< 1 Sama’ila 25 >
1 Sama’ila ya rasu, sai dukan Isra’ila suka taru suka yi makoki saboda shi. Suka binne shi a gidansa a Rama. Sai Dawuda ya gangara zuwa cikin Jejin Faran.
Or, Samuel mourut, et tout Israël fut assemblé; et ils le pleurèrent, et ils l’ensevelirent dans sa maison à Ramatha. Et David, se levant, descendit dans le désert de Pharan.
2 A Mawon, akwai wani mutum wanda yake da dukiya a Karmel, mutumin mai arziki ne ƙwarai. Yana da awaki dubu ɗaya, da tumaki dubu uku waɗanda yake wa aski a Karmel.
Or il y avait un homme dans la solitude de Maon, et sa possession était sur le Carmel; et cet homme était très riche, et il avait trois mille brebis et mille chèvres: et il arriva que l’on tondait son troupeau sur le Carmel.
3 Ana ce da shi Nabal, sunan matarsa kuwa Abigiyel. Tana da hikima ga ta kuma kyakkyawa, amma mijinta mai rowa ne marar mutunci. Shi daga kabilar Kaleb ne.
Or, le nom de cet homme était Nabal, et le nom de sa femme Abigaïl; et cette femme était très prudente et belle; mais son mari était dur, très méchant et rusé: or, il était de la race de Caleb.
4 Lokacin da Dawuda yake a jeji, ya ji labari cewa Nabal yana askin tumaki.
Lors donc que David eut appris dans le désert que Nabal tondait son troupeau,
5 Sai ya zaɓi samari goma ya aike su wurin Nabal a Karmel su gaishe shi a madadinsa,
Il envoya dix jeunes hommes, et leur dit: Montez sur le Carmel et vous irez vers Nabal, et vous le saluerez en mon nom pacifiquement;
6 su ce masa, “Ranka yă daɗe, ina maka fatan alheri, kai da gidanka da dukan abin da kake da shi!
Et vous direz: Que la paix soit avec mes frères et avec toi; et que la paix soit en ta maison, et que la paix soit sur tout ce que tu as.
7 “Na ji cewa, yanzu lokacin askin tumaki ne. Sa’ad da makiyayanka suke tare da mu, ba mu cuce su ba, kuma duk zamansu a Karmel ba abin da yake nasu da ya ɓata.
J’ai appris que tes pasteurs, qui étaient avec nous au désert, tondaient ton troupeau: jamais nous ne les avons inquiétés, et jamais il ne leur a rien manqué de leur troupeau, pendant tout le temps qu’ils ont été avec nous sur le Carmel.
8 Ka tambayi bayinka za su kuwa gaya maka. Saboda haka ka yi wa mutanena kirki, gama yau ranar biki ce. Ina roƙonka ka ba wa samarina, wato, bayinka, da ni ɗanka Dawuda, duk abin da kake iya ba su.”
Interroge tes serviteurs, et ils te le diront. Maintenant donc, que tes serviteurs trouvent grâce à tes yeux; car nous sommes venus dans un bon jour: tout ce que ta main trouvera, donne-le à tes serviteurs et à ton fils David.
9 Da mutanen Dawuda suka isa wurin Nabal, suka ba wa Nabal wannan saƙo a sunan Dawuda, sai suka jira.
Ainsi lorsque les serviteurs de David furent venus, ils dirent à Nabal toutes ces paroles au nom de David, puis ils gardèrent le silence.
10 Nabal ya ce wa mutanen Dawuda, “Wane ne wannan Dawuda? Wane ne wannan ɗan Yesse? Yawancin bayi suna tayar wa iyayengijinsu a kwanakin nan.
Mais Nabal, répondant aux serviteurs de David, dit: Qui est David? et qui est le fils d’Isaï? Aujourd’hui les serviteurs qui fuient leurs maîtres s’augmentent.
11 Don me zan ɗauki burodina da ruwana, da kuma naman da na yanka saboda masu yin wa tumakina aski in ba mutanen da ban ma san inda suka fito ba?”
Je prendrai donc mes pains, mon eau, la chair des bêtes que j’ai tuées pour mes tondeurs, et je les donnerai à des hommes qui sont je ne sais d’où?
12 Mutanen Dawuda suka juya suka koma. Da suka iso sai suka faɗa wa Dawuda abin da Nabal ya ce.
C’est pourquoi les serviteurs de David revinrent par leur chemin, et, étant retournés, ils vinrent et lui rapportèrent toutes les paroles que Nabal avait dites.
13 Dawuda ya ce wa mutanensa, “Kowa yă rataya takobinsa.” Sai duk suka yi haka. Dawuda kuma ya rataya nasa. Mutum wajen ɗari huɗu suka tafi tare da Dawuda, mutum ɗari biyu kuwa suka zauna suna gadin kayansu.
Alors David dit à ses serviteurs: Que chacun se ceigne de son glaive. Et ils se ceignirent chacun de leur glaive, David lui-même se ceignit de son épée; et environ quatre cents hommes suivirent David; mais deux cents restèrent près des bagages.
14 Ɗaya daga cikin bayin Nabal ya gaya wa Abigiyel matar Nabal cewa, “Dawuda ya aiko da bayinsa daga jeji su gai da maigida, amma maigida ya zazzage su.
Mais un des serviteurs de Nabal l’annonça à Abigaïl, sa femme, disant: Voilà que David a envoyé des messagers du désert, pour bénir notre maître, et il les a repoussés.
15 Waɗannan mutane kuwa sun yi mana kirki ƙwarai, ba su ba mu wata wahala ba. Babu abu guda da ya ɓace mana dukan lokacin da muke tare da su.
Ces hommes ont été assez bons pour nous, et ne nous ont point inquiétés, et rien n’a jamais péri de nos troupeaux, pendant tout le temps que nous nous sommes trouvés avec eux dans le désert.
16 Dare da rana sun zama mana katanga kewaya da mu, a duk tsawon lokacin da muke kiwon tumakinmu kusa da su.
ils étaient comme une muraille pour nous, tant la nuit que le jour, durant tous les jours que nous avons fait paître au milieu d’eux les troupeaux.
17 Ki yi nazari a kai, ki ga ko za ki iya yin wani abu, domin masifa yana nan rataye a wuyan maigidanmu da dukan iyalin gidansa. Shi mugun mutum ne wanda ba wani da zai iya yin masa magana.”
C’est pourquoi considérez et pensez à ce que vous ferez; parce que la malice est à son comble contre votre mari et contre votre maison, et que lui-même est un fils de Bélial, en sorte que personne ne peut lui parler.
18 Abigiyel ba tă ɓata lokaci ba. Ta ɗauki burodi guda ɗari biyu, da salkar ruwan inabi biyu da tumaki biyar da aka gyara, da soyayyen hatsi mudu biyar, da waina guda ɗari na’ya’yan inabi, da masa ɗari biyu na kauɗar ɓaure ta labta wa jakuna.
Abigaïl donc se hâta, et elle prit deux cents pains, deux outres de vin, cinq béliers cuits, cinq mesures de grains rôtis, cent grappes de raisins secs et deux cents panerées de figues sèches: elle les plaça sur les ânes;
19 Sai ta ce wa bawanta, “Yi gaba, zan bi ka”. Amma ba tă gaya wa Nabal, mijinta ba.
Et elle dit à ses serviteurs: Précédez-moi; voici que je vous suivrai par derrière: mais à son mari Nabal, elle n’en dit rien.
20 Da tana tafiya a kan jaki, ta kai gindin wani dutse ke nan, sai ga Dawuda da mutanensa suna gangarowa zuwa wajen da take. Sai ta tafi, ta sadu da su.
Lors donc quelle fut montée sur son âne, et qu’elle descendait au pied de la montagne, David et ses serviteurs descendaient à sa rencontre; et elle-même alla au devant d’eux.
21 Bai daɗe ba da Dawuda ya ce a ransa, “Ashe, a banza ne na yi ta lura da dukan abin da yake na mutumin nan a jeji, har ba abinsa da ya ɓace. Ga shi, ya rama mini alheri da mugunta.
Et David dit: Vraiment, c’est en vain que j’ai conservé tout ce qui était à lui dans le désert, et que rien n’a péri de tout ce qui lui appartenait; et il m’a rendu le mal pour le bien.
22 Bari Allah yă yi duk abin da ya ga dama da ni in na bar ko ɗaya daga mazan da suke da tare shi, gobe da safe.”
Que Dieu fasse ceci aux ennemis de David, et qu’il ajoute cela, si de tout ce qui lui appartient, je laisse jusqu’au matin un seul urinant contre une muraille.
23 Da Abigiyel ta ga Dawuda, sai ta gaggauta ta sauka daga kan jaki, ta rusuna a gaban Dawuda da fuskarta har ƙasa.
Mais lorsqu’Abigaïl eut vu David, elle se hâta, descendit de son âne, tomba sur sa face devant David, et se prosterna sur la terre;
24 Ta fāɗi a ƙafafunsa ta ce, “Bari laifin yă zama nawa, ranka yă daɗe. Ina roƙonka ka bar baiwarka ta yi magana, ka ji abin da baiwarka za tă ce.
Puis elle se jeta à ses pieds, et dit: Sur moi soit, mon seigneur, cette iniquité: que votre servante, je vous conjure, parle à vos oreilles, et écoutez les paroles de votre servante.
25 Kada ranka yă daɗe, yă kula da Nabal, mugun mutumin nan. Shi dai kamar sunansa ne, sunansa Wawa ne, kuma wawanci yana cikinsa. Amma ni baiwarka, ban ga mutanen da ranka yă daɗe ya aika ba.
Que mon seigneur roi n’arrête pas son cœur sur cet homme inique de Nabal, puisque, selon son nom, il est insensé, et qu’il y a folie en lui; mais moi, votre servante, je n’ai pas vu, mon seigneur, les serviteurs que vous avez envoyés.
26 Da yake yanzu, ya mai girma, Ubangiji ya hana ka zubar da jini da kuma ɗaukan wa kanka fansa, muddin Ubangiji yana raye, kai kuma kana a raye, bari maƙiyinka da dukan waɗanda suke niyya su cuci shugabana su zama kamar Nabal.
Maintenant donc, mon seigneur, le Seigneur vit, et votre âme vit! le Seigneur qui vous a empêché de venir dans du sang, et qui vous a sauvé votre main; et maintenant qu’ils deviennent comme Nabal, vos ennemis, et ceux qui cherchent la perte de mon seigneur.
27 Bari kuma ka karɓi wannan kyautar da baiwarka ta kawo don samarin da suke binka.
C’est pourquoi, recevez cette bénédiction que votre servante vous a apportée, à vous, mon seigneur, et donnez-la aux serviteurs qui vous suivent, vous, mon seigneur.
28 Ina roƙonka ka gafarta wa baiwarka laifinta gama tabbatacce Ubangiji zai ba shugabana dawwammamiyar sarauta, gama kana yin yaƙin Ubangiji ne. Kuma ba wani mugun abin da zai same ka muddin kana a raye.
Remettez l’iniquité de votre servante; car le Seigneur vous fera très certainement à vous, mon seigneur, une maison fidèle, parce que, mon seigneur, vous combattez les combats du Seigneur: qu’il ne se trouve donc point de malice en vous durant tous les jours de votre vie.
29 Ko da yake wani mutum yana fafaranka domin yă kashe ka, Ubangiji Allahnka zai kiyaye ranka. Amma za a wurgar da rayukan maƙiyanka kamar yadda ake wurga dutsen majajjawa.
Car s’il s’élève un jour un homme qui vous persécute, et cherche votre âme, l’âme de mon seigneur sera gardée, comme dans le faisceau des vivants, auprès du Seigneur votre Dieu; mais l’âme de vos ennemis tournoiera, comme du tournoiement rapide de la fronde.
30 Sa’ad da Ubangiji ya cika kowane alherinsa da ya yi wa shugabana alkawari, ya kuma keɓe shi sarki a bisa Isra’ila,
Lors donc que le Seigneur vous aura fait à vous, mon seigneur, tous les biens qu’il a prédits de vous, et qu’il vous aura établi chef sur Israël,
31 kada yă zama cewa zuciyarka ta ba ka laifi ko ka damu cewa kana da alhakin jini, kada ka yi ramuwa da kanka. Sa’ad da Ubangiji ya nuna maka alheri, ka tuna da ni, baiwarka.”
Ce ne sera pas pour vous un sujet de soupir, ni un scrupule de conscience pour mon seigneur, d’avoir versé un sang innocent, et de vous être vengé vous-même: et lorsque le Seigneur aura fait du bien à mon seigneur, vous vous souviendrez de votre servante.
32 Dawuda ya ce wa Abigiyel, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya aiko ki don ki same ni yau.
Et David répondit à Abigaïl: Béni le Seigneur Dieu d’Israël, qui vous a envoyée aujourd’hui à ma rencontre! et bénie votre parole!
33 Bari Allah yă albarkace ki saboda hikima yanke hukuncinki da kuma hana ni zubar da jini da ɗauka wa kaina fansa da hannuna a wannan rana.
Et bénie vous-même, qui m’avez empêché de venir pour du sang, et de me venger de ma main!
34 Ubangiji, ya hana ni in yi miki ɓarna. Da ba don kin zo kin sadu da ni ba, na rantse da Ubangiji, Allah na Isra’ila Mai Rai, babu ko ɗaya daga cikin mazan gidan Nabal da zai rage gobe da safe.”
Autrement, le Seigneur Dieu d’Israël vit! lequel m’a empêché de vous faire du mal: si vous n’étiez venue si vite à ma rencontre, il ne serait pas resté à Nabal, jusqu’à la lumière du matin, un seul urinant contre une muraille.
35 Sa’an nan Dawuda ya karɓi abin da ta kawo masa daga hannunta, ya kuma ce mata, “Ki koma gida kada ki damu, na ji koke-kokenki, zan kuma biya miki bukatarki.”
David donc reçut de sa main tout ce qu’elle lui avait apporté, et il lui dit: Allez en paix dans votre maison; voilà que j’ai entendu votre voix, et honoré votre face.
36 Da Abigiyel ta kai gida sai ta sami Nabal cikin gida yana ta fama biki iri na sarakuna. Yana ji wa ransa daɗi, ya kuma bugu tilis, saboda haka ba tă ce masa kome ba sai da gari ya waye.
Or, Abigaïl vint vers Nabal; et voilà qu’il y avait un festin dans sa maison, comme le festin du roi, et le cœur de Nabal était joyeux; car Nabal était fort ivre; et elle ne lui dit pas une parole grande ou petite jusqu’au matin.
37 Da safe sa’ad da Nabal ya natsu, sai matarsa ta gaya masa dukan abin da ya faru. Sai zuciyarsa ta tsinke, ya zama kamar dutse.
Mais au point du jour, quand Nabal fut revenu de son ivresse, sa femme lui rapporta ces choses, et son cœur mourut intérieurement, et il devint lui-même comme une pierre.
38 Bayan kusan kwana goma, Ubangiji ya bugi Nabal, sai ya mutu.
Et lorsque dix jours furent passés, le Seigneur frappa Nabal, et il mourut.
39 Da Dawuda ya sami labarin mutuwar Nabal, sai ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya sāka mini a kan irin renin da Nabal ya yi mini. Ya hana bawansa yin mugunta, ga shi ya ɗora wa Nabal muguntar da ya yi.” Sai Dawuda ya aika wa Abigiyel cewa tă zama matarsa.
Lorsque David eut appris que Nabal était mort, il dit: Béni le Seigneur qui a jugé la cause de mon opprobre, venant de la main de Nabal, et qui a préservé son serviteur du mal! car le Seigneur a rejeté la malice de Nabal sur sa tête. David envoya donc, et il parla à Abigaïl, afin de la prendre pour femme.
40 Bayin Dawuda suka tafi Karmel suka ce wa Abigiyel, “Dawuda ya aike mu gare ki, mu zo mu ɗauke ki ki zama matarsa.”
Et les serviteurs de David vinrent vers Abigaïl sur le Carmel, et ils lui parlèrent, disant: David nous a envoyés vers vous, désirant de vous prendre pour femme.
41 Sai ta rusuna da fuskarta har ƙasa ta ce, “Ni baranyarka ce, na shirya in bauta maka in kuma wanke ƙafafun bayin shugabana.”
Abigaïl se levant se prosterna, inclinée vers la terre, et dit: Voici ta servante; qu’elle soit servante pour laver les pieds des serviteurs de mon seigneur.
42 Abigiyel ta tashi da sauri ta hau jaki, ta kuma sa’yan mata biyar da suke mata hidima su bi ta, suka tafi tare da’yan saƙon Dawuda. Ta kuwa zama matarsa.
Et Abigaïl se hâta, et elle se leva, monta sur son âne, et cinq jeunes filles, ses suivantes, allèrent avec elle; et elle suivit les messagers de David; et elle devint sa femme.
43 Dawuda a lokacin ya riga ya auri Ahinowam daga Yezireyel, dukansu suka zama matansa.
Mais David prit aussi Achinoam de Jezraël; et l’une et l’autre fut sa femme.
44 Amma Shawulu ya aurar da Mikal,’yarsa, matar Dawuda, ga Falti ɗan Layish wanda yake daga Gallim.
Or, Saül donna Michol, sa fille, femme de David, à Phalti, fils de Laïs, qui était de Gallim.