxhe.
5 Da Shawulu ya ga sojojin Filistiyawa sai ya ji tsoro, ya firgita ƙwarai.
Şauluk'le Filiştinaaşda zastava g'avcumee, qərq'ı'niyvalin mang'un yik' sacuraycad qa'a.
6 Ya nemi nufin Ubangiji amma bai sami amsa daga wurin Ubangiji ko ta wurin mafarki, ko ta wurin Urim, ko ta wurin annabawa ba.
Mang'vee Rəbbike qiyghan, Rəbbeemee mang'us cuvab nik'eeyid, kaahinıle ğanad, peyğambaraaşiled ğanad nəxüdcad qele deş.
7 Shawulu ya ce wa fadawansa, “Ku nemo mini wata mace mai duba domin in tafi wurinta in yi tambaya.” Suka ce, “Akwai guda a En Dor.”
Şaulee cune insanaaşik'le eyhen: – Yizdemee, hapt'ıynbışin rı'hbı qoot'alna sa zəiyfa t'abal hee'e. Zı məng'ı'kexheeyid hark'ın qiyghanas. Mang'une insanaaşe eyhen: – En-Doree sa məxürna zəiyfa vorna.
8 Sai Shawulu ya sa waɗansu tufafi ya ɓad da kama, shi da waɗansu mutum biyu suka tafi wurin matar da dare, ya ce mata, “Ki yi mini duba ta hanyar sihiri, ki hawar mini duk wanda zan faɗa miki.”
Şaulee cune tanalin paççahaaşin karbı g'ayşu, medınbı ali'ı, q'öyre insanır qort'ul, maqa hayk'an. Mana xəmde mana zəiyfa eexvane cigeeqa hiyxhar. Şaulee məng'ı'k'le eyhen: – Yizdemee, zı eyhene qik'uyng'un rı'h qot'le.
9 Amma matar ta ce masa, “Tabbatacce ka dai san abin da Shawulu ya yi, ya karkashe masu duba da masu maitanci a ƙasar. Me ya sa kake sa mini tarko, don ka sa a kashe ni?”
Zəiyfee eyhen: – Vak'lecad ats'an, Şaulee ine ölkee hı'iyn. Mang'vee ine ölkeençe cadubı ha'anbıyiy hapt'ıynbışin rı'hbı qoot'alan gırgınbı g'eepşıynbı. Nişil-allane zı qiyk'ecenva, ğu zas gugu haa'a?
10 Shawulu ya rantse mata da Ubangiji. Ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a hukunta ki a kan wannan ba.”
Şaulee zəiyfayk'le eyhen: – Vorne Rəbbilqan k'ın ixhenva eyhe, ine işil-alla vak vuççud ixhes deş.
11 Sai matar ta ce, “Wa kake so in hauro maka?” Sai ya ce, “Ki hauro mini da Sama’ila.”
Zəiyfee eyhen: – Yiğnemee vuşune qot'le? Şaulee «Zasqa Şamuel qot'leva» eyhe.
12 Da matar ta ga Sama’ila sai ta yi ihu da ƙarfi ta ce wa Shawulu, “Me ya sa ka ruɗe ni? Kai ne Shawulu!”
Zəiyfayk'le Şamuel g'acuys it'umna bagaray hav'u, eyhen: – Voo, ğu Şaulur, nya'a zas horbı hı'ı?
13 Sai sarki ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Me kika gani?” Matar ta ce, “Na ga wani kurwa tana fitowa daga ƙasa.”
Paççahee məng'ı'k'le eyhen: – Qı'meeq'ən, eyhe vak'le hucooyiy g'ece? Zəiyfee eyhen: – Ç'iyek avğançe qı'ğəən rı'h g'ece.
14 Ya ce, “Yaya kamanninsa yake?” Ta ce, “Wani tsoho sanye da taguwa ne yake haurawa.” Shawulu ya gane cewa Sama’ila ne, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
Şaulee qiyghanan: – Mana şavukiy akar? Zəiyfee eyhen: – P'laş ali'ına sa q'əsda adamiyır qığəə. Şauluk'le mana Şamuel ıxhay ats'axhxha, mang'us ç'iyelqamee k'yoyzarna.
15 Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Don me ka dame ni, ta wurin hauro da ni?” Shawulu ya ce, “Ina cikin babban damuwa ce, Filistiyawa sun fāɗa mini, Allah kuma ya juya mini baya. Bai amsa mini, ko ta mafarki, ko kuma ta annabawa ba, saboda haka na kira ka don ka gaya mini abin yi.”
Şamuelee Şauluk'le eyhen: – Nişisne ğu zı ı'giykar ha'a? Nişisne qoyt'al? Şaulee eyhen: – Zı xənne dağamiyvaleeqa girxhu vor. Filiştinar zalqa k'yophur, Allaheeyid zale aq'va sak'al hı'ı. Mang'vee peyğambaraaşile ğanad, nik'eeyid zas cuvab qele deş. Mançil-allar zı ğu qort'ul, zak'le eyheva, zı hucooyiy ha'as ıkkan.
16 Sama’ila ya ce, “Don me kake tambayata bayan Ubangiji ya rabu da kai? Ya zama maƙiyinka?
Şamuelee eyhen: – Rəbbee vake aq'va sak'al hı'ı, Mana yiğna duşman ıxha. Maa'ad zake qiyghanasın hucooyiy?
17 Ubangiji ya cika abin da ya yi magana ta wurina. Ubangiji ya fizge mulki daga hannunka, ya ba maƙwabcinka Dawuda.
Rəbbee zale ğana vak'le uvhuyn, həşde hı'iyn. Mang'vee paççahiyvalla yiğne xılençe g'avşu, yiğne k'anerıng'usqa, Davudusqa quvu.
18 Gama ba ka yi biyayya ga Ubangiji ba, ba ka zartar da hukuncinsa mai zafi a kan Amalekawa ba. Saboda haka Ubangiji ya yi maka haka yau.
Ğu Rəbbine cuvabıl k'ırı alixhxhı deş, Mang'una qəl Amalekbışike qığavhu deş. G'iyna dişe, Mang'vee valqa ina ver ablyav'u.
19 Ubangiji zai ba da Isra’ila da kuma kai ga Filistiyawa, gobe kuwa da kai da’ya’yanka za ku kasance tare da ni. Ubangiji kuma zai ba da sojojin Isra’ila a hannun Filistiyawa.”
Rəbbee vaka sacigee İzrailib Filiştinaaşde xılyaqa qevles. G'iyqa ğunar yiğın dixbıb yizde k'ane vuxhes. Rəbbee İzrailyna g'oşunub çikana Filiştinaaşde xılyaqa qevles.
20 Da jin maganar Sama’ila sai Shawulu ya faɗi ƙasa warwas. Tsoro ya kama shi ƙwarai. Ba shi kuma da ƙarfi domin bai ci kome ba dukan yini da kuma dukan dare.
Şamuelee eyhenbı g'ayxhı, Şaul qərq'ı'niyvalin ç'iyelqa qukkyoyk'al. Mang'vee bıkırne xəmnayiy yiğna kar udyotxhun ıxhayke, mang'uqa taq'at axva deş.
21 Da matar ta zo wurin Shawulu, ta ga shi a firgice, sai ta ce masa, “Duba baranyarka ta yi maka biyayya ta yi kasai da ranta, ta yi abin da ka ce ta yi.
Zəiyfa Şaulusqa qiyxhamee, mana sacuray qıxha g'acu, eyhen: – Zı, yiğne nukaree, val k'ırı alixhxhıyn. Zı qiyk'uyle qiyeeq'ən yixheeyir, meed ğu uvhuyn hı'iyncad.
22 To, kai ma ka kasa kunne ga baranyarka, zan ba ka abinci ka ci don ka sami ƙarfin tafiya.”
Hucoona ixhes, həşde yiğne nukarne cuvabıl k'ırı alixhxhe, zı yiğne ögeeqa sa ghaledın gıney gixhxhes, man oxhne. Yəqqı'lqa qığəmee, taq'at ixhecen.
23 Sai ya ƙi. Ya ce, “Ba zan ci abinci ba.” Sai da bayinsa da matar suka roƙe shi, sa’an nan ya ji maganarsu, ya tashi daga ƙasa, ya zauna a bakin gado.
Şaulee «Deş ıkkanva» eyhe. Cune insanaaşed zəiyfayka sacigee mana kar oxhanas ilekkamee, mang'vee manbışil k'ırı iliyxhen. Mana ç'iyele oza qıxha, tyulee g'iya'ar.
24 Matar kuwa tana da maraƙin da take kiwo a gida, sai ta ɗauke shi nan da nan ta yanka. Ta ɗauki garin fulawa ta kwaɓa, ta yi waina marar yisti.
Zəiyfayqa xaa tavulyna dana vooxhe. Məng'ee mana zaraba givk'u, urvad alyaat'u balatıy deşin gıney ha'a.
25 Sai ta kawo wa Shawulu da bayinsa suka kuwa ci. A daren nan suka tashi suka tafi.
Qiyğa məng'ee man Şaulneyiy cune insanaaşine ögilqa giyxhe. Manbışe man otxhun, manecab xəmde oza qeepxha avayk'ananbı.

< 1 Sama’ila 28 >