< 1 Sama’ila 25 >
1 Sama’ila ya rasu, sai dukan Isra’ila suka taru suka yi makoki saboda shi. Suka binne shi a gidansa a Rama. Sai Dawuda ya gangara zuwa cikin Jejin Faran.
And he died Samuel and they gathered together all Israel and they mourned for him and they buried him at house his in Ramah and he arose David and he went down to [the] wilderness of Paran.
2 A Mawon, akwai wani mutum wanda yake da dukiya a Karmel, mutumin mai arziki ne ƙwarai. Yana da awaki dubu ɗaya, da tumaki dubu uku waɗanda yake wa aski a Karmel.
And a man [was] in Maon and business his [was] in Carmel and the man [was] great very and [belonged] to him sheep three thousand and one thousand goats and it was when sheared sheep his in Carmel.
3 Ana ce da shi Nabal, sunan matarsa kuwa Abigiyel. Tana da hikima ga ta kuma kyakkyawa, amma mijinta mai rowa ne marar mutunci. Shi daga kabilar Kaleb ne.
And [the] name of the man [was] Nabal and [the] name of wife his [was] Abigail and the woman [was] good of insight and beautiful of appearance and the man [was] hard and evil of deeds and he ([was] a Calebite. *Q(K)*)
4 Lokacin da Dawuda yake a jeji, ya ji labari cewa Nabal yana askin tumaki.
And he heard David in the wilderness that [was] shearing Nabal sheep his.
5 Sai ya zaɓi samari goma ya aike su wurin Nabal a Karmel su gaishe shi a madadinsa,
And he sent David ten young men and he said David to the young men go up Carmel towards and you will go to Nabal and you will ask of him in name my to welfare.
6 su ce masa, “Ranka yă daɗe, ina maka fatan alheri, kai da gidanka da dukan abin da kake da shi!
And you will say thus to the living [one] and you peace and house your peace and all that [belongs] to you peace.
7 “Na ji cewa, yanzu lokacin askin tumaki ne. Sa’ad da makiyayanka suke tare da mu, ba mu cuce su ba, kuma duk zamansu a Karmel ba abin da yake nasu da ya ɓata.
And now I have heard that shearers [belong] to you now the shepherds who [belong] to you they have been with us not we have humiliated them and not it has been missing to them anything all [the] days of being they in Carmel.
8 Ka tambayi bayinka za su kuwa gaya maka. Saboda haka ka yi wa mutanena kirki, gama yau ranar biki ce. Ina roƙonka ka ba wa samarina, wato, bayinka, da ni ɗanka Dawuda, duk abin da kake iya ba su.”
Ask own young men your so they may tell to you and let them find the young men favor in view your for on a day good we have come give! please [that] which it will find hand your to servants your and to son your to David.
9 Da mutanen Dawuda suka isa wurin Nabal, suka ba wa Nabal wannan saƙo a sunan Dawuda, sai suka jira.
And they went [the] young men of David and they spoke to Nabal according to all the words these in [the] name of David and they rested.
10 Nabal ya ce wa mutanen Dawuda, “Wane ne wannan Dawuda? Wane ne wannan ɗan Yesse? Yawancin bayi suna tayar wa iyayengijinsu a kwanakin nan.
And he answered Nabal [the] servants of David and he said who? [is] David and who? [is] [the] son of Jesse this day they are many servants who break away each one from before master his.
11 Don me zan ɗauki burodina da ruwana, da kuma naman da na yanka saboda masu yin wa tumakina aski in ba mutanen da ban ma san inda suka fito ba?”
And will I take bread my and water my and slaughter my which I have slaughtered for shearers my and will I give [them] to men who not I know where? from this [are] they.
12 Mutanen Dawuda suka juya suka koma. Da suka iso sai suka faɗa wa Dawuda abin da Nabal ya ce.
And they turned round [the] young men of David to way their and they returned and they came and they told to him according to all the words these.
13 Dawuda ya ce wa mutanensa, “Kowa yă rataya takobinsa.” Sai duk suka yi haka. Dawuda kuma ya rataya nasa. Mutum wajen ɗari huɗu suka tafi tare da Dawuda, mutum ɗari biyu kuwa suka zauna suna gadin kayansu.
And he said David to men his gird on - everyone sword his and they girded on everyone sword his and he girded on also David sword his and they went up - after David about four hundred man and two hundred they remained with the baggage.
14 Ɗaya daga cikin bayin Nabal ya gaya wa Abigiyel matar Nabal cewa, “Dawuda ya aiko da bayinsa daga jeji su gai da maigida, amma maigida ya zazzage su.
And to Abigail [the] wife of Nabal he told a young man one from the young men saying there! he sent David messengers - from the wilderness to bless master our and he shouted at them.
15 Waɗannan mutane kuwa sun yi mana kirki ƙwarai, ba su ba mu wata wahala ba. Babu abu guda da ya ɓace mana dukan lokacin da muke tare da su.
And the men [were] good to us very and not we were humiliated and not we missed anything all [the] days [which] we went about with them when were we in the field.
16 Dare da rana sun zama mana katanga kewaya da mu, a duk tsawon lokacin da muke kiwon tumakinmu kusa da su.
A wall they were with us both night as well as by day all [the] days of being we with them shepherding the flock.
17 Ki yi nazari a kai, ki ga ko za ki iya yin wani abu, domin masifa yana nan rataye a wuyan maigidanmu da dukan iyalin gidansa. Shi mugun mutum ne wanda ba wani da zai iya yin masa magana.”
And now know and see what? will you do for it has been determined evil against master our and on all household his and he [is] a son of worthlessness from speaking to him.
18 Abigiyel ba tă ɓata lokaci ba. Ta ɗauki burodi guda ɗari biyu, da salkar ruwan inabi biyu da tumaki biyar da aka gyara, da soyayyen hatsi mudu biyar, da waina guda ɗari na’ya’yan inabi, da masa ɗari biyu na kauɗar ɓaure ta labta wa jakuna.
And she made haste (Abigail *Q(k)*) and she took two hundred bread[s] and two jars of wine and five sheep (prepared *Q(k)*) and five seahs of roasted grain and a hundred bunches of raisins and two hundred fig cakes and she put [them] on the donkeys.
19 Sai ta ce wa bawanta, “Yi gaba, zan bi ka”. Amma ba tă gaya wa Nabal, mijinta ba.
And she said to servants her pass on before me here I after you [will be] coming and to husband her Nabal not she told.
20 Da tana tafiya a kan jaki, ta kai gindin wani dutse ke nan, sai ga Dawuda da mutanensa suna gangarowa zuwa wajen da take. Sai ta tafi, ta sadu da su.
And it was she - [was] riding on the donkey and [was] going down in [the] cover of the mountain and there! David and men his [were] going down to meet her and she met them.
21 Bai daɗe ba da Dawuda ya ce a ransa, “Ashe, a banza ne na yi ta lura da dukan abin da yake na mutumin nan a jeji, har ba abinsa da ya ɓace. Ga shi, ya rama mini alheri da mugunta.
And David he had said surely to deception I have guarded all that [belongs] to this [man] in the wilderness and not it has been missing any of all that [belongs] to him anything and he has returned to me evil in place of good.
22 Bari Allah yă yi duk abin da ya ga dama da ni in na bar ko ɗaya daga mazan da suke da tare shi, gobe da safe.”
Thus may he do God to [the] enemies David and thus may he add if I will leave any of all that [belongs] to him until the morning [one who] urinates on a wall.
23 Da Abigiyel ta ga Dawuda, sai ta gaggauta ta sauka daga kan jaki, ta rusuna a gaban Dawuda da fuskarta har ƙasa.
And she saw Abigail David and she made haste and she came down from on the donkey and she fell to [the] face of David on face her and she bowed down [the] ground.
24 Ta fāɗi a ƙafafunsa ta ce, “Bari laifin yă zama nawa, ranka yă daɗe. Ina roƙonka ka bar baiwarka ta yi magana, ka ji abin da baiwarka za tă ce.
And she fell at feet his and she said [be] on me I O lord my the iniquity and let her speak please maidservant your in ears your and hear [the] words of maidservant your.
25 Kada ranka yă daɗe, yă kula da Nabal, mugun mutumin nan. Shi dai kamar sunansa ne, sunansa Wawa ne, kuma wawanci yana cikinsa. Amma ni baiwarka, ban ga mutanen da ranka yă daɗe ya aika ba.
May not please he set lord my - heart his to [the] man of worthlessness this on Nabal for like name his [is] so he [is] Nabal name his and disgraceful folly [is] with him and I maidservant your not I saw [the] young men of lord my whom you sent.
26 Da yake yanzu, ya mai girma, Ubangiji ya hana ka zubar da jini da kuma ɗaukan wa kanka fansa, muddin Ubangiji yana raye, kai kuma kana a raye, bari maƙiyinka da dukan waɗanda suke niyya su cuci shugabana su zama kamar Nabal.
And now O lord my [by] [the] life of Yahweh and [by] [the] life of self your that he has restrained you Yahweh from coming in blood and [from] delivering hand your you and now may they be like Nabal enemies your and those [who] seek against lord my evil.
27 Bari kuma ka karɓi wannan kyautar da baiwarka ta kawo don samarin da suke binka.
And now the blessing this which he has brought maidservant your to lord my and it will be given to the young men who go about at [the] feet of lord my.
28 Ina roƙonka ka gafarta wa baiwarka laifinta gama tabbatacce Ubangiji zai ba shugabana dawwammamiyar sarauta, gama kana yin yaƙin Ubangiji ne. Kuma ba wani mugun abin da zai same ka muddin kana a raye.
Forgive please to [the] transgression of maidservant your for certainly he will make Yahweh for lord my a house enduring for [the] battles of Yahweh lord my [is] fighting and evil not it will be found in you from days your.
29 Ko da yake wani mutum yana fafaranka domin yă kashe ka, Ubangiji Allahnka zai kiyaye ranka. Amma za a wurgar da rayukan maƙiyanka kamar yadda ake wurga dutsen majajjawa.
And he has arisen a man to pursue you and to seek life your and it will be [the] life of lord my bound up - in [the] bundle of the living with Yahweh God your and [the] life of enemies your he will sling out it in [the] midst of [the] hollow of sling.
30 Sa’ad da Ubangiji ya cika kowane alherinsa da ya yi wa shugabana alkawari, ya kuma keɓe shi sarki a bisa Isra’ila,
And it will be that he will do Yahweh to lord my according to all that he has spoken the good on you and he will appoint you to ruler over Israel.
31 kada yă zama cewa zuciyarka ta ba ka laifi ko ka damu cewa kana da alhakin jini, kada ka yi ramuwa da kanka. Sa’ad da Ubangiji ya nuna maka alheri, ka tuna da ni, baiwarka.”
And not it will become this - for you staggering and stumbling of heart for lord my and pouring out of blood without cause and to deliver lord my himself and he will do good Yahweh to lord my and you will remember maidservant your.
32 Dawuda ya ce wa Abigiyel, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya aiko ki don ki same ni yau.
And he said David to Abigail [be] blessed Yahweh [the] God of Israel who he has sent you the day this to meet me.
33 Bari Allah yă albarkace ki saboda hikima yanke hukuncinki da kuma hana ni zubar da jini da ɗauka wa kaina fansa da hannuna a wannan rana.
And [be] blessed discernment your and [be] blessed you who you have restrained me the day this from coming in blood and [from] delivering hand my me.
34 Ubangiji, ya hana ni in yi miki ɓarna. Da ba don kin zo kin sadu da ni ba, na rantse da Ubangiji, Allah na Isra’ila Mai Rai, babu ko ɗaya daga cikin mazan gidan Nabal da zai rage gobe da safe.”
And but [by] [the] life of Yahweh [the] God of Israel who he has restrained me from doing harm to you if - if not you had made haste (and you had come *Q(k)*) to meet me that except he has been left to Nabal until [the] light of the morning [one who] urinates on a wall.
35 Sa’an nan Dawuda ya karɓi abin da ta kawo masa daga hannunta, ya kuma ce mata, “Ki koma gida kada ki damu, na ji koke-kokenki, zan kuma biya miki bukatarki.”
And he took David from hand her [that] which she had brought to him and to her he said go up to peace to house your see I have listened to voice your and I have lifted up face your.
36 Da Abigiyel ta kai gida sai ta sami Nabal cikin gida yana ta fama biki iri na sarakuna. Yana ji wa ransa daɗi, ya kuma bugu tilis, saboda haka ba tă ce masa kome ba sai da gari ya waye.
And she went Abigail - to Nabal and there! [belonged] to him a feast in house his like [the] feast of king and [the] heart of Nabal it was good on him and he [was] drunk up to muchness and not she told to him anything small and great until [the] light of the morning.
37 Da safe sa’ad da Nabal ya natsu, sai matarsa ta gaya masa dukan abin da ya faru. Sai zuciyarsa ta tsinke, ya zama kamar dutse.
And it was in the morning when had gone out the wine from Nabal and she told to him wife his the things these and it died heart his in inward part[s] his and he he became stone.
38 Bayan kusan kwana goma, Ubangiji ya bugi Nabal, sai ya mutu.
And it was about [the] ten the days and he struck Yahweh Nabal and he died.
39 Da Dawuda ya sami labarin mutuwar Nabal, sai ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya sāka mini a kan irin renin da Nabal ya yi mini. Ya hana bawansa yin mugunta, ga shi ya ɗora wa Nabal muguntar da ya yi.” Sai Dawuda ya aika wa Abigiyel cewa tă zama matarsa.
And he heard David that he had died Nabal and he said [be] blessed Yahweh who he has conducted [the] case of disgrace my from [the] hand of Nabal and servant his he has restrained from evil and [the] evil of Nabal he has turned back Yahweh on own head his and he sent David and he spoke with Abigail to take her for himself to a wife.
40 Bayin Dawuda suka tafi Karmel suka ce wa Abigiyel, “Dawuda ya aike mu gare ki, mu zo mu ɗauke ki ki zama matarsa.”
And they went [the] servants of David to Abigail Carmel towards and they spoke to her saying David he has sent us to you to take you for himself to a wife.
41 Sai ta rusuna da fuskarta har ƙasa ta ce, “Ni baranyarka ce, na shirya in bauta maka in kuma wanke ƙafafun bayin shugabana.”
And she arose and she bowed down face [the] ground towards and she said here! maidservant your to a maid to wash [the] feet of [the] servants of lord my.
42 Abigiyel ta tashi da sauri ta hau jaki, ta kuma sa’yan mata biyar da suke mata hidima su bi ta, suka tafi tare da’yan saƙon Dawuda. Ta kuwa zama matarsa.
And she made haste and she arose Abigail and she rode on the donkey and five maids her who walked to foot her and she went after [the] messengers of David and she became of him a wife.
43 Dawuda a lokacin ya riga ya auri Ahinowam daga Yezireyel, dukansu suka zama matansa.
And Ahinoam he had taken David from Jezreel and they became also both of them of him wives.
44 Amma Shawulu ya aurar da Mikal,’yarsa, matar Dawuda, ga Falti ɗan Layish wanda yake daga Gallim.
And Saul he had given Michal daughter his [the] wife of David to Palti [the] son of Laish who [was] from Gallim.