< 1 Sama’ila 28 >

1 Filistiyawa suka tattara sojojinsu domin su yaƙi Isra’ila. Akish ya ce wa Dawuda, “Sai ka sani fa, kai da mutanenka za ku tafi tare da ni da sojojina.”
Fa: no, eso enoga Filisidini dunu ilia da Isala: ili fi ilima gegemusa: , dadi gagui dunu gilisi. Amola A: igise da Da: ibidima amane sia: i, “Dafawane! Di amola dia dunu da namagale Isala: ili dunuma gegemu.”
2 Dawuda ya ce, “Kai da kanka za ka ga abin da bawanka zai yi.” Akish ya ce, “Da kyau, zan sa ka zama mai kāre ni.”
Da: ibidi da amane sia: i, “Ma! Dafawane! Na da dia hawa: hamosu dunu. Amola di da na hamobe di siga disu ba: mu.” A: igise da amane sia: i, “Defea! Na da di na da: i gaga: su dunu hamomu.”
3 Sama’ila dai ya riga ya rasu, dukan Isra’ila suka yi makokinsa suka binne shi a garinsa a Rama. Shawulu kuma ya kori duk masu duba da masu maitanci daga ƙasar.
Sa: miuele da bogoi dagoi amola Isala: ili dunu ilia bogoi didigia: lalu amola hina: moilaidafa La: ima amoga uli dogoi. Solo da wadela: i ba: la: lusu dunu, gesami dasu amola bosa: ga: su uda amola dunu amo Isala: ili sogega sefasi dagoi ba: i.
4 Filistiyawa suka tattaru suka yi sansani a Shunem. Shawulu ya tattara dukan Isra’ila suka yi sansani a Gilbowa.
Filisidini dadi gagui dunu da mogodigili asili amola Siouneme moilai gadenene wa: i fi esalu. Solo da Isala: ili dadi gagui dunu gilisili, Giliboua Goumia awalia wa: i fi esalu.
5 Da Shawulu ya ga sojojin Filistiyawa sai ya ji tsoro, ya firgita ƙwarai.
Solo da Filisidini dadi gagui gilisibi ba: loba, e da baligili beda: i galu.
6 Ya nemi nufin Ubangiji amma bai sami amsa daga wurin Ubangiji ko ta wurin mafarki, ko ta wurin Urim, ko ta wurin annabawa ba.
Amaiba: le, e da Hina Godema adi hamoma: bela: le adole ba: i. Be Hina Gode da ema golaia ba: su amola Iulimi amola Damimi amoga amola balofede dunu ilia sia: amoga dabe hame adole i.
7 Shawulu ya ce wa fadawansa, “Ku nemo mini wata mace mai duba domin in tafi wurinta in yi tambaya.” Suka ce, “Akwai guda a En Dor.”
Amalalu, Solo da ea eagene ouligisu dunuma amane sia: i, “Bosa: ga: su uda afae nagili hogolesima. Amalalu na da ema adole ba: la masunu.” Ilia da ema amane adole i, “Bosa: ga: su uda da Enedo moilaiga esala.”
8 Sai Shawulu ya sa waɗansu tufafi ya ɓad da kama, shi da waɗansu mutum biyu suka tafi wurin matar da dare, ya ce mata, “Ki yi mini duba ta hanyar sihiri, ki hawar mini duk wanda zan faɗa miki.”
Amaiba: le, Solo da enoga e dawa: digisa: besa: le, hina: da: i afadenei. E abula eno salawane, gasibi galu e amola dunu aduna eno, amo uda ba: la asi. E amo udama amane sia: i, “Bogoi a: silibuma adole ba: lalu, hobea misunu hou nama olelema. Dunu ea dio na sia: mu, amo ea a: silibu misa: ne sia: ma.”
9 Amma matar ta ce masa, “Tabbatacce ka dai san abin da Shawulu ya yi, ya karkashe masu duba da masu maitanci a ƙasar. Me ya sa kake sa mini tarko, don ka sa a kashe ni?”
Bosa: ga: su uda da Soloma bu adole i, “Dia da abuliba: le na bogosu logo fodosala: ? Di da hina bagade Solo ea hamobe hame dawa: sala: ? E da ba: la: lusu dunu amola bosa: ga: su dunu amola uda huluane Isala: ili sogega sefasi dagoi.”
10 Shawulu ya rantse mata da Ubangiji. Ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a hukunta ki a kan wannan ba.”
Amalalu, Solo da dafawanedafa sia: amane ilegei, “Esalebe Hina Gode amo Ea Dioba: le, di da amo hou hamosea, se iasu hamedafa ba: mu, amo na da ilegesa.”
11 Sai matar ta ce, “Wa kake so in hauro maka?” Sai ya ce, “Ki hauro mini da Sama’ila.”
Uda da bu adole ba: i, “Na da di ba: ma: ne, nowa bogoi dunu amo misa: ne sia: ma: bela: ?” Solo da adole i, “Sa: miuele!”
12 Da matar ta ga Sama’ila sai ta yi ihu da ƙarfi ta ce wa Shawulu, “Me ya sa ka ruɗe ni? Kai ne Shawulu!”
Be uda da Sa: miuele manebe ba: beba: le, a:a: ia gusa: nu, Soloma amane sia: i, “Di da abuliba: le nama ogogobela: ? Di da hina bagade Solofa galu galebe!”
13 Sai sarki ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Me kika gani?” Matar ta ce, “Na ga wani kurwa tana fitowa daga ƙasa.”
Hina bagade Solo da ema amane sia: i, “Mae beda: ma! Di da adi ba: sala: ?” Uda da bu adole i, “Na da a: silibu osoba gudunini heda: lebe ba: sa!”
14 Ya ce, “Yaya kamanninsa yake?” Ta ce, “Wani tsoho sanye da taguwa ne yake haurawa.” Shawulu ya gane cewa Sama’ila ne, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
E bu adole ba: i, “Amo da adi agoane ba: sala: ?” Uda da amane sia: i, “Amo da dunu da: i hamoi agoai heda: lebe.” “E da abula amoga idinigi galebe.” Amalalu, Solo da amo bogoi a: silibu da Sa: miuele galebeya dawa: digi. Amola e da ema nodomusa: , osoba begudui.
15 Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Don me ka dame ni, ta wurin hauro da ni?” Shawulu ya ce, “Ina cikin babban damuwa ce, Filistiyawa sun fāɗa mini, Allah kuma ya juya mini baya. Bai amsa mini, ko ta mafarki, ko kuma ta annabawa ba, saboda haka na kira ka don ka gaya mini abin yi.”
Sa: miuele da Soloma amane sia: i, “Dia da abuliba: le na didilisibala: ? Dia da abuliba: le na buhagima: ne hamobela: ?” Solo da bu adole i, “Bidi hamosu bagade da nama doaga: i dagoi. Filisidini dunu da nama gegenana amola Gode da na yolesi dagoi. E da nama golaia amola balofede dunumadi na adole ba: su amo nama dabe hame adole iaha. Amaiba: le, na da dima wele sia: na misi. Di da nama, na hamomu liligi olelema!”
16 Sama’ila ya ce, “Don me kake tambayata bayan Ubangiji ya rabu da kai? Ya zama maƙiyinka?
Sa: miuele da amane sia: i, “Hina Gode da di yolesili, bu dimawane ha lai dagoi. Amaiba: le, di da abuliba: le na misa: ne wele sia: bela: ?
17 Ubangiji ya cika abin da ya yi magana ta wurina. Ubangiji ya fizge mulki daga hannunka, ya ba maƙwabcinka Dawuda.
Hina Gode da na lafidili dima olelei liligi amo hamoi dagoi. E da dia hina bagade hou amo dima fadegale, Da: ibidima i dagoi.
18 Gama ba ka yi biyayya ga Ubangiji ba, ba ka zartar da hukuncinsa mai zafi a kan Amalekawa ba. Saboda haka Ubangiji ya yi maka haka yau.
Di da Hina Gode Ea sia: i amo mae nabawane, A:malege dunu amola ilia liligi huluane wadela: ma: nedafa hame hamoi. Hina Gode Ea wali dima hamobe amo ea bai da goea.
19 Ubangiji zai ba da Isra’ila da kuma kai ga Filistiyawa, gobe kuwa da kai da’ya’yanka za ku kasance tare da ni. Ubangiji kuma zai ba da sojojin Isra’ila a hannun Filistiyawa.”
E da di amola Isala: ili fi amo ali Filisidini dunu ilia lobo da: iya imunu. Aya eso, di amola diagofelali da nama gilisimu. Amola Hina Gode da Isala: ili dadi gagui wa: i amo Filisidini dunu ilia lobo da: iya imunu.”
20 Da jin maganar Sama’ila sai Shawulu ya faɗi ƙasa warwas. Tsoro ya kama shi ƙwarai. Ba shi kuma da ƙarfi domin bai ci kome ba dukan yini da kuma dukan dare.
Amogalu, hedolowane Solo da osoba gala: la sa: ili, mogosusuli dialebe ba: i. E da Sa: miuele ea sia: beba: le baligili beda: i galu. E da amo esoha amola gasia ha: i hame maiba: le, gasa hame ba: i.
21 Da matar ta zo wurin Shawulu, ta ga shi a firgice, sai ta ce masa, “Duba baranyarka ta yi maka biyayya ta yi kasai da ranta, ta yi abin da ka ce ta yi.
Uda da ema asili, e da baligili beda: i amo ba: beba: le, e amane sia: i, “Dafawane, Hina! Na da dia adole ba: i amo hamobeba: le, na esalusu gadenenewane udidimu agoai ba: i.
22 To, kai ma ka kasa kunne ga baranyarka, zan ba ka abinci ka ci don ka sami ƙarfin tafiya.”
Dafawane, wali na dima adoleba: be amo dia hamoma. Na da digili ha: i manu hamoma: ne sia: ma. Di da bu gasa lama: ne, ha: i manu da defea.”
23 Sai ya ƙi. Ya ce, “Ba zan ci abinci ba.” Sai da bayinsa da matar suka roƙe shi, sa’an nan ya ji maganarsu, ya tashi daga ƙasa, ya zauna a bakin gado.
Solo da ha: i hame manu sia: i. Be ea eagene ouligisu dunu da e ha: i moma: ne logei. E da ouesalu, amalalu ilia sia: nababeba: le, osoba dialu wa: legadole, dia heda: su fafai amoga fila heda: i.
24 Matar kuwa tana da maraƙin da take kiwo a gida, sai ta ɗauke shi nan da nan ta yanka. Ta ɗauki garin fulawa ta kwaɓa, ta yi waina marar yisti.
Uda da hedolowane bulamagau mano (amo da sefe fima: ne, e da diasu ganodini ha: i manu iasu) amo fane legei. E da agi lale, hahamonanu, yisidi mae salawane gobei.
25 Sai ta kawo wa Shawulu da bayinsa suka kuwa ci. A daren nan suka tashi suka tafi.
E da amo ha: i manu Solo amola ea ouligisu dunu ilia moma: ne, ilia midadi ligisi. Amalu, ilia da amo mai. Amola ilia amo gasia yolesili asi.

< 1 Sama’ila 28 >