< 1 Sama’ila 25 >

1 Sama’ila ya rasu, sai dukan Isra’ila suka taru suka yi makoki saboda shi. Suka binne shi a gidansa a Rama. Sai Dawuda ya gangara zuwa cikin Jejin Faran.
Og Samuel døde, og al Israel samlede sig og sørgede over ham, og de begrove ham i hans Hjem udi Rama, og David gjorde sig rede og drog ned til Ørken i Paran.
2 A Mawon, akwai wani mutum wanda yake da dukiya a Karmel, mutumin mai arziki ne ƙwarai. Yana da awaki dubu ɗaya, da tumaki dubu uku waɗanda yake wa aski a Karmel.
Og der var en Mand i Maon, og han havde sin Bedrift paa Karmel, og samme Mand var meget rig, og han havde tre Tusinde Faar og Tusinde Geder; og han klippede netop sine Faar ved Karmel.
3 Ana ce da shi Nabal, sunan matarsa kuwa Abigiyel. Tana da hikima ga ta kuma kyakkyawa, amma mijinta mai rowa ne marar mutunci. Shi daga kabilar Kaleb ne.
Og Mandens Navn var Nabal, og hans Hustrus Navn Abigail; og Kvinden var af god Forstand og dejlig af Skikkelse, men Manden var haard og ond i sine Gerninger; og han var en Kalebiter.
4 Lokacin da Dawuda yake a jeji, ya ji labari cewa Nabal yana askin tumaki.
Men David hørte i Ørken, at Nabal klippede sine Faar.
5 Sai ya zaɓi samari goma ya aike su wurin Nabal a Karmel su gaishe shi a madadinsa,
Da udsendte David ti unge Karle, og David sagde til de unge Karle: Gaar op til Karmel, og naar I komme til Nabal, da hilser ham i mit Navn.
6 su ce masa, “Ranka yă daɗe, ina maka fatan alheri, kai da gidanka da dukan abin da kake da shi!
Og siger saaledes: Til Lykke! Fred være med dig og Fred være med dit Hus og Fred være med alt det, du har!
7 “Na ji cewa, yanzu lokacin askin tumaki ne. Sa’ad da makiyayanka suke tare da mu, ba mu cuce su ba, kuma duk zamansu a Karmel ba abin da yake nasu da ya ɓata.
Og nu har jeg hørt, at du har Faareklipning; nu! de Hyrder, som du har, have været sammen med os, vi have ikke forhaanet dem, og de savnede intet alle de Dage, de vare i Karmel.
8 Ka tambayi bayinka za su kuwa gaya maka. Saboda haka ka yi wa mutanena kirki, gama yau ranar biki ce. Ina roƙonka ka ba wa samarina, wato, bayinka, da ni ɗanka Dawuda, duk abin da kake iya ba su.”
Spørg dine unge Karle, og de skulle kundgøre dig det, og lad vore unge Karle finde Naade for dine Øjne, thi vi ere komne paa en god Dag; kære, giv dine Tjenere og din Søn David, hvad din Haand formaar.
9 Da mutanen Dawuda suka isa wurin Nabal, suka ba wa Nabal wannan saƙo a sunan Dawuda, sai suka jira.
Og Davids unge Karle kom og talede til Nabal efter alle disse Ord i Davids Navn, og de holdt sig rolige.
10 Nabal ya ce wa mutanen Dawuda, “Wane ne wannan Dawuda? Wane ne wannan ɗan Yesse? Yawancin bayi suna tayar wa iyayengijinsu a kwanakin nan.
Og Nabal svarede Davids Tjenere og sagde: Hvo er David? og hvo er Isais Søn? der ere nu om Stunder mange Tjenere, som løbe bort fra deres Herres Ansigt.
11 Don me zan ɗauki burodina da ruwana, da kuma naman da na yanka saboda masu yin wa tumakina aski in ba mutanen da ban ma san inda suka fito ba?”
Og skulde jeg tage mit Brød og Vand og mit Slagtekvæg, som jeg har slagtet til dem, som klippe for mig, og give de Mænd, om hvem jeg ikke ved, hvorfra de ere?
12 Mutanen Dawuda suka juya suka koma. Da suka iso sai suka faɗa wa Dawuda abin da Nabal ya ce.
Da vendte Davids unge Karle sig for at gaa deres Vej, de vendte tilbage og kom og forkyndte ham alle disse Ord.
13 Dawuda ya ce wa mutanensa, “Kowa yă rataya takobinsa.” Sai duk suka yi haka. Dawuda kuma ya rataya nasa. Mutum wajen ɗari huɗu suka tafi tare da Dawuda, mutum ɗari biyu kuwa suka zauna suna gadin kayansu.
Da sagde David til sine Mænd: Ombinder hver sit Sværd; og de ombandt hver sit Sværd, og David ombandt ogsaa sit Sværd, og der droge op efter David ved fire Hundrede Mand, men to Hundrede bleve ved Tøjet.
14 Ɗaya daga cikin bayin Nabal ya gaya wa Abigiyel matar Nabal cewa, “Dawuda ya aiko da bayinsa daga jeji su gai da maigida, amma maigida ya zazzage su.
Og en af de unge Karle gav Abigail, Nabals Hustru, det til Kende og sagde: Se, David sendte Bud fra Ørken, at velsigne vor Herre, men han foer løs paa dem.
15 Waɗannan mutane kuwa sun yi mana kirki ƙwarai, ba su ba mu wata wahala ba. Babu abu guda da ya ɓace mana dukan lokacin da muke tare da su.
Og de Mænd have været os saare gode, og vi bleve ikke forhaanede, og vi savnede ikke noget alle de Dage, vi vandrede hos dem, naar vi vare paa Marken.
16 Dare da rana sun zama mana katanga kewaya da mu, a duk tsawon lokacin da muke kiwon tumakinmu kusa da su.
De have været en Mur for os baade Nat og Dag alle de Dage, vi vare hos dem og vogtede Faarene.
17 Ki yi nazari a kai, ki ga ko za ki iya yin wani abu, domin masifa yana nan rataye a wuyan maigidanmu da dukan iyalin gidansa. Shi mugun mutum ne wanda ba wani da zai iya yin masa magana.”
Saa vid nu og se, hvad du vil gøre, thi en Ulykke er fast besluttet over vor Herre og over alt hans Hus; og han er et Belials Barn, saa at man ikke kan tale til ham.
18 Abigiyel ba tă ɓata lokaci ba. Ta ɗauki burodi guda ɗari biyu, da salkar ruwan inabi biyu da tumaki biyar da aka gyara, da soyayyen hatsi mudu biyar, da waina guda ɗari na’ya’yan inabi, da masa ɗari biyu na kauɗar ɓaure ta labta wa jakuna.
Da skyndte Abigail sig og tog to Hundrede Brød og to Flasker Vin og fem tillavede Faar og fem Maal ristede Aks og hundrede Klaser Rosiner og to Hundrede Klumper Figen, og hun lagde det paa Asener.
19 Sai ta ce wa bawanta, “Yi gaba, zan bi ka”. Amma ba tă gaya wa Nabal, mijinta ba.
Og hun sagde til sine Drenge: Gaar foran mig, se, jeg kommer efter eder; men hun gav ikke Nabal sin Mand det til Kende.
20 Da tana tafiya a kan jaki, ta kai gindin wani dutse ke nan, sai ga Dawuda da mutanensa suna gangarowa zuwa wajen da take. Sai ta tafi, ta sadu da su.
Og det skete, der hun red paa Asenet og drog ned i Skjul af Bjerget, se, da drog David og hans Mænd ned imod hende, og hun mødte dem.
21 Bai daɗe ba da Dawuda ya ce a ransa, “Ashe, a banza ne na yi ta lura da dukan abin da yake na mutumin nan a jeji, har ba abinsa da ya ɓace. Ga shi, ya rama mini alheri da mugunta.
Men David havde sagt: Visseligen, jeg har forgæves bevaret alt det, denne havde i Ørken, og der savnedes ikke noget af alt det, som han havde; men han betalte mig ondt for godt.
22 Bari Allah yă yi duk abin da ya ga dama da ni in na bar ko ɗaya daga mazan da suke da tare shi, gobe da safe.”
Gud gøre ved Davids Fjender nu og fremdeles saa og saa, om jeg skal lade overblive af alt det, han har, indtil Morgen, det bliver lyst, nogen af Mandkøn!
23 Da Abigiyel ta ga Dawuda, sai ta gaggauta ta sauka daga kan jaki, ta rusuna a gaban Dawuda da fuskarta har ƙasa.
Der Abigail saa David, da skyndte hun sig og steg ned af Asenet, og hun faldt ned paa sit Ansigt for Davids Ansigt og nedbøjede sig paa Jorden.
24 Ta fāɗi a ƙafafunsa ta ce, “Bari laifin yă zama nawa, ranka yă daɗe. Ina roƙonka ka bar baiwarka ta yi magana, ka ji abin da baiwarka za tă ce.
Og hun faldt ned for hans Fødder og sagde: Hør mig, min Herre! denne Misgerning skal være min; Kære, lad din Tjenerinde tale for dine Øren og hør din Tjenerindes Ord.
25 Kada ranka yă daɗe, yă kula da Nabal, mugun mutumin nan. Shi dai kamar sunansa ne, sunansa Wawa ne, kuma wawanci yana cikinsa. Amma ni baiwarka, ban ga mutanen da ranka yă daɗe ya aika ba.
Min Herre vende ikke sit Hjerte imod denne Belials Mand, imod Nabal, thi som hans Navn er, saa er han: Nabal er hans Navn, og Daarlighed er hos ham; men jeg, din Tjenerinde, saa ikke min Herres unge Karle, som du havde udsendt.
26 Da yake yanzu, ya mai girma, Ubangiji ya hana ka zubar da jini da kuma ɗaukan wa kanka fansa, muddin Ubangiji yana raye, kai kuma kana a raye, bari maƙiyinka da dukan waɗanda suke niyya su cuci shugabana su zama kamar Nabal.
Og nu, min Herre, saa vist som Herren lever, og saa vist som din Sjæl lever, da har Herren forhindret dig i at udøse Blod og i at tage dig selv til Rette, saa skulle nu dine Fjender og de, som søge min Herres Ulykke, vorde som Nabal.
27 Bari kuma ka karɓi wannan kyautar da baiwarka ta kawo don samarin da suke binka.
Og her er nu denne Foræring, som din Tjenerinde førte til min Herre, og lad den gives de unge Karle, som følge min Herre.
28 Ina roƙonka ka gafarta wa baiwarka laifinta gama tabbatacce Ubangiji zai ba shugabana dawwammamiyar sarauta, gama kana yin yaƙin Ubangiji ne. Kuma ba wani mugun abin da zai same ka muddin kana a raye.
Kære, forlad din Tjenerindes Overtrædelse; thi Herren skal berede min Herre et bestandigt Hus; thi min Herre fører Herrens Krige, og intet ondt skal times dig i dine Dage.
29 Ko da yake wani mutum yana fafaranka domin yă kashe ka, Ubangiji Allahnka zai kiyaye ranka. Amma za a wurgar da rayukan maƙiyanka kamar yadda ake wurga dutsen majajjawa.
Naar noget Menneske rejser sig til at forfølge dig og til at søge efter dit Liv: Saa skal min Herres Sjæl være bunden i de levendes Knippe hos Herren din Gud; men dine Fjenders Sjæl, den skal han udslynge ud af Slyngen.
30 Sa’ad da Ubangiji ya cika kowane alherinsa da ya yi wa shugabana alkawari, ya kuma keɓe shi sarki a bisa Isra’ila,
Og det skal ske, naar Herren gør min Herre efter alt det gode, som han har talet over dig, og sætter dig til en Fyrste over al Israel,
31 kada yă zama cewa zuciyarka ta ba ka laifi ko ka damu cewa kana da alhakin jini, kada ka yi ramuwa da kanka. Sa’ad da Ubangiji ya nuna maka alheri, ka tuna da ni, baiwarka.”
da skal dette ikke være dig til Selvbebrejdelse eller min Herres Hjerte til Anstød, at han har udøst uskyldigt Blod, og at min Herre har taget sig selv til Rette; og naar Herren gør vel imod min Herre, da skal du komme din Tjenerinde i Hu.
32 Dawuda ya ce wa Abigiyel, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya aiko ki don ki same ni yau.
Da sagde David til Abigail: Lovet være Herren, Israels Gud, som sendte dig mig i Møde i Dag,
33 Bari Allah yă albarkace ki saboda hikima yanke hukuncinki da kuma hana ni zubar da jini da ɗauka wa kaina fansa da hannuna a wannan rana.
og velsignet være din Fornuftighed, og velsignet være du, som forhindrede mig paa denne Dag fra at udøse Blod og fra at tage mig selv til Rette!
34 Ubangiji, ya hana ni in yi miki ɓarna. Da ba don kin zo kin sadu da ni ba, na rantse da Ubangiji, Allah na Isra’ila Mai Rai, babu ko ɗaya daga cikin mazan gidan Nabal da zai rage gobe da safe.”
Og sandelig, saa vist som Herren, Israels Gud, lever, som forhindrede mig i at gøre dig ondt: Om du ikke havde skyndt dig og var kommen mig i Møde, da havde Nabal ikke beholdt tilovers indtil Morgen, naar det bliver lyst, nogen af Mandkøn.
35 Sa’an nan Dawuda ya karɓi abin da ta kawo masa daga hannunta, ya kuma ce mata, “Ki koma gida kada ki damu, na ji koke-kokenki, zan kuma biya miki bukatarki.”
Saa tog David af hendes Haand det, som hun førte til ham, og han sagde til hende: Drag med Fred op til dit Hus, se, jeg adlød din Røst og ansaa din Person.
36 Da Abigiyel ta kai gida sai ta sami Nabal cikin gida yana ta fama biki iri na sarakuna. Yana ji wa ransa daɗi, ya kuma bugu tilis, saboda haka ba tă ce masa kome ba sai da gari ya waye.
Og Abigail kom til Nabal, og se, han havde et Gæstebud i sit Hus, som en Konges Gæstebud, og Nabals Hjerte var vel til Mode, og han var saare drukken; men hun kundgjorde ham ikke noget, hverken lidet eller stort, før det blev lyst om Morgenen.
37 Da safe sa’ad da Nabal ya natsu, sai matarsa ta gaya masa dukan abin da ya faru. Sai zuciyarsa ta tsinke, ya zama kamar dutse.
Og det skete om Morgenen, da Nabals Rus var forbi, da kundgjorde hans Hustru ham disse Ting; og hans Hjerte døde i ham, og han blev som en Sten.
38 Bayan kusan kwana goma, Ubangiji ya bugi Nabal, sai ya mutu.
Og det skete ved ti Dage derefter, da slog Herren Nabal, og han døde.
39 Da Dawuda ya sami labarin mutuwar Nabal, sai ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya sāka mini a kan irin renin da Nabal ya yi mini. Ya hana bawansa yin mugunta, ga shi ya ɗora wa Nabal muguntar da ya yi.” Sai Dawuda ya aika wa Abigiyel cewa tă zama matarsa.
Og der David hørte, at Nabal var død, da sagde han: Lovet være Herren, som udførte min Forsmædelses Sag imod Nabal og forhindrede sin Tjener fra ondt, og Herren lod Nabals Ondskab falde tilbage paa hans Hoved; og David sendte hen og lod tale med Abigail om at tage sig hende til Hustru.
40 Bayin Dawuda suka tafi Karmel suka ce wa Abigiyel, “Dawuda ya aike mu gare ki, mu zo mu ɗauke ki ki zama matarsa.”
Og der Davids Tjenere kom til Abigail ved Karmel, da talede de til hende og sagde: David sendte os til dig for at tage dig til sin Hustru.
41 Sai ta rusuna da fuskarta har ƙasa ta ce, “Ni baranyarka ce, na shirya in bauta maka in kuma wanke ƙafafun bayin shugabana.”
Og hun stod op og bøjede sig med sit Ansigt til Jorden, og sagde: Se, her er din Tjenerinde til en Tjenestekvinde til at to min Herres Tjeneres Fødder.
42 Abigiyel ta tashi da sauri ta hau jaki, ta kuma sa’yan mata biyar da suke mata hidima su bi ta, suka tafi tare da’yan saƙon Dawuda. Ta kuwa zama matarsa.
Og Abigail skyndte sig og gjorde sig rede og red paa et Asen med fem af hendes Piger, og hun drog efter Davids Bud og blev hans Hustru.
43 Dawuda a lokacin ya riga ya auri Ahinowam daga Yezireyel, dukansu suka zama matansa.
David tog og Ahinoam at Jisreel; og de bleve ogsaa begge hans Hustruer.
44 Amma Shawulu ya aurar da Mikal,’yarsa, matar Dawuda, ga Falti ɗan Layish wanda yake daga Gallim.
Men Saul havde givet Mikal sin Datter, Davids Hustru, til Palti, Lais Søn, som var fra Gallim.

< 1 Sama’ila 25 >