< 1 Sama’ila 26 >

1 Zifawa suka je wurin Shawulu a Gibeya suka ce, “Ashe, ba Dawuda ne ya ɓuya a tudun Hakila da yake fuskantar Yeshimon ba?”
Jo-Zif nodhi Gibea ir Saulo ma giwachone niya, “Donge Daudi opondo ewi got Hakila momanyore gi Jeshimon?”
2 Sai Shawulu ya tashi ya gangara zuwa Jejin Zif, tare da zaɓaɓɓun mutane dubu uku na Isra’ila. Suka fita neman Dawuda a can.
Eka Saulo nodhi mwalo e piny motimo ongoro e Zif, nodhi gi joge alufu adek, jo-Israel moyier, mondo odwar Daudi kuno.
3 Shawulu ya yi sansani a bakin hanyar zuwa tudun Hakila mai fuskantar Yeshimon. Amma Dawuda yana zaune a jeji. Sa’ad da ya ga Shawulu ya biyo shi har zuwa can,
Saulo noloso kambine but yo man e got Hakila momanyore gi Jeshimon, Daudi to ni kama otwo ma otimo ongoro. Kane oneno ni Saulo noseluwe kuno,
4 sai ya aiki’yan leƙen asiri su tabbata lalle Shawulu ya iso can.
ne ooro jombetre mane ongʼeyo ratiro ni Saulo nosechopo.
5 Sai Dawuda ya kintsa ya tafi inda Shawulu ya yi sansani. Ya ga inda Shawulu da Abner ɗan Ner shugaban ƙungiyar soja suka kwanta. Shawulu yana kwance a cikin sansani tare da sojoji kewaye da shi.
Eka Daudi nowuok modhi kuma Saulo nojotie. Noneno kama Saulo gi Abner wuod Ner ma jatend jolwenje, noyudo osenindoe. Saulo ne nindo ei kambi, ka jolweny olwore.
6 Sai Dawuda ya ce wa Ahimelek mutumin Hitti da Abishai ɗan Zeruhiya ɗan’uwan Yowab, “Wa zai gangara tare da ni zuwa sansanin Shawulu?” Sai Abishai ya ce, “Zan tafi tare da kai.”
Daudi nopenjo Ahimelek ja-Hiti gi Abishai wuod Zeruya, mowadgi Joab niya, “Ngʼama biro dhi koda mwalo e kambi ir Saulo?” Abishai nowacho niya, “Abiro dhi kodi.”
7 Saboda haka Dawuda da Abishai suka gangara zuwa wurin rundunar da dare, sai ga Shawulu kwance yana barci a cikin sansani da māshinsa a kafe a ƙasa kusa da kansa. Abner kuwa tare da sojoji suna kwance kewaye da shi.
Daudi gi Abishai nodhi ir jolweny gotieno, Saulo nonindo kanyo e kambi kochwoyo tonge piny yo ka wiye. Abner gi jolweny nonindo kolwore.
8 Abishai ya ce wa Dawuda, “Yau Allah ya ba da maƙiyinka a hannunka. Bari in kafe shi da ƙasa da māshina, zan soke shi da māshi sau ɗaya tak, ba na bukata in soke shi sau biyu.”
Abishai nowachone Daudi niya, “Kawuono Nyasaye oseketo jasiki e lweti. Koro yiena mondo achwowe dichiel gi tonga; ok abi chwowe diriyo.”
9 Amma Dawuda ya ce wa Abishai, “Kada ka hallaka shi. Wa zai sa hannu a kan shafaffe na Ubangiji, har yă tsira?
To Daudi nowachone Abishai niya, “Kik inege! En ngʼa manyalo keto lwete kuom ngʼat Jehova Nyasaye mowir ma ok oket ne bura?”
10 Muddin Ubangiji yana a raye, Ubangiji da kansa zai buge shi, ko yă mutu a lokacinsa, ko kuma yă mutu a wurin yaƙi.
Nowacho niya, “Akwongʼora gi nying Jehova Nyasaye mangima, ni Jehova Nyasaye owuon ema nonege; kata ndalone chiengʼ moro nochopi mi otho kata nodhi e lweny mi notho kuno.
11 Amma Allah yă sawwaƙa in sa hannu a shafaffen Ubangiji, ka ɗauki māshin da butar ruwan da take kusa da kansa mu tafi.”
To Jehova Nyasaye ok diyiena ni mondo ater lweta kuom ngʼat Jehova Nyasaye mowir. Koro kaw tongʼ gi puga mar pi machiegni gi wiye kaeto wadhi.”
12 Saboda haka Dawuda ya ɗauki māshin da butar ruwan da take kusa da Shawulu suka tafi. Ba wanda ya gan su, ba wanda ya san abin da ya faru, ba kuwa wanda ya farka, dukansu suna barci gama Ubangiji ya sa barci mai nauyi ya ɗauke su.
Omiyo Daudi nokawo tongʼ kod puga mar pi mane nitie machiegni gi wi Saulo kendo negidhi. Onge ngʼama nonenogi kata mane ongʼeyo wachno, bende onge ngʼama ne ochiewo. Giduto ne ginindo, nikech Jehova Nyasaye nomiyogi nindo matut.
13 Sa’an nan Dawuda ya haye zuwa wancan gefen kwarin, ya hau kan wani tudu mai ɗan nisa inda Shawulu tare da mutanensa suke. Akwai babban fili tsakaninsu.
Eka Daudi nongʼado modhi loka machielo mochungʼ ewi got kuma bor; ne odhi mochwalore kodgi; ne nitie thuolo malach e kindgi.
14 Sai Dawuda ya kira sojojin Shawulu da kuma Abner ɗan Ner ya ce, “Abner ba za ka amsa mini ba?” Abner ya ce, “Wane ne yake kira yana damun sarki haka?”
Nopenjo jolweny kod Abner wuod Ner niya, “Bende unyalo dwoka, Abner?” Abner nodwoke niya, “In ngʼa maluongo ruoth?”
15 Dawuda ya ce wa Abner, “Wane irin mutum ne kai? Ba kai ne soja mafi iya yaƙi a Isra’ila ba? Don me ba ka yi gadin ranka yă daɗe, sarki da kyau ba? Ɗazu wani ya shiga tsakiyarku don yă kashe ranka yă daɗe, sarki.
Daudi nopenjo Abner niya, “Donge in ngʼama dichwo? To ere ngʼama chal kodi e Israel? Angʼo momiyo ne ok irito ruodhi ma en ruoth? Ngʼato nobiro mondo oneg ruodhi ma ruoth.
16 Abin da ka yi bai yi kyau ba. Muddin Ubangiji yana a raye kai da mutanenka kun cancanci mutuwa, domin ba ku lura da maigidanku shafaffe na Ubangiji ba. Ka duba kewaye da kai, ina māshi da kuma butar ruwan da suke kusa da kansa?”
Gima isetimo ok ber. Akwongʼora gi nying Jehova Nyasaye mangima ni in kod jogi uwinjoru gi tho, nikech ne ok urito ruodhu ma ngʼat Jehova Nyasaye mowir. Ranguru anena, ere tongʼ mar ruoth gi puga mar pi mane nitiere machiegni gi wiye?”
17 Shawulu ya gane muryar Dawuda, sai ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Dawuda ya ce, “I, muryata ce ya ranka yă daɗe, sarki.”
Saulo nochamo dwond Daudi mowacho niya, “Mano en dwondi Daudi wuoda?” Daudi nodwoke niya, “Ee mano dwonda ruodha ma ruoth.”
18 Ya ƙara da cewa, “Don me ranka yă daɗe, yake fafarata? Mene ne na yi? Wane abu ne aka same ni da laifi a kai?
Kendo nomedo wacho niya, “Angʼo momiyo ruodha lawo jatichne? Angʼo masetimo, rach mane madimi abed jaketho?
19 To, bari ranka yă daɗe, sarkina yă kasa kunne yă ji abin da zan faɗa. Idan Ubangiji ne ya sa ka yi fushi da ni, bari yă karɓi hadaya ta hatsi. Amma idan mutane ne suka sa ka, bari a la’anta su, Ubangiji ne shaidata. Gama sun kore ni don kada in sami rabo cikin gādon Ubangiji, suna cewa, ‘Ka je ka bauta wa waɗansu alloli.’
Koro ruoth ma ruodha oyie owinj weche ma jatije wacho. Ka diponi Jehova Nyasaye ema thuya kodi, to madoyie okaw misango. To ka dipo ni ji ema timo mano to mondo okwongʼ-gi e nyim Jehova Nyasaye! Koro giseriemba mondo kik ayud girkeni ma Jehova Nyasaye omiya kagiwacho ni, ‘Dhi iti ne nyiseche mamoko.’
20 Kada ka yarda jinina yă zuba a ƙasa nesa da gaban Ubangiji. Sarkin Isra’ila ya fito yă nemi kuɗin cizo kamar mai farautar kazan duwatsu.”
Koro yie mondo remba kik oo piny kuma bor gi kama Jehova Nyasaye nitie. Ruodh Israel osewuok mondo odwar kikun mana kaka ngʼato dwaro winyo e gode.”
21 Sai Shawulu ya ce, “Na yi zunubi ka dawo Dawuda ɗana. Ba zan yi maka kome ba, domin ka darajarta raina yau. Lalle na yi wawanci! Na yi babban kuskure.”
Eka Saulo nowacho niya, “Asetimo marach, omiyo duogi, Daudi wuoda. Nikech ne ineno ni ngimana ber kendo owinjore bedie kawuono. Ok nachak atem mondo ahinyi kendo. Adieri asetimo tim ngʼat mofuwo kendo aseketho marach.”
22 Dawuda ya ce, “Ga māshin sarki, ka aiko wani saurayi yă zo yă karɓa.
Daudi nodwoko niya, “Tongʼ mar ruoth eri ni ka. Or achiel kuom yawuowi obi oome.
23 Ubangiji yakan sāka wa kowa bisa ga adalcinsa da amincinsa. Ubangiji ya bashe ka a hannuna yau, amma ba zan sa hannuna a kan shafaffe na Ubangiji ba.
To Jehova Nyasaye chiwo pok ne ngʼato ka ngʼato moromore gi ratiche gi timne makare. Kawuono Jehova Nyasaye nochiwi e lweta to ne ok anyal keto lweta kuom ngʼat Jehova Nyasaye mowir.
24 Kamar yadda na ga darajar ranka yau. Haka ma bari Ubangiji yă ga darajar raina, yă cece ni daga dukan wahala.”
Mana kaka ngimani nelongʼona kawuono, mad ngimana bende bed malongʼo ni Jehova Nyasaye mondo oresa e chandruok duto.”
25 Sai Shawulu ya ce wa Dawuda, “Allah yă albarkace ka ɗana, Dawuda, za ka yi manyan abubuwa, tabbatacce kuma ka yi nasara.” Sai Dawuda ya yi tafiyarsa, Shawulu kuwa ya koma gida.
Eka Saulo nowachone Daudi niya, “Mad gwedhi wuoda Daudi; ibiro timo gik madongo adieri inilochi.” Bangʼ mano Daudi nodhi yore, to Saulo nodok dala.

< 1 Sama’ila 26 >