< 1 Sama’ila 28 >

1 Filistiyawa suka tattara sojojinsu domin su yaƙi Isra’ila. Akish ya ce wa Dawuda, “Sai ka sani fa, kai da mutanenka za ku tafi tare da ni da sojojina.”
Or, il arriva, en ces jours-là, que les Philistins assemblèrent leurs troupes, pour se préparer à la guerre contre Israël; et Achis dit à David: Sache bien que tu viendras avec moi dans mon camp, toi et tes hommes.
2 Dawuda ya ce, “Kai da kanka za ka ga abin da bawanka zai yi.” Akish ya ce, “Da kyau, zan sa ka zama mai kāre ni.”
Et David répondit à Achis: Maintenant vous saurez ce que votre serviteur doit faire. Achis dit encore à David: Et moi je t’établirai garde de ma personne pour toujours.
3 Sama’ila dai ya riga ya rasu, dukan Isra’ila suka yi makokinsa suka binne shi a garinsa a Rama. Shawulu kuma ya kori duk masu duba da masu maitanci daga ƙasar.
Or, Samuel était mort, tout le peuple d’Israël l’avait pleuré, et ils l’avaient enseveli à Ramatha, sa ville. Et Saül avait chassé les magiciens et les devins de son pays.
4 Filistiyawa suka tattaru suka yi sansani a Shunem. Shawulu ya tattara dukan Isra’ila suka yi sansani a Gilbowa.
Et les Philistins s’assemblèrent et vinrent, et ils campèrent à Sunam; mais Saül aussi assembla tout Israël, et vint à Gelboé.
5 Da Shawulu ya ga sojojin Filistiyawa sai ya ji tsoro, ya firgita ƙwarai.
Et Saül vit le camp des Philistins, et il craignit, et son cœur fut tout saisi d’épouvante.
6 Ya nemi nufin Ubangiji amma bai sami amsa daga wurin Ubangiji ko ta wurin mafarki, ko ta wurin Urim, ko ta wurin annabawa ba.
Et il consulta le Seigneur, et le Seigneur ne lui répondit point, ni par des songes, ni par les prêtres, ni par les prophètes.
7 Shawulu ya ce wa fadawansa, “Ku nemo mini wata mace mai duba domin in tafi wurinta in yi tambaya.” Suka ce, “Akwai guda a En Dor.”
Alors Saül dit à ses serviteurs: Cherchez-moi une femme ayant un esprit de python, et j’irai à elle, et je l’interrogerai. Et ses serviteurs lui répondirent: II y a à Endor une femme qui a un esprit de python.
8 Sai Shawulu ya sa waɗansu tufafi ya ɓad da kama, shi da waɗansu mutum biyu suka tafi wurin matar da dare, ya ce mata, “Ki yi mini duba ta hanyar sihiri, ki hawar mini duk wanda zan faɗa miki.”
Il changea donc son habillement, se revêtit d’autres vêtements, et s’en alla, lui et deux hommes avec lui, et ils vinrent vers la femme pendant la nuit, et il lui dit: Devine pour moi par l’esprit de python, et évoque-moi celui que je te dirai.
9 Amma matar ta ce masa, “Tabbatacce ka dai san abin da Shawulu ya yi, ya karkashe masu duba da masu maitanci a ƙasar. Me ya sa kake sa mini tarko, don ka sa a kashe ni?”
Et la femme lui répondit: Voilà que tu sais tout ce qu’a fait Saül, et de quelle manière il a exterminé de la terre les magiciens et les devins; pourquoi donc tends-tu des pièges à mon âme, pour que je sois tuée?
10 Shawulu ya rantse mata da Ubangiji. Ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a hukunta ki a kan wannan ba.”
Et Saül lui jura par le Seigneur, disant: Le Seigneur vit! il ne t’arrivera rien de mal à cause de ceci.
11 Sai matar ta ce, “Wa kake so in hauro maka?” Sai ya ce, “Ki hauro mini da Sama’ila.”
Et la femme lui demanda: Qui t’évoquerai-je? Il répondit: Evoque-moi Samuel.
12 Da matar ta ga Sama’ila sai ta yi ihu da ƙarfi ta ce wa Shawulu, “Me ya sa ka ruɗe ni? Kai ne Shawulu!”
Or, quand la femme eut vu Samuel, elle s’écria à haute voix, et dit à Saül: Pourquoi m’en avez-vous imposé? car vous êtes Saül.
13 Sai sarki ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Me kika gani?” Matar ta ce, “Na ga wani kurwa tana fitowa daga ƙasa.”
Alors le roi lui dit: Ne crains point; qu’as-tu vu? Et la femme répondit à Saül: Ce sont des dieux que j’ai vus montant de la terre.
14 Ya ce, “Yaya kamanninsa yake?” Ta ce, “Wani tsoho sanye da taguwa ne yake haurawa.” Shawulu ya gane cewa Sama’ila ne, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
Et il lui demanda: Quelle est sa forme? Elle répondit: Un vieillard est monté, et il est couvert d’un manteau. Et Saül comprit que c’était Samuel, et il s’inclina sur sa face vers la terre, et il se prosterna.
15 Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Don me ka dame ni, ta wurin hauro da ni?” Shawulu ya ce, “Ina cikin babban damuwa ce, Filistiyawa sun fāɗa mini, Allah kuma ya juya mini baya. Bai amsa mini, ko ta mafarki, ko kuma ta annabawa ba, saboda haka na kira ka don ka gaya mini abin yi.”
Or Samuel dit à Saül: Pourquoi m’avez-vous troublé, de sorte que je fusse évoqué? Et Saül répondit: Je suis dans une grande contrainte; puisque les Philistins combattent contre moi, que Dieu s’est retiré de moi, et qu’il n’a point voulu m’entendre ni par l’entremise des prophètes, ni par des songes; je vous ai donc appelé, pour que vous me montriez ce que je dois faire.
16 Sama’ila ya ce, “Don me kake tambayata bayan Ubangiji ya rabu da kai? Ya zama maƙiyinka?
Et Samuel répliqua: Pourquoi m’interrogez-vous, puisque le Seigneur s’est retiré de vous, et qu’il est passé à votre rival?
17 Ubangiji ya cika abin da ya yi magana ta wurina. Ubangiji ya fizge mulki daga hannunka, ya ba maƙwabcinka Dawuda.
Car le Seigneur vous fera, comme il a dit par mon entremise, et il divisera votre royaume en l’arrachant de votre main, et il le donnera à votre parent David,
18 Gama ba ka yi biyayya ga Ubangiji ba, ba ka zartar da hukuncinsa mai zafi a kan Amalekawa ba. Saboda haka Ubangiji ya yi maka haka yau.
Parce que vous n’avez pas obéi à la voix du Seigneur, et vous n’avez pas accompli la colère de sa fureur contre Amalec; c’est pour cela que ce que vous souffrez, le Seigneur vous l’a fait aujourd’hui.
19 Ubangiji zai ba da Isra’ila da kuma kai ga Filistiyawa, gobe kuwa da kai da’ya’yanka za ku kasance tare da ni. Ubangiji kuma zai ba da sojojin Isra’ila a hannun Filistiyawa.”
Et le Seigneur abandonnera aussi Israël avec vous aux mains des Philistins; mais demain vous et vos fils vous serez avec moi; et même le camp d’Israël, le Seigneur le livrera aux Philistins.
20 Da jin maganar Sama’ila sai Shawulu ya faɗi ƙasa warwas. Tsoro ya kama shi ƙwarai. Ba shi kuma da ƙarfi domin bai ci kome ba dukan yini da kuma dukan dare.
Et aussitôt Saül tomba et resta étendu sur la terre; car il avait été épouvanté des paroles de Samuel, et il n’y avait pas de force en lui, parce qu’il n’avait pas mangé de pain durant tout ce jour-là.
21 Da matar ta zo wurin Shawulu, ta ga shi a firgice, sai ta ce masa, “Duba baranyarka ta yi maka biyayya ta yi kasai da ranta, ta yi abin da ka ce ta yi.
C’est pourquoi cette femme vint vers Saül (car il était fort troublé), et elle lui dit: Voilà que votre servante a obéi à votre voix, et j’ai mis mon âme en ma main, et j’ai écouté vos paroles, que vous m’avez dites.
22 To, kai ma ka kasa kunne ga baranyarka, zan ba ka abinci ka ci don ka sami ƙarfin tafiya.”
Maintenant donc écoutez, vous aussi, la voix de votre servante, et je mettrai devant vous une bouchée de pain, afin que mangeant, vous repreniez vos forces, et que vous puissiez faire la route.
23 Sai ya ƙi. Ya ce, “Ba zan ci abinci ba.” Sai da bayinsa da matar suka roƙe shi, sa’an nan ya ji maganarsu, ya tashi daga ƙasa, ya zauna a bakin gado.
Saül refusa, et dit: Je ne mangerai point. Mais ses serviteurs et la femme le contraignirent, et enfin, leur voix écoutée, il se leva de terre, et s’assit sur le lit.
24 Matar kuwa tana da maraƙin da take kiwo a gida, sai ta ɗauke shi nan da nan ta yanka. Ta ɗauki garin fulawa ta kwaɓa, ta yi waina marar yisti.
Or, cette femme avait un veau gras en sa maison, elle se hâta, et le tua; puis prenant de la farine, elle la pétrit, et fit cuire des pains azymes,
25 Sai ta kawo wa Shawulu da bayinsa suka kuwa ci. A daren nan suka tashi suka tafi.
Et elle les mit devant Saül et devant ses serviteurs. Lorsqu’ils eurent mangé, ils se levèrent, et marchèrent durant toute cette nuit.

< 1 Sama’ila 28 >