< 1 Sama’ila 28 >
1 Filistiyawa suka tattara sojojinsu domin su yaƙi Isra’ila. Akish ya ce wa Dawuda, “Sai ka sani fa, kai da mutanenka za ku tafi tare da ni da sojojina.”
And it came to pass, in those days, when the Philistines gathered together their hosts for war, to fight with Israel, that Achish said unto David, Thou must, know, that, with me, shalt thou go forth in the host, thou and thy men.
2 Dawuda ya ce, “Kai da kanka za ka ga abin da bawanka zai yi.” Akish ya ce, “Da kyau, zan sa ka zama mai kāre ni.”
And David said unto Achish, Therefore, now, shalt thou know what thy servant can do. And Achish said unto David, Therefore, keeper of my head, will I appoint thee, all the days.
3 Sama’ila dai ya riga ya rasu, dukan Isra’ila suka yi makokinsa suka binne shi a garinsa a Rama. Shawulu kuma ya kori duk masu duba da masu maitanci daga ƙasar.
Now, Samuel, was dead, and all Israel had lamented him, and buried him in Ramah, even in his own city, —Saul, moreover had put away them who had familiar spirits and them who were oracles, out of the land.
4 Filistiyawa suka tattaru suka yi sansani a Shunem. Shawulu ya tattara dukan Isra’ila suka yi sansani a Gilbowa.
So then the Philistines gathered themselves together, and came in, and encamped in Shunem, —and Saul gathered together all Israel, and they encamped in Gilboa.
5 Da Shawulu ya ga sojojin Filistiyawa sai ya ji tsoro, ya firgita ƙwarai.
And, when Saul saw the host of the Philistines, he was afraid, and his heart trembled exceedingly.
6 Ya nemi nufin Ubangiji amma bai sami amsa daga wurin Ubangiji ko ta wurin mafarki, ko ta wurin Urim, ko ta wurin annabawa ba.
Then Saul enquired of Yahweh, but Yahweh answered him not, —neither by Dreams, nor by the Lights, nor by prophets.
7 Shawulu ya ce wa fadawansa, “Ku nemo mini wata mace mai duba domin in tafi wurinta in yi tambaya.” Suka ce, “Akwai guda a En Dor.”
Then said Saul unto his servants—Seek me out a woman that owneth a familiar spirit, that I may even go unto her, and enquire of her. And his servants said unto him, Lo! there is a woman that owneth a familiar spirit in En-dor.
8 Sai Shawulu ya sa waɗansu tufafi ya ɓad da kama, shi da waɗansu mutum biyu suka tafi wurin matar da dare, ya ce mata, “Ki yi mini duba ta hanyar sihiri, ki hawar mini duk wanda zan faɗa miki.”
Saul therefore disguised himself, and put on other raiment, and departed—he and two men with him, and they came to the woman by night, —and he said—Divine for me, I pray thee, by the familiar spirit, and bring up for me—whomsoever I shall name unto thee.
9 Amma matar ta ce masa, “Tabbatacce ka dai san abin da Shawulu ya yi, ya karkashe masu duba da masu maitanci a ƙasar. Me ya sa kake sa mini tarko, don ka sa a kashe ni?”
And the woman said unto him—Lo! thou, knowest what Saul hath done, how he hath cut off them who have familiar spirits and him who is an oracle, out of the land, —wherefore, then, art thou striking at my life, to put me to death?
10 Shawulu ya rantse mata da Ubangiji. Ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a hukunta ki a kan wannan ba.”
So then Saul sware unto her by Yahweh, saying, —By the life of Yahweh, there shall no punishment befall thee for this thing.
11 Sai matar ta ce, “Wa kake so in hauro maka?” Sai ya ce, “Ki hauro mini da Sama’ila.”
Then said the woman, Whom shall I bring up for thee? And he said, Samuel, bring thou up for me.
12 Da matar ta ga Sama’ila sai ta yi ihu da ƙarfi ta ce wa Shawulu, “Me ya sa ka ruɗe ni? Kai ne Shawulu!”
And, when the woman saw Samuel, she made outcry with a loud voice, —and the woman spake unto Saul, saying—Wherefore hast thou deceived me, thou thyself being Saul?
13 Sai sarki ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Me kika gani?” Matar ta ce, “Na ga wani kurwa tana fitowa daga ƙasa.”
And the king said unto her—Be not afraid, but what sawest thou? And the woman said unto Saul, A god, saw I, coming up out of the earth.
14 Ya ce, “Yaya kamanninsa yake?” Ta ce, “Wani tsoho sanye da taguwa ne yake haurawa.” Shawulu ya gane cewa Sama’ila ne, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
And he said to her—What was his form? And she said—An old man, coming up, he being wrapped about with a robe. Then Saul knew, that it was, Samuel, so he inclined his face to the earth, and bowed himself down.
15 Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Don me ka dame ni, ta wurin hauro da ni?” Shawulu ya ce, “Ina cikin babban damuwa ce, Filistiyawa sun fāɗa mini, Allah kuma ya juya mini baya. Bai amsa mini, ko ta mafarki, ko kuma ta annabawa ba, saboda haka na kira ka don ka gaya mini abin yi.”
And Samuel said unto Saul, Wherefore hast thou disquieted me, by bringing me up? And Saul said—I am in sore distress, for, the Philistines, are making war against me, and, God, hath turned away from me, and answereth me no more—either by means of the prophets, or by dreams, therefore have I even called for thee, to let me know, what I am to do.
16 Sama’ila ya ce, “Don me kake tambayata bayan Ubangiji ya rabu da kai? Ya zama maƙiyinka?
Then said Samuel, Wherefore, then, shouldst thou ask me, —when, Yahweh, hath turned away from thee, and hath come to be with thy neighbour?
17 Ubangiji ya cika abin da ya yi magana ta wurina. Ubangiji ya fizge mulki daga hannunka, ya ba maƙwabcinka Dawuda.
Therefore hath Yahweh done for him, as he spake by me, —yea Yahweh hath rent the kingdom out of thy hand, and given it to a neighbour of thine—to David.
18 Gama ba ka yi biyayya ga Ubangiji ba, ba ka zartar da hukuncinsa mai zafi a kan Amalekawa ba. Saboda haka Ubangiji ya yi maka haka yau.
As thou didst not hearken unto the voice of Yahweh, neither didst execute the glow of his anger upon Amalek, therefore, this thing, hath Yahweh done unto thee this day;
19 Ubangiji zai ba da Isra’ila da kuma kai ga Filistiyawa, gobe kuwa da kai da’ya’yanka za ku kasance tare da ni. Ubangiji kuma zai ba da sojojin Isra’ila a hannun Filistiyawa.”
that Yahweh may deliver, Israel also, with thee, into the hand of the Philistines, and, to-morrow, thou and thy sons with thee are about to fall, —the host of Israel also, will Yahweh deliver, into the hand of the Philistines.
20 Da jin maganar Sama’ila sai Shawulu ya faɗi ƙasa warwas. Tsoro ya kama shi ƙwarai. Ba shi kuma da ƙarfi domin bai ci kome ba dukan yini da kuma dukan dare.
Then Saul hastened, and fell prostrate—the whole length of him—to the earth, and was sore afraid, at the words of Samuel, and indeed, no, strength, was left in him, for he had not eaten food all the day and all the night.
21 Da matar ta zo wurin Shawulu, ta ga shi a firgice, sai ta ce masa, “Duba baranyarka ta yi maka biyayya ta yi kasai da ranta, ta yi abin da ka ce ta yi.
And the woman came unto Saul, and, when she saw that he was greatly terrified, she said unto him—Lo! thy handmaid hearkened unto thy voice, and I put my life into my hand, and heard thy words which thou didst speak unto me.
22 To, kai ma ka kasa kunne ga baranyarka, zan ba ka abinci ka ci don ka sami ƙarfin tafiya.”
Now, therefore, I pray thee, hearken, thou also, unto the voice of thy handmaid, and let me set before thee a morsel of food, and eat thou, —that there may be in thee strength, when thou goest on thy journey.
23 Sai ya ƙi. Ya ce, “Ba zan ci abinci ba.” Sai da bayinsa da matar suka roƙe shi, sa’an nan ya ji maganarsu, ya tashi daga ƙasa, ya zauna a bakin gado.
But he refused, and said—I will not eat. But, when his servants, and the woman also, strongly urged him, then hearkened he unto their voice, —and rose up from the earth, and sat on the bed.
24 Matar kuwa tana da maraƙin da take kiwo a gida, sai ta ɗauke shi nan da nan ta yanka. Ta ɗauki garin fulawa ta kwaɓa, ta yi waina marar yisti.
Now, the woman, had a calf fattening, in the shed. So she hastened, and sacrificed it, —and took meal, and kneaded, and baked thereof, unleavened cakes;
25 Sai ta kawo wa Shawulu da bayinsa suka kuwa ci. A daren nan suka tashi suka tafi.
and brought near before Saul and before his servants, and they did eat. Then rose they up and departed, the same night.