< 1 Sama’ila 28 >

1 Filistiyawa suka tattara sojojinsu domin su yaƙi Isra’ila. Akish ya ce wa Dawuda, “Sai ka sani fa, kai da mutanenka za ku tafi tare da ni da sojojina.”
And it came to pass in those days, that the Philistines gathered together their armies to be prepared for war against Israel: and Achis said to David: Know thou now assuredly, that thou shalt go out with me to the war, thou, and thy men.
2 Dawuda ya ce, “Kai da kanka za ka ga abin da bawanka zai yi.” Akish ya ce, “Da kyau, zan sa ka zama mai kāre ni.”
And David said to Achis: Now thou shalt know what thy servant will do. And Achis said to David: And I will appoint thee to guard my life for ever.
3 Sama’ila dai ya riga ya rasu, dukan Isra’ila suka yi makokinsa suka binne shi a garinsa a Rama. Shawulu kuma ya kori duk masu duba da masu maitanci daga ƙasar.
Now Samuel was dead, and all Israel mourned for him, and buried him in Ramatha his city. And Saul had put away all the magicians and soothsayers out of the land.
4 Filistiyawa suka tattaru suka yi sansani a Shunem. Shawulu ya tattara dukan Isra’ila suka yi sansani a Gilbowa.
And the Philistines were gathered together, and came and camped in Sunam: and Saul also gathered together all Israel, and came to Gelboe.
5 Da Shawulu ya ga sojojin Filistiyawa sai ya ji tsoro, ya firgita ƙwarai.
And Saul saw the army of the Plilistines, and was afraid, and his heart was very much dismayed.
6 Ya nemi nufin Ubangiji amma bai sami amsa daga wurin Ubangiji ko ta wurin mafarki, ko ta wurin Urim, ko ta wurin annabawa ba.
And he consulted the Lord, and he answered him not, neither by dreams, nor by priests, nor by prophets.
7 Shawulu ya ce wa fadawansa, “Ku nemo mini wata mace mai duba domin in tafi wurinta in yi tambaya.” Suka ce, “Akwai guda a En Dor.”
And Saul said to his servants: Seek me a woman that hath a divining spirit, and I will go to her, and inquire by her. And his servants said to him: There is a woman that hath a divining spirit at Endor.
8 Sai Shawulu ya sa waɗansu tufafi ya ɓad da kama, shi da waɗansu mutum biyu suka tafi wurin matar da dare, ya ce mata, “Ki yi mini duba ta hanyar sihiri, ki hawar mini duk wanda zan faɗa miki.”
Then he disguised himself: and put on other clothes, and he went, and two men with him, and they came to the woman by night, and he said to her: Divine to me by thy divining spirit, and bring me up him whom I shall tell thee.
9 Amma matar ta ce masa, “Tabbatacce ka dai san abin da Shawulu ya yi, ya karkashe masu duba da masu maitanci a ƙasar. Me ya sa kake sa mini tarko, don ka sa a kashe ni?”
And the woman said to him: Behold thou knowest all that Saul hath done, and how he hath rooted out the magicians and soothsayers from the land: why then dost thou lay a snare for my life, to cause me to be put to death?
10 Shawulu ya rantse mata da Ubangiji. Ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a hukunta ki a kan wannan ba.”
And Saul swore unto her by the Lord, saying: As the Lord liveth there shall no evil happen to thee for this thing.
11 Sai matar ta ce, “Wa kake so in hauro maka?” Sai ya ce, “Ki hauro mini da Sama’ila.”
And the woman said to him: Whom shall I bring up to thee? And he said, Bring me up Samuel.
12 Da matar ta ga Sama’ila sai ta yi ihu da ƙarfi ta ce wa Shawulu, “Me ya sa ka ruɗe ni? Kai ne Shawulu!”
And when the woman saw Samuel, she cried out with a loud voice, and said to Saul: Why hast thou deceived me? for thou art Saul.
13 Sai sarki ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Me kika gani?” Matar ta ce, “Na ga wani kurwa tana fitowa daga ƙasa.”
And the king said to her: Fear not: what hast thou seen? And the woman said to Saul: I saw gods ascending out of the earth.
14 Ya ce, “Yaya kamanninsa yake?” Ta ce, “Wani tsoho sanye da taguwa ne yake haurawa.” Shawulu ya gane cewa Sama’ila ne, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
And he said to her: What form is he of? And she said: An old man cometh up, and he is covered with a mantle. And Saul understood that it was Samuel, and he bowed himself with his face to the ground, and adored.
15 Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Don me ka dame ni, ta wurin hauro da ni?” Shawulu ya ce, “Ina cikin babban damuwa ce, Filistiyawa sun fāɗa mini, Allah kuma ya juya mini baya. Bai amsa mini, ko ta mafarki, ko kuma ta annabawa ba, saboda haka na kira ka don ka gaya mini abin yi.”
And Samuel said to Saul: Why hast thou disturbed my rest, that I should be brought up? And Saul said, I am in great distress: for the Philistines fight against me, and God is departed from me, and would not hear me, neither by the hand of prophets, nor by dreams: therefore I have called thee, that thou mayest shew me what I shall do.
16 Sama’ila ya ce, “Don me kake tambayata bayan Ubangiji ya rabu da kai? Ya zama maƙiyinka?
And Samuel said: Why askest thou me, seeing the Lord has departed from thee, and is gone over to thy rival:
17 Ubangiji ya cika abin da ya yi magana ta wurina. Ubangiji ya fizge mulki daga hannunka, ya ba maƙwabcinka Dawuda.
For the Lord will do to thee as he spoke by me, and he will rend thy kingdom out of thy hand, and will give it to thy neighbour David:
18 Gama ba ka yi biyayya ga Ubangiji ba, ba ka zartar da hukuncinsa mai zafi a kan Amalekawa ba. Saboda haka Ubangiji ya yi maka haka yau.
Because thou didst not obey the voice of the Lord, neither didst thou execute the wrath of his indignation upon Amalec. Therefore hath the Lord done to thee what thou sufferest this day.
19 Ubangiji zai ba da Isra’ila da kuma kai ga Filistiyawa, gobe kuwa da kai da’ya’yanka za ku kasance tare da ni. Ubangiji kuma zai ba da sojojin Isra’ila a hannun Filistiyawa.”
And the Lord also will deliver Israel with thee into the hands of the Philistines: and tomorrow thou and thy sons shall be with me: and the Lord will also deliver the army of Israel into the hands of the Philistines.
20 Da jin maganar Sama’ila sai Shawulu ya faɗi ƙasa warwas. Tsoro ya kama shi ƙwarai. Ba shi kuma da ƙarfi domin bai ci kome ba dukan yini da kuma dukan dare.
And forthwith Saul fell all along on the ground, for he was frightened with the words of Samuel, and there was no strength in him, for he had eaten no bread all that day.
21 Da matar ta zo wurin Shawulu, ta ga shi a firgice, sai ta ce masa, “Duba baranyarka ta yi maka biyayya ta yi kasai da ranta, ta yi abin da ka ce ta yi.
And the woman came to Saul (for he was very much troubled) and said to him: Behold thy handmaid hath obeyed thy voice, and I have put my life in my hand: and I hearkened unto the words which thou spokest to me.
22 To, kai ma ka kasa kunne ga baranyarka, zan ba ka abinci ka ci don ka sami ƙarfin tafiya.”
Now therefore hear thou also the voice of thy handmaid, and let me set before thee a morsel of bread, that thou mayest eat and recover strength, and be able to go on thy journey.
23 Sai ya ƙi. Ya ce, “Ba zan ci abinci ba.” Sai da bayinsa da matar suka roƙe shi, sa’an nan ya ji maganarsu, ya tashi daga ƙasa, ya zauna a bakin gado.
But he refused, and said: I will not eat. But his servants and the woman forced him, and at length hearkening to their voice, he arose from the ground and sat upon the bed.
24 Matar kuwa tana da maraƙin da take kiwo a gida, sai ta ɗauke shi nan da nan ta yanka. Ta ɗauki garin fulawa ta kwaɓa, ta yi waina marar yisti.
Now the woman had a fatted calf in the house, and she made haste and killed it: and taking meal kneaded it, and baked some unleavened bread,
25 Sai ta kawo wa Shawulu da bayinsa suka kuwa ci. A daren nan suka tashi suka tafi.
And set it before Saul, and before his servants. And when they had eaten they rose up, and walked all that night.

< 1 Sama’ila 28 >