< 1 Sama’ila 26 >

1 Zifawa suka je wurin Shawulu a Gibeya suka ce, “Ashe, ba Dawuda ne ya ɓuya a tudun Hakila da yake fuskantar Yeshimon ba?”
Og Sifiterne kom til Saul i Gibea og sagde: Har ikke David skjult sig paa Hakilas Høj lige for Ørken?
2 Sai Shawulu ya tashi ya gangara zuwa Jejin Zif, tare da zaɓaɓɓun mutane dubu uku na Isra’ila. Suka fita neman Dawuda a can.
Da gjorde Saul sig rede og drog ned til Ørken Sif, og tre Tusinde Mand, udvalgte af Israel, med ham, for at søge efter David i Ørken Sif.
3 Shawulu ya yi sansani a bakin hanyar zuwa tudun Hakila mai fuskantar Yeshimon. Amma Dawuda yana zaune a jeji. Sa’ad da ya ga Shawulu ya biyo shi har zuwa can,
Og Saul lejrede sig ved Hakilas Høj, som ligger lige for Ørken ved Vejen; men David blev i Ørken, og han saa, at Saul kom efter ham i Ørken.
4 sai ya aiki’yan leƙen asiri su tabbata lalle Shawulu ya iso can.
Da sendte David Spejdere og fik at vide, at Saul virkelig var kommen.
5 Sai Dawuda ya kintsa ya tafi inda Shawulu ya yi sansani. Ya ga inda Shawulu da Abner ɗan Ner shugaban ƙungiyar soja suka kwanta. Shawulu yana kwance a cikin sansani tare da sojoji kewaye da shi.
Og David gjorde sig rede og kom til det Sted, hvor Saul havde lejret sig, og David saa Stedet, hvor Saul laa tillige med Abner, Ners Søn, hans Stridshøvedsmand; thi Saul laa i Vognborgen, og Folket havde lejret sig omkring ham.
6 Sai Dawuda ya ce wa Ahimelek mutumin Hitti da Abishai ɗan Zeruhiya ɗan’uwan Yowab, “Wa zai gangara tare da ni zuwa sansanin Shawulu?” Sai Abishai ya ce, “Zan tafi tare da kai.”
Da svarede David og sagde til Hethiteren Akimelek, og til Abisai, Zerujas Søn, Joabs Broder, saaledes: Hvo vil gaa ned med mig til Saul i Lejren? og Abisai svarede: Jeg vil gaa ned med dig.
7 Saboda haka Dawuda da Abishai suka gangara zuwa wurin rundunar da dare, sai ga Shawulu kwance yana barci a cikin sansani da māshinsa a kafe a ƙasa kusa da kansa. Abner kuwa tare da sojoji suna kwance kewaye da shi.
Saa kom David og Abisai til Folket om Natten, og se, Saul laa og sov i Vognborgen, og hans Spyd var stukket i Jorden ved hans Hovedgærde, og Abner og Folket laa omkring ham.
8 Abishai ya ce wa Dawuda, “Yau Allah ya ba da maƙiyinka a hannunka. Bari in kafe shi da ƙasa da māshina, zan soke shi da māshi sau ɗaya tak, ba na bukata in soke shi sau biyu.”
Da sagde Abisai til David: Gud har i Dag overgivet din Fjende i din Haand, saa vil jeg nu stikke Spydet igennem ham og ned i Jorden een Gang, at jeg ej behøver at gøre det anden Gang.
9 Amma Dawuda ya ce wa Abishai, “Kada ka hallaka shi. Wa zai sa hannu a kan shafaffe na Ubangiji, har yă tsira?
Men David sagde til Abisai: Dræb ham ikke; thi hvo vil lægge Haand paa Herrens Salvede og bliver uskyldig?
10 Muddin Ubangiji yana a raye, Ubangiji da kansa zai buge shi, ko yă mutu a lokacinsa, ko kuma yă mutu a wurin yaƙi.
Fremdeles sagde David: Saa vist som Herren lever, uden saa er, at Herren slaar ham, eller hans Dag kommer, at han dør, eller han drager ned i Krigen og omkommer,
11 Amma Allah yă sawwaƙa in sa hannu a shafaffen Ubangiji, ka ɗauki māshin da butar ruwan da take kusa da kansa mu tafi.”
saa lade Herren det være langt fra mig, at udrække min Haand mod Herrens Salvede; men nu, kære, tag Spydet, som er ved hans Hovedgærde, og Vandkrukken, og lader os gaa.
12 Saboda haka Dawuda ya ɗauki māshin da butar ruwan da take kusa da Shawulu suka tafi. Ba wanda ya gan su, ba wanda ya san abin da ya faru, ba kuwa wanda ya farka, dukansu suna barci gama Ubangiji ya sa barci mai nauyi ya ɗauke su.
Saa tog David Spydet og Vandkrukken fra Sauls Hovedgærde, og de gik bort; og der var ingen, som saa det, og ingen, som vidste det, og ingen, som opvaagnede, thi de sov allesammen; thi der var falden en dyb Søvn fra Herren paa dem.
13 Sa’an nan Dawuda ya haye zuwa wancan gefen kwarin, ya hau kan wani tudu mai ɗan nisa inda Shawulu tare da mutanensa suke. Akwai babban fili tsakaninsu.
Der David var kommen over paa hin Side, da stod han paa Bjergets Top langt fra; der var et stort Rum imellem dem.
14 Sai Dawuda ya kira sojojin Shawulu da kuma Abner ɗan Ner ya ce, “Abner ba za ka amsa mini ba?” Abner ya ce, “Wane ne yake kira yana damun sarki haka?”
Og David raabte til Folket og til Abner, Ners Søn, og sagde: Vil du ikke svare, Abner? og Abner svarede og sagde: Hvo er du, som raaber til Kongen?
15 Dawuda ya ce wa Abner, “Wane irin mutum ne kai? Ba kai ne soja mafi iya yaƙi a Isra’ila ba? Don me ba ka yi gadin ranka yă daɗe, sarki da kyau ba? Ɗazu wani ya shiga tsakiyarku don yă kashe ranka yă daɗe, sarki.
Men David sagde til Abner: Er du ikke en Mand? og hvo er som du i Israel? og hvorfor har du ikke vaaget over din Herre Kongen? thi der er kommen een af Folket ind for at dræbe Kongen, din Herre.
16 Abin da ka yi bai yi kyau ba. Muddin Ubangiji yana a raye kai da mutanenka kun cancanci mutuwa, domin ba ku lura da maigidanku shafaffe na Ubangiji ba. Ka duba kewaye da kai, ina māshi da kuma butar ruwan da suke kusa da kansa?”
Dette er ikke en god Ting, som du har gjort; saa vist som Herren lever, I ere Dødens Børn, fordi I ikke have vaaget over eders Herre, Herrens Salvede; og se nu, hvor er Kongens Spyd og den Vandkrukke, som var ved hans Hovedgærde?
17 Shawulu ya gane muryar Dawuda, sai ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Dawuda ya ce, “I, muryata ce ya ranka yă daɗe, sarki.”
Da kendte Saul Davids Røst og sagde: Er dette din Røst, min Søn David? og David sagde: Det er min Røst, min Herre Konge!
18 Ya ƙara da cewa, “Don me ranka yă daɗe, yake fafarata? Mene ne na yi? Wane abu ne aka same ni da laifi a kai?
Og han sagde: Hvorfor forfølger min Herre saa sin Tjener? thi hvad har jeg gjort, og hvad ondt er der i min Haand?
19 To, bari ranka yă daɗe, sarkina yă kasa kunne yă ji abin da zan faɗa. Idan Ubangiji ne ya sa ka yi fushi da ni, bari yă karɓi hadaya ta hatsi. Amma idan mutane ne suka sa ka, bari a la’anta su, Ubangiji ne shaidata. Gama sun kore ni don kada in sami rabo cikin gādon Ubangiji, suna cewa, ‘Ka je ka bauta wa waɗansu alloli.’
Og nu høre dog min Herre Kongen sin Tjeners Ord: Dersom Herren har tilskyndet dig imod mig, da lad ham lugte et Madoffer, men dersom det er Menneskens Børn, da være de forbandede for Herrens Ansigt; thi de have uddrevet mig i Dag, at jeg ikke kan holde mig til Herrens Arv, og de sige: Gak bort, tjen andre Guder!
20 Kada ka yarda jinina yă zuba a ƙasa nesa da gaban Ubangiji. Sarkin Isra’ila ya fito yă nemi kuɗin cizo kamar mai farautar kazan duwatsu.”
Og nu, lad ej mit Blod falde til Jorden, fjernt fra Herrens Ansigt; thi Israels Konge er dragen ud for at opsøge en Loppe, ligesom man jager efter en Agerhøne paa Bjergene.
21 Sai Shawulu ya ce, “Na yi zunubi ka dawo Dawuda ɗana. Ba zan yi maka kome ba, domin ka darajarta raina yau. Lalle na yi wawanci! Na yi babban kuskure.”
Da sagde Saul: Jeg har syndet, kom tilbage min Søn David; thi jeg vil ikke ydermere gøre dig ondt, fordi mit Liv var dyrebart for dine Øjne paa denne Dag, se, jeg har handlet daarlig og er faret vild saare meget.
22 Dawuda ya ce, “Ga māshin sarki, ka aiko wani saurayi yă zo yă karɓa.
Da svarede David og sagde: Se, her er Kongens Spyd; men lad een af de unge Karle komme over og hente det.
23 Ubangiji yakan sāka wa kowa bisa ga adalcinsa da amincinsa. Ubangiji ya bashe ka a hannuna yau, amma ba zan sa hannuna a kan shafaffe na Ubangiji ba.
Men Herren betale den Mand hans Retfærdighed og hans Troskab, i hvis Haand Herren har givet dig i Dag; men jeg vilde ikke udrække min Haand mod Herrens Salvede.
24 Kamar yadda na ga darajar ranka yau. Haka ma bari Ubangiji yă ga darajar raina, yă cece ni daga dukan wahala.”
Og se, ligesom din Sjæl var storligen agtet paa denne Dag for mine Øjne: Saa skal min Sjæl blive storligen agtet for Herrens Øjne, og han skal fri mig af al Angest.
25 Sai Shawulu ya ce wa Dawuda, “Allah yă albarkace ka ɗana, Dawuda, za ka yi manyan abubuwa, tabbatacce kuma ka yi nasara.” Sai Dawuda ya yi tafiyarsa, Shawulu kuwa ya koma gida.
Da sagde Saul til David: Velsignet være du, min Søn David! ja, hvad du tager dig for, skal du ogsaa magte! Saa gik David sin Vej, og Saul vendte om til sit Sted.

< 1 Sama’ila 26 >