< 1 Sama’ila 28 >

1 Filistiyawa suka tattara sojojinsu domin su yaƙi Isra’ila. Akish ya ce wa Dawuda, “Sai ka sani fa, kai da mutanenka za ku tafi tare da ni da sojojina.”
Some time later, the people of Philistia gathered their army to attack the Israelis [again]. King Achish told David, “I am expecting that you and your men will join with my men to attack [the Israelis].”
2 Dawuda ya ce, “Kai da kanka za ka ga abin da bawanka zai yi.” Akish ya ce, “Da kyau, zan sa ka zama mai kāre ni.”
David replied, “[We will go with you, and then] you will see for yourself what we can do!” Achish said, “Okay, I will appoint you to be my bodyguard permanently.”
3 Sama’ila dai ya riga ya rasu, dukan Isra’ila suka yi makokinsa suka binne shi a garinsa a Rama. Shawulu kuma ya kori duk masu duba da masu maitanci daga ƙasar.
[While Samuel was still alive, Saul did many things that pleased Yahweh. One of the good things that] Saul [did was to] expel from Israel all the people who were fortune-tellers or who talked to the spirits of dead people. But Samuel had died, and all the Israeli people had mourned for him. Then they had buried him in Ramah, his hometown. [After that, Saul did not try to please Yahweh any more].
4 Filistiyawa suka tattaru suka yi sansani a Shunem. Shawulu ya tattara dukan Isra’ila suka yi sansani a Gilbowa.
The army of Philistia gathered and set up their tents at Shunem [city, in the north of Israel]. Saul gathered the Israeli army and set up their tents at Gilboa [in the eastern part of the same valley].
5 Da Shawulu ya ga sojojin Filistiyawa sai ya ji tsoro, ya firgita ƙwarai.
When Saul saw the army of Philistia, he became so afraid that his heart pounded/shook.
6 Ya nemi nufin Ubangiji amma bai sami amsa daga wurin Ubangiji ko ta wurin mafarki, ko ta wurin Urim, ko ta wurin annabawa ba.
He prayed to Yahweh, but Yahweh did not answer him. Yahweh did not [tell Saul what he should do by] giving him a dream, or by [having the priest throw] the marked stones [that were in his sacred vest], or by [giving a message about Saul to] any prophet.
7 Shawulu ya ce wa fadawansa, “Ku nemo mini wata mace mai duba domin in tafi wurinta in yi tambaya.” Suka ce, “Akwai guda a En Dor.”
Then Saul said to his servants, “Find for me a woman who talks to the spirits of dead people, in order that I can ask her [what will happen].” His servants replied, “There is a woman in Endor [town] who does that.”
8 Sai Shawulu ya sa waɗansu tufafi ya ɓad da kama, shi da waɗansu mutum biyu suka tafi wurin matar da dare, ya ce mata, “Ki yi mini duba ta hanyar sihiri, ki hawar mini duk wanda zan faɗa miki.”
So Saul [took off the clothes that showed that he was the king, and he] put on ordinary clothes (to disguise himself/so that people would not recognize who he was). Then he and two of his men went during the night to talk to that woman. Saul said to her, “I want you to talk to a spirit [of someone who has died]. Cause to appear the person whose name I will [give to you].”
9 Amma matar ta ce masa, “Tabbatacce ka dai san abin da Shawulu ya yi, ya karkashe masu duba da masu maitanci a ƙasar. Me ya sa kake sa mini tarko, don ka sa a kashe ni?”
But the woman replied, “You surely know what Saul has done. He expelled from this land all the people who talk to spirits of dead people and all fortune-tellers. I think that you are trying to trap me, in order that I will be executed [for doing something that is not permitted].”
10 Shawulu ya rantse mata da Ubangiji. Ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a hukunta ki a kan wannan ba.”
Saul replied, solemnly asking Yahweh to listen to what he was saying, “Just as surely as Yahweh lives, you will not be punished for doing this.”
11 Sai matar ta ce, “Wa kake so in hauro maka?” Sai ya ce, “Ki hauro mini da Sama’ila.”
Then the woman said, “Whom do you want me to cause to appear?” Saul replied, “Cause Samuel to appear.”
12 Da matar ta ga Sama’ila sai ta yi ihu da ƙarfi ta ce wa Shawulu, “Me ya sa ka ruɗe ni? Kai ne Shawulu!”
[So] the woman [did that. But] when she saw Samuel, she screamed. She said, “You have tricked me [RHQ]! You are Saul! [You will execute me for doing this]!”
13 Sai sarki ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Me kika gani?” Matar ta ce, “Na ga wani kurwa tana fitowa daga ƙasa.”
Saul said to her, “Do not be afraid. What do you see?” The woman said, “I see a god/spirit coming up out of the ground.”
14 Ya ce, “Yaya kamanninsa yake?” Ta ce, “Wani tsoho sanye da taguwa ne yake haurawa.” Shawulu ya gane cewa Sama’ila ne, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
Saul said, “What does he look like?” The woman replied, “An old man wearing a robe is appearing.” Then Saul knew that it was Samuel. So he bowed down with his face touching the ground.
15 Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Don me ka dame ni, ta wurin hauro da ni?” Shawulu ya ce, “Ina cikin babban damuwa ce, Filistiyawa sun fāɗa mini, Allah kuma ya juya mini baya. Bai amsa mini, ko ta mafarki, ko kuma ta annabawa ba, saboda haka na kira ka don ka gaya mini abin yi.”
Samuel said to Saul, “Why have you bothered/disturbed me by causing me to appear?” Saul said, “I am very worried. The army of Philistia is about to attack my army, and God has abandoned me. He does not answer my questions any more. He does not give me dreams [to tell me what to do] or give messages to prophets [to tell me what to do]. That is the reason that I came to see you. So you tell me what I should do!”
16 Sama’ila ya ce, “Don me kake tambayata bayan Ubangiji ya rabu da kai? Ya zama maƙiyinka?
Samuel said, “Yahweh has abandoned you and has become your enemy. So why do you ask me [what you should do]? [RHQ]
17 Ubangiji ya cika abin da ya yi magana ta wurina. Ubangiji ya fizge mulki daga hannunka, ya ba maƙwabcinka Dawuda.
He has done what he told me [previously] that he would do to you. He has torn the kingdom away from you, and he is giving it to someone who is another Israeli—David.
18 Gama ba ka yi biyayya ga Ubangiji ba, ba ka zartar da hukuncinsa mai zafi a kan Amalekawa ba. Saboda haka Ubangiji ya yi maka haka yau.
You did not obey Yahweh. Yahweh was very angry with the Amalek people-group. You did not [kill all of their animals], with the result that you did not show that he was very angry with them. That is the reason that he has done this to you today.
19 Ubangiji zai ba da Isra’ila da kuma kai ga Filistiyawa, gobe kuwa da kai da’ya’yanka za ku kasance tare da ni. Ubangiji kuma zai ba da sojojin Isra’ila a hannun Filistiyawa.”
Yahweh will enable the Philistia army to defeat you and all the other Israeli soldiers. And tomorrow you and your sons will be with me [in the place where spirits of dead people are]. Yahweh will cause the whole Israeli army to be defeated by the Philistia army.” [And after Samuel said that, he disappeared].
20 Da jin maganar Sama’ila sai Shawulu ya faɗi ƙasa warwas. Tsoro ya kama shi ƙwarai. Ba shi kuma da ƙarfi domin bai ci kome ba dukan yini da kuma dukan dare.
Saul immediately fell flat on the ground. He was so afraid because of what Samuel had said that he became paralyzed. He was also very weak because he had not eaten anything all that day and night.
21 Da matar ta zo wurin Shawulu, ta ga shi a firgice, sai ta ce masa, “Duba baranyarka ta yi maka biyayya ta yi kasai da ranta, ta yi abin da ka ce ta yi.
The woman saw that he was extremely worried/terrified. She said to him, “Listen to me! I have done what you requested me to do. I could be executed for doing that.
22 To, kai ma ka kasa kunne ga baranyarka, zan ba ka abinci ka ci don ka sami ƙarfin tafiya.”
So now please pay attention to what I say. Allow me to give you some food, in order that you will [eat it and] get enough strength to go back [to your army].”
23 Sai ya ƙi. Ya ce, “Ba zan ci abinci ba.” Sai da bayinsa da matar suka roƙe shi, sa’an nan ya ji maganarsu, ya tashi daga ƙasa, ya zauna a bakin gado.
But Saul refused. He said, “No, I will not eat anything.” Then Saul’s servants also urged him [to eat something], and finally he heeded what they said. He got up from the ground and sat on the bed.
24 Matar kuwa tana da maraƙin da take kiwo a gida, sai ta ɗauke shi nan da nan ta yanka. Ta ɗauki garin fulawa ta kwaɓa, ta yi waina marar yisti.
The woman had a fat calf close to her house. She quickly slaughtered it [and cooked it]. She took some flour and mixed it [with olive oil], and baked it without putting in any yeast.
25 Sai ta kawo wa Shawulu da bayinsa suka kuwa ci. A daren nan suka tashi suka tafi.
She placed the food in front of Saul and his servants, and they ate some of it. Then that night they got up and left.

< 1 Sama’ila 28 >