< 1 Sama’ila 26 >
1 Zifawa suka je wurin Shawulu a Gibeya suka ce, “Ashe, ba Dawuda ne ya ɓuya a tudun Hakila da yake fuskantar Yeshimon ba?”
Och de af Siph kommo till Saul i Gibea, och sade: Är icke David fördold på berget Hachila, inför öknene?
2 Sai Shawulu ya tashi ya gangara zuwa Jejin Zif, tare da zaɓaɓɓun mutane dubu uku na Isra’ila. Suka fita neman Dawuda a can.
Då stod Saul upp, och drog ned till den öknen Siph; och med honom tretusend unge män af Israel; på det han skulle uppsöka David i öknene Siph.
3 Shawulu ya yi sansani a bakin hanyar zuwa tudun Hakila mai fuskantar Yeshimon. Amma Dawuda yana zaune a jeji. Sa’ad da ya ga Shawulu ya biyo shi har zuwa can,
Och lägrade sig på det berget Hachila, som ligger inför öknene vid vägen; men David blef i öknene. Och då han såg, att Saul kom efter honom i öknena,
4 sai ya aiki’yan leƙen asiri su tabbata lalle Shawulu ya iso can.
Sände han spejare ut, och förfor att Saul visserliga kommen var.
5 Sai Dawuda ya kintsa ya tafi inda Shawulu ya yi sansani. Ya ga inda Shawulu da Abner ɗan Ner shugaban ƙungiyar soja suka kwanta. Shawulu yana kwance a cikin sansani tare da sojoji kewaye da shi.
Och David stod upp, och kom till det rummet, der Saul höll sitt lägre; och han såg rummet, der Saul låg med sin härhöfvitsman, Abner, Ners son; ty Saul låg i vagnborgene, och härfolket omkring honom.
6 Sai Dawuda ya ce wa Ahimelek mutumin Hitti da Abishai ɗan Zeruhiya ɗan’uwan Yowab, “Wa zai gangara tare da ni zuwa sansanin Shawulu?” Sai Abishai ya ce, “Zan tafi tare da kai.”
Då svarade David, och sade till Ahimelech den Hetheen, och till Abisai, ZeruJa son, Joabs broder: Ho vill med mig neder till Saul i lägret? Abisai sade: Jag vill ned med dig.
7 Saboda haka Dawuda da Abishai suka gangara zuwa wurin rundunar da dare, sai ga Shawulu kwance yana barci a cikin sansani da māshinsa a kafe a ƙasa kusa da kansa. Abner kuwa tare da sojoji suna kwance kewaye da shi.
Så kom David och Abisai till folket om nattena, och si, Saul låg och sof i vagnborgene, och hans spjut stött i jordena, vid hans hufvud; men Abner och folket låg omkring honom.
8 Abishai ya ce wa Dawuda, “Yau Allah ya ba da maƙiyinka a hannunka. Bari in kafe shi da ƙasa da māshina, zan soke shi da māshi sau ɗaya tak, ba na bukata in soke shi sau biyu.”
Då sade Abisai till David: Gud hafver i denna dag beslutit din fienda i dina hand; så vill jag nu en gång med spjutet stinga honom igenom i jordena, så att han skall icke mer behöfva.
9 Amma Dawuda ya ce wa Abishai, “Kada ka hallaka shi. Wa zai sa hannu a kan shafaffe na Ubangiji, har yă tsira?
Men David sade till Abisai: Förderfva honom intet; ty ho vill komma sina hand vid Herrans smorda, och blifva oskyldig?
10 Muddin Ubangiji yana a raye, Ubangiji da kansa zai buge shi, ko yă mutu a lokacinsa, ko kuma yă mutu a wurin yaƙi.
Ytterligare sade David: Så visst som Herren lefver, om Herren icke slår honom, eller hans tid kommer, att han dör, eller han drager i en strid, och så blifver borta,
11 Amma Allah yă sawwaƙa in sa hannu a shafaffen Ubangiji, ka ɗauki māshin da butar ruwan da take kusa da kansa mu tafi.”
Så låte Herren det vara långt ifrå mig, att jag skall komma mina hand vid Herrans smorda; så tag nu spjutet vid hans hufvud, och vattubägaren, och låt oss gå.
12 Saboda haka Dawuda ya ɗauki māshin da butar ruwan da take kusa da Shawulu suka tafi. Ba wanda ya gan su, ba wanda ya san abin da ya faru, ba kuwa wanda ya farka, dukansu suna barci gama Ubangiji ya sa barci mai nauyi ya ɗauke su.
Så tog David spjutet och vattubägaren vid Sauls hufvud, och gingo sina färde; och ingen var, som det såg eller märkte, eller vaknade, utan de sofvo alle; ty en tung sömn var fallen på dem af Herranom.
13 Sa’an nan Dawuda ya haye zuwa wancan gefen kwarin, ya hau kan wani tudu mai ɗan nisa inda Shawulu tare da mutanensa suke. Akwai babban fili tsakaninsu.
Då nu David var kommen öfver på hinsidon, gick han upp på bergskullan långt ifrå, så att der var stort rum emellan dem;
14 Sai Dawuda ya kira sojojin Shawulu da kuma Abner ɗan Ner ya ce, “Abner ba za ka amsa mini ba?” Abner ya ce, “Wane ne yake kira yana damun sarki haka?”
Och ropade till folket och till Abner, Ners son, och sade: Hörer du icke, Abner? Och Abner svarade, och sade: Ho äst du, att du så ropar Konungen?
15 Dawuda ya ce wa Abner, “Wane irin mutum ne kai? Ba kai ne soja mafi iya yaƙi a Isra’ila ba? Don me ba ka yi gadin ranka yă daɗe, sarki da kyau ba? Ɗazu wani ya shiga tsakiyarku don yă kashe ranka yă daɗe, sarki.
Och David sade till Abner: Äst du icke en man? Och ho är din like i Israel? Hvi hafver du då icke bevarat din herra Konungen? Ty en af folket är der ingången, till att slå din herra Konungen ihjäl.
16 Abin da ka yi bai yi kyau ba. Muddin Ubangiji yana a raye kai da mutanenka kun cancanci mutuwa, domin ba ku lura da maigidanku shafaffe na Ubangiji ba. Ka duba kewaye da kai, ina māshi da kuma butar ruwan da suke kusa da kansa?”
Det är icke redeligit, som du gjort hafver; så visst som Herren lefver, I ären dödsens barn, att I edar herra, Herrans smorda, icke bevarat hafven; nu se, här är Konungens spjut och vattubägaren, som stodo vid hans hufvud.
17 Shawulu ya gane muryar Dawuda, sai ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Dawuda ya ce, “I, muryata ce ya ranka yă daɗe, sarki.”
Då kände Saul Davids röst, och sade: Är det icke din röst, min son David? David sade: Det är min röst, min herre Konung.
18 Ya ƙara da cewa, “Don me ranka yă daɗe, yake fafarata? Mene ne na yi? Wane abu ne aka same ni da laifi a kai?
Och sade ytterligare: Hvi förföljer min herre så sin tjenare? Hvad hafver jag gjort? Och hvad ondt är i mine hand?
19 To, bari ranka yă daɗe, sarkina yă kasa kunne yă ji abin da zan faɗa. Idan Ubangiji ne ya sa ka yi fushi da ni, bari yă karɓi hadaya ta hatsi. Amma idan mutane ne suka sa ka, bari a la’anta su, Ubangiji ne shaidata. Gama sun kore ni don kada in sami rabo cikin gādon Ubangiji, suna cewa, ‘Ka je ka bauta wa waɗansu alloli.’
Så höre dock nu min herre Konungen sin tjenares ord: Om Herren uppretar dig emot mig, så låte man ett spisoffer lukta; men om menniskors barn göra det, så vare de förbannade för Herranom, att de på denna dag hafva fördrifvit mig, att jag icke må blifva i Herrans arfvedel, och säga: Gack bort, och tjena andra gudar.
20 Kada ka yarda jinina yă zuba a ƙasa nesa da gaban Ubangiji. Sarkin Isra’ila ya fito yă nemi kuɗin cizo kamar mai farautar kazan duwatsu.”
Så förfalle nu icke mitt blod på jordena för Herrans ansigte; ty Israels Konung är utdragen till att söka ena loppo, såsom man jagar ett rapphöns på bergen.
21 Sai Shawulu ya ce, “Na yi zunubi ka dawo Dawuda ɗana. Ba zan yi maka kome ba, domin ka darajarta raina yau. Lalle na yi wawanci! Na yi babban kuskure.”
Och Saul sade: Jag hafver syndat. Kom igen, min son David, jag vill intet ondt mer göra dig, derföre att min själ hafver i denna dag dyr varit för din ögon; si, jag hafver gjorts dårliga och ganska ovisliga.
22 Dawuda ya ce, “Ga māshin sarki, ka aiko wani saurayi yă zo yă karɓa.
David svarade, och sade: Si, här är Konungens spjut; en af de unga män gånge hitupp, och tage det.
23 Ubangiji yakan sāka wa kowa bisa ga adalcinsa da amincinsa. Ubangiji ya bashe ka a hannuna yau, amma ba zan sa hannuna a kan shafaffe na Ubangiji ba.
Herren varder väl hvarjom och enom vedergällandes efter hans rättfärdighet och tro; ty Herren hade i dag gifvit dig i mina hand; men jag ville icke komma mina hand vid Herrans smorda.
24 Kamar yadda na ga darajar ranka yau. Haka ma bari Ubangiji yă ga darajar raina, yă cece ni daga dukan wahala.”
Och såsom din själ hafver i denna dagen för min ögon mycket aktad varit, så varde ock min själ mycket aktad för Herrans ögon, och hjelpe mig utur all bedröfvelse.
25 Sai Shawulu ya ce wa Dawuda, “Allah yă albarkace ka ɗana, Dawuda, za ka yi manyan abubuwa, tabbatacce kuma ka yi nasara.” Sai Dawuda ya yi tafiyarsa, Shawulu kuwa ya koma gida.
Saul sade till David: Välsignad vare du, min son David; du skall görat, och gåt igenom. Så gick David sin väg; och Saul vände om hem igen.