< 1 Sama’ila 25 >
1 Sama’ila ya rasu, sai dukan Isra’ila suka taru suka yi makoki saboda shi. Suka binne shi a gidansa a Rama. Sai Dawuda ya gangara zuwa cikin Jejin Faran.
Forsothe Samuel was deed; and al Israel was gaderid to gidere, and thei biweiliden hym greetly, and birieden hym in his hows in Ramatha. And Dauid roos, and yede doun in to deseert of Faran.
2 A Mawon, akwai wani mutum wanda yake da dukiya a Karmel, mutumin mai arziki ne ƙwarai. Yana da awaki dubu ɗaya, da tumaki dubu uku waɗanda yake wa aski a Karmel.
Forsothe a `man was in Maon, and his possessioun was in Carmele, and thilke man was ful greet, and thre thousynde scheep and a thousynde geet `weren to hym; and it bifelde that his flocke was clippid in Carmele.
3 Ana ce da shi Nabal, sunan matarsa kuwa Abigiyel. Tana da hikima ga ta kuma kyakkyawa, amma mijinta mai rowa ne marar mutunci. Shi daga kabilar Kaleb ne.
Forsothe the name of that man was Nabal, and the name of his wijf was Abigail; and thilke womman was moost prudent and fair; forsothe hir hosebond was hard and ful wickid and malicious; sotheli he was of the kyn of Caleph.
4 Lokacin da Dawuda yake a jeji, ya ji labari cewa Nabal yana askin tumaki.
Therfor whanne Dauid hadde herde in deseert, that Nabal clippide his floc,
5 Sai ya zaɓi samari goma ya aike su wurin Nabal a Karmel su gaishe shi a madadinsa,
he sente ten yonge men, and seide to hem, Stie ye in to Carmele, and ye schulen come to Nabal, and ye schulen grete hym of my name pesibli;
6 su ce masa, “Ranka yă daɗe, ina maka fatan alheri, kai da gidanka da dukan abin da kake da shi!
and ye schulen seie thus, Pees be to my britheren and to thee, and pees be to thin hows, and pees be to alle thingis, `what euer thingis thou hast.
7 “Na ji cewa, yanzu lokacin askin tumaki ne. Sa’ad da makiyayanka suke tare da mu, ba mu cuce su ba, kuma duk zamansu a Karmel ba abin da yake nasu da ya ɓata.
Y herde that thi scheepherdis, that weren with vs in deseert, clippiden thi flockis; we weren neuere diseseful to hem, nether ony tyme ony thing of the floc failide to hem, in al time in which thei weren with vs in Carmele;
8 Ka tambayi bayinka za su kuwa gaya maka. Saboda haka ka yi wa mutanena kirki, gama yau ranar biki ce. Ina roƙonka ka ba wa samarina, wato, bayinka, da ni ɗanka Dawuda, duk abin da kake iya ba su.”
axe thi children, and thei schulen schewe to thee. Now therfor thi children fynde grace in thin iyen; for in a good dai we camen to thee; what euer thing thin hond fyndith, yyue to thi seruauntis, and to thi sone Dauid.
9 Da mutanen Dawuda suka isa wurin Nabal, suka ba wa Nabal wannan saƙo a sunan Dawuda, sai suka jira.
And whanne the children of Dauid hadden come, thei spaken to Nabal alle these wordis in the name of Dauid, and helden pees.
10 Nabal ya ce wa mutanen Dawuda, “Wane ne wannan Dawuda? Wane ne wannan ɗan Yesse? Yawancin bayi suna tayar wa iyayengijinsu a kwanakin nan.
Forsoth Nabal answeride to the children of Dauid, and seide, Who is Dauith? and who is the sone of Isai? To dai seruauntis encreesiden that fleen her lords.
11 Don me zan ɗauki burodina da ruwana, da kuma naman da na yanka saboda masu yin wa tumakina aski in ba mutanen da ban ma san inda suka fito ba?”
Therfor schal Y take my looues and my watris, and the fleischis of beestis, whiche Y haue slayn to my schereris, and schal Y yyue to men, whiche Y knowe not of whennus thei ben?
12 Mutanen Dawuda suka juya suka koma. Da suka iso sai suka faɗa wa Dawuda abin da Nabal ya ce.
Therfor the children of Dauid yeden ayen bi her weie; and thei turneden ayen, and camen, and telden to hym alle wordis whiche Nabal hadde seid.
13 Dawuda ya ce wa mutanensa, “Kowa yă rataya takobinsa.” Sai duk suka yi haka. Dawuda kuma ya rataya nasa. Mutum wajen ɗari huɗu suka tafi tare da Dawuda, mutum ɗari biyu kuwa suka zauna suna gadin kayansu.
Thanne Dauid seide to hise children, Ech man be gird with his swerd. And alle men weren gird with her swerdis, and Dauid also was gird with his swerd; and as foure hundrid men sueden Dauid, forsothe two hundrid leften at the fardels.
14 Ɗaya daga cikin bayin Nabal ya gaya wa Abigiyel matar Nabal cewa, “Dawuda ya aiko da bayinsa daga jeji su gai da maigida, amma maigida ya zazzage su.
Forsothe oon of hise children telde to Abigail, wijf of Nabal, and seide, Lo! Dauid sente messangeris fro deseert, that thei schulden blesse oure lord, and he turnede hem awey;
15 Waɗannan mutane kuwa sun yi mana kirki ƙwarai, ba su ba mu wata wahala ba. Babu abu guda da ya ɓace mana dukan lokacin da muke tare da su.
these men weren good ynow, and not diseseful to vs, and no thing perischide `in ony tyme in al the tyme in which we lyueden with hem in deseert;
16 Dare da rana sun zama mana katanga kewaya da mu, a duk tsawon lokacin da muke kiwon tumakinmu kusa da su.
thei weren to vs for a wal, bothe in niyt and in dai, in alle daies in whiche we lesewiden flockis at hem.
17 Ki yi nazari a kai, ki ga ko za ki iya yin wani abu, domin masifa yana nan rataye a wuyan maigidanmu da dukan iyalin gidansa. Shi mugun mutum ne wanda ba wani da zai iya yin masa magana.”
Wherfor biholde thou, and thenke, what thou schalt do; for malice is fillid ayens thin hosebonde, and ayens `thin hows; and he is the sone of Belial, so that no man may speke to him.
18 Abigiyel ba tă ɓata lokaci ba. Ta ɗauki burodi guda ɗari biyu, da salkar ruwan inabi biyu da tumaki biyar da aka gyara, da soyayyen hatsi mudu biyar, da waina guda ɗari na’ya’yan inabi, da masa ɗari biyu na kauɗar ɓaure ta labta wa jakuna.
Therfor Abigail hastide, and took two hundrid looues, and two vessels of wyn, and fyue whetheris sodun, and seuene buyschelis and an half of flour, and an hundrid bundles of dried grape, and two hundrid gobetis of dried figus; and puttide on assis,
19 Sai ta ce wa bawanta, “Yi gaba, zan bi ka”. Amma ba tă gaya wa Nabal, mijinta ba.
and seide to hir children, Go ye bifor me; lo! Y schal sue you `aftir the bak. Forsothe sche schewide not to hir hosebonde Nabal.
20 Da tana tafiya a kan jaki, ta kai gindin wani dutse ke nan, sai ga Dawuda da mutanensa suna gangarowa zuwa wajen da take. Sai ta tafi, ta sadu da su.
Therfor whanne sche hadde stied on the asse, and cam doun `at the roote of the hil, and Dauid and hise men camen doun in to the comyng `of hir; whiche also sche mette.
21 Bai daɗe ba da Dawuda ya ce a ransa, “Ashe, a banza ne na yi ta lura da dukan abin da yake na mutumin nan a jeji, har ba abinsa da ya ɓace. Ga shi, ya rama mini alheri da mugunta.
And Dauid seide, Verili in veyn Y haue kept alle thingis that weren of this Nabal in the deseert, and no thing perischide of alle thingis that perteyneden to hym, and he hath yolde to me yuel for good.
22 Bari Allah yă yi duk abin da ya ga dama da ni in na bar ko ɗaya daga mazan da suke da tare shi, gobe da safe.”
The Lord do these thingis, and adde these thingis to the enemyes of Dauid, if Y schal leeue of alle thingis that perteynen to him til the morewe a pisser to the wal.
23 Da Abigiyel ta ga Dawuda, sai ta gaggauta ta sauka daga kan jaki, ta rusuna a gaban Dawuda da fuskarta har ƙasa.
Sotheli whanne Abigail siy Dauid, sche hastide, and yede doun of the asse; and sche fel doun bifor Dauid on hir face, and worschipide on the erthe.
24 Ta fāɗi a ƙafafunsa ta ce, “Bari laifin yă zama nawa, ranka yă daɗe. Ina roƙonka ka bar baiwarka ta yi magana, ka ji abin da baiwarka za tă ce.
And sche felde doun to hise feet, and seide, My lord the kyng, this wickydnesse be in me; Y biseche, speke thin handmayden in thin eeris, and here thou the wordis of thi seruauntesse;
25 Kada ranka yă daɗe, yă kula da Nabal, mugun mutumin nan. Shi dai kamar sunansa ne, sunansa Wawa ne, kuma wawanci yana cikinsa. Amma ni baiwarka, ban ga mutanen da ranka yă daɗe ya aika ba.
Y preie, my lord the kyng, sette not his herte on this wickid man Nabal, for bi his name he is a fool, and foli is with hym; but, my lord, Y thin handmayde siy not thi children, whiche thou sentist.
26 Da yake yanzu, ya mai girma, Ubangiji ya hana ka zubar da jini da kuma ɗaukan wa kanka fansa, muddin Ubangiji yana raye, kai kuma kana a raye, bari maƙiyinka da dukan waɗanda suke niyya su cuci shugabana su zama kamar Nabal.
Now therfor, my lord, the Lord lyueth, and thi soule lyueth, which Lord forbeed thee, lest thou schuldist come in to blood, and he sauede thi soule to thee; and now thin enemyes, and thei that seken yuel to my lord, be maad as Nabal.
27 Bari kuma ka karɓi wannan kyautar da baiwarka ta kawo don samarin da suke binka.
Wherfor resseyue thou this blessyng, which thin handmaide brouyte to thee, my lord, and yyue thou to the children that suen thee, my lord.
28 Ina roƙonka ka gafarta wa baiwarka laifinta gama tabbatacce Ubangiji zai ba shugabana dawwammamiyar sarauta, gama kana yin yaƙin Ubangiji ne. Kuma ba wani mugun abin da zai same ka muddin kana a raye.
Do thou awey the wickidnesse of thi seruauntesse; for the Lord makynge schal make a feithful hows to thee, my lord, for thou, my lord, fiytist the batels of the Lord; therfor malice be not foundun in thee in alle dais of thi lijf.
29 Ko da yake wani mutum yana fafaranka domin yă kashe ka, Ubangiji Allahnka zai kiyaye ranka. Amma za a wurgar da rayukan maƙiyanka kamar yadda ake wurga dutsen majajjawa.
For if a man risith ony tyme, and pursueth thee, and sekith thi lijf, the lijf of my lord schal be kept as in a bundel of lyuynge trees, at thi Lord God; forsothe the soule of thin enemyes schal be hurlid round aboute as in feersnesse, and sercle of a slynge.
30 Sa’ad da Ubangiji ya cika kowane alherinsa da ya yi wa shugabana alkawari, ya kuma keɓe shi sarki a bisa Isra’ila,
Therfor whanne the Lord hath do to thee, my lord, alle these goode thingis, whiche he spak of thee, and hath ordeyned thee duyk on Israel,
31 kada yă zama cewa zuciyarka ta ba ka laifi ko ka damu cewa kana da alhakin jini, kada ka yi ramuwa da kanka. Sa’ad da Ubangiji ya nuna maka alheri, ka tuna da ni, baiwarka.”
this schal not be in to siyyng and in to doute of herte to thee, my lord, that thou hast sched out giltles blood, ether that thou hast vengid thee. And whanne the Lord hath do wel to thee, my lord, thou schalt haue mynde on thin handmaide, and thou schalt do wel to hir.
32 Dawuda ya ce wa Abigiyel, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya aiko ki don ki same ni yau.
And Dauid seide to Abigail, Blessid be the Lord God of Israel, that sente thee to dai in to my comyng, and blessid be thi speche;
33 Bari Allah yă albarkace ki saboda hikima yanke hukuncinki da kuma hana ni zubar da jini da ɗauka wa kaina fansa da hannuna a wannan rana.
and blessid be thou, that hast forbede me, lest Y yede to blood, and vengide me with myn hond;
34 Ubangiji, ya hana ni in yi miki ɓarna. Da ba don kin zo kin sadu da ni ba, na rantse da Ubangiji, Allah na Isra’ila Mai Rai, babu ko ɗaya daga cikin mazan gidan Nabal da zai rage gobe da safe.”
ellis the Lord God of Israel lyueth, which forbeed me, `lest Y dide yuel to thee, if thou haddist not soone come in to `metyng to me, a pissere to the wal schulde not haue left to Nabal til to the morewe liyt.
35 Sa’an nan Dawuda ya karɓi abin da ta kawo masa daga hannunta, ya kuma ce mata, “Ki koma gida kada ki damu, na ji koke-kokenki, zan kuma biya miki bukatarki.”
Therfor Dauid resseyuede of hir hond alle thingis whiche sche hadde brouyt to hym; and he seide to hir, Go thou in pees in to thin hows; lo! Y herde thi vois, and Y onouride thi face.
36 Da Abigiyel ta kai gida sai ta sami Nabal cikin gida yana ta fama biki iri na sarakuna. Yana ji wa ransa daɗi, ya kuma bugu tilis, saboda haka ba tă ce masa kome ba sai da gari ya waye.
Forsothe Abigail cam to Nabal; and, lo! a feeste was to him in his hows, as the feeste of a kyng; and the herte of Nabal was iocounde, for he was `drunkun greetli; and sche schewide not to hym a word litil ether greet til the morewe.
37 Da safe sa’ad da Nabal ya natsu, sai matarsa ta gaya masa dukan abin da ya faru. Sai zuciyarsa ta tsinke, ya zama kamar dutse.
Forsothe in the morewtid, whanne Nabal hadde defied the wiyn, his wijf schewide to hym alle these wordis; and his herte was almest deed with ynne, and he was maad as a stoon.
38 Bayan kusan kwana goma, Ubangiji ya bugi Nabal, sai ya mutu.
And whanne ten daies hadden passid, the Lord smoot Nabal, and he was deed.
39 Da Dawuda ya sami labarin mutuwar Nabal, sai ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya sāka mini a kan irin renin da Nabal ya yi mini. Ya hana bawansa yin mugunta, ga shi ya ɗora wa Nabal muguntar da ya yi.” Sai Dawuda ya aika wa Abigiyel cewa tă zama matarsa.
Which thing whanne Dauid hadde herd, Nabal deed, he seide, Blessid be the Lord God, that vengide the cause of my schenschip of the hond of Nabal, and kepte his seruaunt fro yuel, and the Lord yeldide the malice of Nabal in to the heed of hym. Therfor Dauid sente, and spak to Abigail, that he wolde take hir wijf to hym.
40 Bayin Dawuda suka tafi Karmel suka ce wa Abigiyel, “Dawuda ya aike mu gare ki, mu zo mu ɗauke ki ki zama matarsa.”
And the children of Dauid camen to Abigail in to Carmele, and spaken to hir, and seiden, Dauid sente vs to thee, that he take thee in to wijf to hym.
41 Sai ta rusuna da fuskarta har ƙasa ta ce, “Ni baranyarka ce, na shirya in bauta maka in kuma wanke ƙafafun bayin shugabana.”
And sche roos, and worschipide lowe to erthe, and seide, Lo! thi seruauntesse be in to an handmayde, that sche waische the feet of the seruauntis of my lord.
42 Abigiyel ta tashi da sauri ta hau jaki, ta kuma sa’yan mata biyar da suke mata hidima su bi ta, suka tafi tare da’yan saƙon Dawuda. Ta kuwa zama matarsa.
And Abigail hastide, and roos, and stiede on an asse; and fyue damesels, sueris of hir feet, yeden with hir, and sche suede the messangeris of Dauid, and was maad wijf to hym.
43 Dawuda a lokacin ya riga ya auri Ahinowam daga Yezireyel, dukansu suka zama matansa.
But also Dauid took Achynoem of Jezrael, and euer eithir was wijf to hym;
44 Amma Shawulu ya aurar da Mikal,’yarsa, matar Dawuda, ga Falti ɗan Layish wanda yake daga Gallim.
forsothe Saul yaf Mycol his douytir, wijf of Dauid, to Phalti, the sone of Lais, that was of Gallym.