< 1 Sama’ila 28 >

1 Filistiyawa suka tattara sojojinsu domin su yaƙi Isra’ila. Akish ya ce wa Dawuda, “Sai ka sani fa, kai da mutanenka za ku tafi tare da ni da sojojina.”
And it came to pass in those days, that the Philistines gathered their camps together for warfare, to fight with Israel; and Achish said unto David, Thou must know that thou shalt go out with me into the camp, thou and thy men.
2 Dawuda ya ce, “Kai da kanka za ka ga abin da bawanka zai yi.” Akish ya ce, “Da kyau, zan sa ka zama mai kāre ni.”
And David said to Achish, By reason of this wilt thou thyself ascertain what thy servant will do. And Achish said to David, Therefore will I make thee the guard of my head for all times.
3 Sama’ila dai ya riga ya rasu, dukan Isra’ila suka yi makokinsa suka binne shi a garinsa a Rama. Shawulu kuma ya kori duk masu duba da masu maitanci daga ƙasar.
Now Samuel was dead, and all Israel had lamented him, and buried him in Ramah, even in his own city; and Saul had removed those that had familiar spirits, and the wizards, out of the land.
4 Filistiyawa suka tattaru suka yi sansani a Shunem. Shawulu ya tattara dukan Isra’ila suka yi sansani a Gilbowa.
And the Philistines assembled themselves together, and came and encamped at Shunem: and Saul assembled together all Israel, and they encamped at Gilboa'.
5 Da Shawulu ya ga sojojin Filistiyawa sai ya ji tsoro, ya firgita ƙwarai.
And when Saul saw the camp of the Philistines, he was afraid, and his heart trembled greatly.
6 Ya nemi nufin Ubangiji amma bai sami amsa daga wurin Ubangiji ko ta wurin mafarki, ko ta wurin Urim, ko ta wurin annabawa ba.
And Saul asked counsel of the Lord; but the Lord answered him not, either by means of dreams, or by means of the Urim, or by means of the prophets.
7 Shawulu ya ce wa fadawansa, “Ku nemo mini wata mace mai duba domin in tafi wurinta in yi tambaya.” Suka ce, “Akwai guda a En Dor.”
Then said Saul unto his servants, Seek out for me a woman that hath a familiar spirit, that I may go to her and inquire of her. And his servants said to him, Behold, there is a woman that hath a familiar spirit at 'En-dor.
8 Sai Shawulu ya sa waɗansu tufafi ya ɓad da kama, shi da waɗansu mutum biyu suka tafi wurin matar da dare, ya ce mata, “Ki yi mini duba ta hanyar sihiri, ki hawar mini duk wanda zan faɗa miki.”
And Saul disguised himself, and put on other garments, and he went, he and two men with him, and they came to the woman by night: and he said, Divine, I pray thee, unto me by the familiar spirit, and bring up for me the one whom I shall say unto thee.
9 Amma matar ta ce masa, “Tabbatacce ka dai san abin da Shawulu ya yi, ya karkashe masu duba da masu maitanci a ƙasar. Me ya sa kake sa mini tarko, don ka sa a kashe ni?”
And the woman said unto him, Behold, thou well knowest that which Saul hath done, that he hath cut off those that have familiar spirits, and the wizards, out of the land; wherefore then layest thou a snare for my life, to cause me to die?
10 Shawulu ya rantse mata da Ubangiji. Ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a hukunta ki a kan wannan ba.”
And Saul swore to her by the Lord, saying, As the Lord liveth, there shall no guilt attach to thee for this thing.
11 Sai matar ta ce, “Wa kake so in hauro maka?” Sai ya ce, “Ki hauro mini da Sama’ila.”
Then said the woman, Whom shall I bring up for thee? And he said, Samuel thou must bring up for me.
12 Da matar ta ga Sama’ila sai ta yi ihu da ƙarfi ta ce wa Shawulu, “Me ya sa ka ruɗe ni? Kai ne Shawulu!”
And when the woman saw Samuel, she cried with a loud voice: and the woman said to Saul thus, Why hast thou deceived me? since thou art Saul.
13 Sai sarki ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Me kika gani?” Matar ta ce, “Na ga wani kurwa tana fitowa daga ƙasa.”
And the king said unto her, Be not afraid; however, what hast thou seen? And the woman said unto Saul, A divine being have I seen ascending out of the earth.
14 Ya ce, “Yaya kamanninsa yake?” Ta ce, “Wani tsoho sanye da taguwa ne yake haurawa.” Shawulu ya gane cewa Sama’ila ne, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
And he said unto her, What is his form? And she said, An old man is coming up; and he is wrapt in a mantle. And so Saul perceived that it was Samuel, and he bowed with his face to the ground, and prostrated himself.
15 Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Don me ka dame ni, ta wurin hauro da ni?” Shawulu ya ce, “Ina cikin babban damuwa ce, Filistiyawa sun fāɗa mini, Allah kuma ya juya mini baya. Bai amsa mini, ko ta mafarki, ko kuma ta annabawa ba, saboda haka na kira ka don ka gaya mini abin yi.”
And Samuel said to Saul, Why hast thou disquieted me, to bring me up? And Saul answered, I am greatly distressed, and the Philistines make war against me, and God is departed from me, and hath not answered me any more, either by the agency of the prophets, or by means of dreams; wherefore I have called thee, to make known unto me what I shall do.
16 Sama’ila ya ce, “Don me kake tambayata bayan Ubangiji ya rabu da kai? Ya zama maƙiyinka?
Then said Samuel, And why wilt thou ask me, seeing the Lord is departed from thee, and is become thy enemy?
17 Ubangiji ya cika abin da ya yi magana ta wurina. Ubangiji ya fizge mulki daga hannunka, ya ba maƙwabcinka Dawuda.
And the Lord hath done for himself as he hath spoken through my agency; and the Lord hath rent the government out of thy hand, and hath given it to thy associate, to David;
18 Gama ba ka yi biyayya ga Ubangiji ba, ba ka zartar da hukuncinsa mai zafi a kan Amalekawa ba. Saboda haka Ubangiji ya yi maka haka yau.
As thou didst not obey the voice of the Lord, and didst not execute his fierce wrath upon 'Amalek; therefore hath the Lord done this thing unto thee this day.
19 Ubangiji zai ba da Isra’ila da kuma kai ga Filistiyawa, gobe kuwa da kai da’ya’yanka za ku kasance tare da ni. Ubangiji kuma zai ba da sojojin Isra’ila a hannun Filistiyawa.”
And the Lord will deliver also Israel with thee into the hand of the Philistines; and tomorrow shalt thou and thy sons be with me: also the camp of Israel will the Lord deliver into the hand of the Philistines.
20 Da jin maganar Sama’ila sai Shawulu ya faɗi ƙasa warwas. Tsoro ya kama shi ƙwarai. Ba shi kuma da ƙarfi domin bai ci kome ba dukan yini da kuma dukan dare.
Then fell Saul hastily with his full length to the earth, and was greatly afraid, because of the words of Samuel: there was also no strength in him; for he had not eaten any food all that day, and all that night.
21 Da matar ta zo wurin Shawulu, ta ga shi a firgice, sai ta ce masa, “Duba baranyarka ta yi maka biyayya ta yi kasai da ranta, ta yi abin da ka ce ta yi.
And the woman came unto Saul, and saw that he was greatly terrified; and she said unto him, Behold, thy hand-maid hath obeyed thy voice; and I put my life in my hand, and hearkened unto thy words which thou spokest unto me.
22 To, kai ma ka kasa kunne ga baranyarka, zan ba ka abinci ka ci don ka sami ƙarfin tafiya.”
And now, hearken thou also, I pray thee, unto the voice of thy hand-maid, and let me set before thee a morsel of bread, and eat; that thou mayest have strength when thou goest on the way.
23 Sai ya ƙi. Ya ce, “Ba zan ci abinci ba.” Sai da bayinsa da matar suka roƙe shi, sa’an nan ya ji maganarsu, ya tashi daga ƙasa, ya zauna a bakin gado.
But he refused, and said, I will not eat. But his servants urged him much, as also the woman; and he hearkened unto their voice. So he arose from the earth, and sat upon the bed.
24 Matar kuwa tana da maraƙin da take kiwo a gida, sai ta ɗauke shi nan da nan ta yanka. Ta ɗauki garin fulawa ta kwaɓa, ta yi waina marar yisti.
And the woman had a fatted calf in the house; and she hastened, and slaughtered it, and took flour, and kneaded it, and baked unleavened bread thereof:
25 Sai ta kawo wa Shawulu da bayinsa suka kuwa ci. A daren nan suka tashi suka tafi.
And she brought it near before Saul, and before his servants; and they ate. Then they rose up, and went away that night.

< 1 Sama’ila 28 >