< 1 Sama’ila 28 >

1 Filistiyawa suka tattara sojojinsu domin su yaƙi Isra’ila. Akish ya ce wa Dawuda, “Sai ka sani fa, kai da mutanenka za ku tafi tare da ni da sojojina.”
It came about in those days that the Philistines gathered their armies together for battle to fight with Israel. Achish said to David, “Know for certain that you will go out with me in the host, you and your men.”
2 Dawuda ya ce, “Kai da kanka za ka ga abin da bawanka zai yi.” Akish ya ce, “Da kyau, zan sa ka zama mai kāre ni.”
David said to Achish, “So you will know what your servant can do.” Achish said to David, “So I will make you my bodyguard all your days.”
3 Sama’ila dai ya riga ya rasu, dukan Isra’ila suka yi makokinsa suka binne shi a garinsa a Rama. Shawulu kuma ya kori duk masu duba da masu maitanci daga ƙasar.
Now Samuel had died, and all Israel had lamented him and buried him in Ramah, in his own city. Also, Saul had banned from the land those who talked with the dead or with spirits.
4 Filistiyawa suka tattaru suka yi sansani a Shunem. Shawulu ya tattara dukan Isra’ila suka yi sansani a Gilbowa.
Then the Philistines gathered themselves together and came and camped at Shunem; and Saul gathered all Israel together, and they camped at Gilboa.
5 Da Shawulu ya ga sojojin Filistiyawa sai ya ji tsoro, ya firgita ƙwarai.
When Saul saw the army of the Philistines, he was afraid, and his heart trembled very much.
6 Ya nemi nufin Ubangiji amma bai sami amsa daga wurin Ubangiji ko ta wurin mafarki, ko ta wurin Urim, ko ta wurin annabawa ba.
Saul prayed to Yahweh for help, but Yahweh did not answer him—neither by dreams, nor by Urim, nor by prophets.
7 Shawulu ya ce wa fadawansa, “Ku nemo mini wata mace mai duba domin in tafi wurinta in yi tambaya.” Suka ce, “Akwai guda a En Dor.”
Then Saul said to his servants, “Find me a woman who talks with the dead, so that I may go to her and seek her advice.” His servants said to him, “See, there is a woman in Endor who claims to talk with the dead.”
8 Sai Shawulu ya sa waɗansu tufafi ya ɓad da kama, shi da waɗansu mutum biyu suka tafi wurin matar da dare, ya ce mata, “Ki yi mini duba ta hanyar sihiri, ki hawar mini duk wanda zan faɗa miki.”
Saul disguised himself, put on other clothing, and went, he and two men with him; they went to the woman by night. He said, “Divine for me, I beg you, with a spirit, and bring me up whomever I name to you.”
9 Amma matar ta ce masa, “Tabbatacce ka dai san abin da Shawulu ya yi, ya karkashe masu duba da masu maitanci a ƙasar. Me ya sa kake sa mini tarko, don ka sa a kashe ni?”
The woman said to him, “See, you know what Saul has done, how he has banned from the land those who talk with the dead or with spirits. So why are you setting a trap for my life, to make me die?”
10 Shawulu ya rantse mata da Ubangiji. Ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a hukunta ki a kan wannan ba.”
Saul swore to her by Yahweh and said, “As Yahweh lives, no punishment will happen to you for this thing.”
11 Sai matar ta ce, “Wa kake so in hauro maka?” Sai ya ce, “Ki hauro mini da Sama’ila.”
Then the woman said, “Whom should I bring up to you?” Saul said, “Bring up Samuel for me.”
12 Da matar ta ga Sama’ila sai ta yi ihu da ƙarfi ta ce wa Shawulu, “Me ya sa ka ruɗe ni? Kai ne Shawulu!”
When the woman saw Samuel, she cried with a loud voice and spoke to Saul, saying, “Why have you deceived me? For you are Saul.”
13 Sai sarki ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Me kika gani?” Matar ta ce, “Na ga wani kurwa tana fitowa daga ƙasa.”
The king said to her, “Do not be afraid. What do you see?” The woman said to Saul, “I see a god coming up out of the earth.”
14 Ya ce, “Yaya kamanninsa yake?” Ta ce, “Wani tsoho sanye da taguwa ne yake haurawa.” Shawulu ya gane cewa Sama’ila ne, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
He said to her, “What does he look like?” She said, “An old man is coming up; he is clothed with a robe.” Saul perceived that it was Samuel, and he bowed with his face to the ground and showed respect.
15 Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Don me ka dame ni, ta wurin hauro da ni?” Shawulu ya ce, “Ina cikin babban damuwa ce, Filistiyawa sun fāɗa mini, Allah kuma ya juya mini baya. Bai amsa mini, ko ta mafarki, ko kuma ta annabawa ba, saboda haka na kira ka don ka gaya mini abin yi.”
Samuel said to Saul, “Why have you disturbed me and brought me up?” Saul answered, “I am very distressed, for the Philistines are waging war against me, and God has left me and does not answer me any more, neither by prophets, nor by dreams. Therefore I have called you, that you may make known to me what I will do.”
16 Sama’ila ya ce, “Don me kake tambayata bayan Ubangiji ya rabu da kai? Ya zama maƙiyinka?
Samuel said, “What then do you ask me, since Yahweh has left you, and he has become your enemy?
17 Ubangiji ya cika abin da ya yi magana ta wurina. Ubangiji ya fizge mulki daga hannunka, ya ba maƙwabcinka Dawuda.
Yahweh has done to you what he said he would. Yahweh has torn the kingdom out of your hand and he has given it to someone else—to David.
18 Gama ba ka yi biyayya ga Ubangiji ba, ba ka zartar da hukuncinsa mai zafi a kan Amalekawa ba. Saboda haka Ubangiji ya yi maka haka yau.
Because you did not obey the voice of Yahweh and did not carry out his fierce wrath on Amalek, he has therefore done this today to you.
19 Ubangiji zai ba da Isra’ila da kuma kai ga Filistiyawa, gobe kuwa da kai da’ya’yanka za ku kasance tare da ni. Ubangiji kuma zai ba da sojojin Isra’ila a hannun Filistiyawa.”
Yahweh will give Israel along with you into the hand of the Philistines, and tomorrow you and your sons will be with me. Yahweh will also give the army of Israel into the hand of the Philistines.”
20 Da jin maganar Sama’ila sai Shawulu ya faɗi ƙasa warwas. Tsoro ya kama shi ƙwarai. Ba shi kuma da ƙarfi domin bai ci kome ba dukan yini da kuma dukan dare.
Then Saul immediately fell his full length on the ground and was very afraid because of the words of Samuel. There was no strength in him, for he had eaten no food all that day, neither that whole night.
21 Da matar ta zo wurin Shawulu, ta ga shi a firgice, sai ta ce masa, “Duba baranyarka ta yi maka biyayya ta yi kasai da ranta, ta yi abin da ka ce ta yi.
The woman came to Saul and saw that he was very troubled, She said to him, “See, your woman servant has listened to your voice; I have put my life in my hand and have listened to the words that you said to me.
22 To, kai ma ka kasa kunne ga baranyarka, zan ba ka abinci ka ci don ka sami ƙarfin tafiya.”
Now therefore, I beg you, listen also to the voice of your woman servant, and let me set a little food in front of you. Eat so that you may gain strength for when you go on your way.”
23 Sai ya ƙi. Ya ce, “Ba zan ci abinci ba.” Sai da bayinsa da matar suka roƙe shi, sa’an nan ya ji maganarsu, ya tashi daga ƙasa, ya zauna a bakin gado.
But Saul refused and said, “I will not eat.” But his servants, together with the woman, compelled him, and he listened to their voice. So he rose from the ground and sat on the bed.
24 Matar kuwa tana da maraƙin da take kiwo a gida, sai ta ɗauke shi nan da nan ta yanka. Ta ɗauki garin fulawa ta kwaɓa, ta yi waina marar yisti.
The woman had a fatted calf in the house; she hurried and killed it; she took flour, kneaded it, and baked unleavened bread with it.
25 Sai ta kawo wa Shawulu da bayinsa suka kuwa ci. A daren nan suka tashi suka tafi.
She brought it before Saul and his servants, and they ate. Then they got up and left that night.

< 1 Sama’ila 28 >