< 1 Sama’ila 24 >

1 Bayan da Shawulu ya komo daga fafaran Filistiyawa, sai aka gaya masa cewa, “Dawuda yana can a Jejin En Gedi.”
Saul Filistliler'i kovalamaktan dönünce, Davut'un Eyn-Gedi Çölü'nde olduğu haberini aldı.
2 Saboda haka Shawulu ya zaɓi mutum dubu uku daga cikin dukan Isra’ila, suka fita neman Dawuda da mutanensa kusa da Duwatsun Awakin Jeji.
Saul da Davut'la adamlarını Dağ Keçisi Kayalığı dolaylarında arayıp bulmak için, bütün İsrail'den üç bin seçme asker alıp yola çıktı.
3 Da Shawulu ya isa inda ake ajiye garken tumaki a bakin hanya inda akwai kogo, sai ya shiga ciki kogon don yă yi bayan gari. Dawuda da mutanensa kuwa suna can zaune a ƙurewar kogon.
Yolda koyun ağıllarına rastladı. Yakında bir de mağara vardı. Saul ihtiyacını gidermek için mağaraya girdi. Davut'la adamları mağaranın en iç bölümünde kalıyorlardı.
4 Mutanen Dawuda suka ce, wannan rana ce Ubangiji ya yi magana ya ce maka, “Zan ba da maƙiyinka a hannunka domin ka yi abin da ka ga dama da shi.” Sai Dawuda ya tashi a hankali ya je ya yanke shafin rigar Shawulu.
Adamları, Davut'a, “İşte RAB'bin sana, ‘Dilediğini yapabilmen için düşmanını eline teslim edeceğim’ dediği gün bugündür” dediler. Davut kalkıp Saul'un cüppesinin eteğinden gizlice bir parça kesti.
5 Daga baya Dawuda ya damu domin ya yanke shafin rigar Shawulu.
Ama sonradan Saul'un eteğinden bir parça kestiği için kendini suçlu buldu.
6 Ya ce wa mutanensa, “Ubangiji yă sawwaƙe in yi abu haka ga shugabana da Ubangiji ya shafe, ko in ɗaga hannuna in kashe shi, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.”
Adamlarına, “Efendime, RAB'bin meshettiği kişiye karşı böyle bir şey yapmaktan, el kaldırmaktan RAB beni uzak tutsun” dedi, “Çünkü o RAB'bin meshettiği kişidir.”
7 Da wannan magana Dawuda ya kwaɓi mutanensa, bai yarda su fāɗa wa Shawulu ba. Shawulu kuwa ya bar kogon ya yi tafiyarsa.
Davut bu sözlerle adamlarını engelledi ve Saul'a saldırmalarına izin vermedi. Saul mağaradan çıkıp yoluna koyuldu.
8 Daga baya Dawuda ya fita daga kogon sai ya kira Shawulu ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki!” Da Shawulu ya waiwaya, sai Dawuda ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
O zaman Davut da mağaradan çıktı. Saul'a, “Efendim kral!” diye seslendi. Saul arkasına bakınca, Davut eğilip yüzüstü yere kapandı.
9 Ya ce wa Shawulu, “Me ya sa kake saurari mutanen da suke cewa, ‘Dawuda ya dāge yă cuce ka’?
“‘Davut sana kötülük yapmak istiyor’ diyenlerin sözlerini neden önemsiyorsun?” dedi,
10 Yau ka ga da idonka yadda Ubangiji ya bashe ka a hannuna a cikin kogon nan. Waɗansu sun ce mini in kashe ka, amma na bar ka, na ce, ‘Ba zan sa hannuna a kan shugabana ba, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.’
“Bugün RAB'bin mağarada seni elime nasıl teslim ettiğini gözünle görüyorsun. Bazıları seni öldürmemi istedi. Ama ben seni esirgeyip, ‘Efendime el kaldırmayacağım, çünkü o RAB'bin meshettiği kişidir’ dedim.
11 Babana, duba, ga shafin rigarka a hannuna, na yanke shafin rigarka amma ban kashe ka ba. Yanzu ka gane ka kuma sani cewa ba ni da laifin aikata kome ko tayarwa, ban yi maka laifi ba, amma kana farautar raina.
Ey baba, cüppenin eteğinden kesilmiş, elimdeki şu parçaya bak; evet, bak! Cüppenden bir parça kestim, ama seni öldürmedim. Bundan ötürü içimde kötülük ve başkaldırma düşüncesi olmadığını iyice bilesin. Sana kötülük yapmadığım halde sen beni öldürmeye çalışıyorsun.
12 Ubangiji zai shari’anta tsakanina da kai. Ubangiji zai sāka mini laifin da ka yi mini, amma ni kam ba zan taɓa ka ba.
RAB aramızda yargıç olsun ve benim öcümü senden O alsın. Ama ben elimi sana karşı kaldırmayacağım.
13 Kamar yadda karin maganan nan na dā ya ce, ‘Daga cikin masu mugunta, mugunta ke fitowa,’ hannuna dai ba zai taɓa ka ba.
Eskilerin şu, ‘Kötülük kötü kişilerden gelir’ deyişi uyarınca elim sana karşı kalkmayacaktır.
14 “Wane ne sarkin Isra’ila, ka fito kake bi? Wa kake kora? Kana bin mataccen kare ko kuɗin cizo?
İsrail Kralı kime karşı çıkmış? Sen kimi kovalıyorsun? Ölü bir köpek mi? Bir pire mi?
15 Ubangiji yă zama alƙali, yă yi shari’a tsakanina da kai, bari Ubangiji yă duba, yă tsaya mini, yă nuna ba ni da laifi.”
RAB yargıç olsun ve hangimizin haklı olduğuna O karar versin. RAB davama baksın ve beni savunup senin elinden kurtarsın.”
16 Da Dawuda ya gama wannan magana, sai Shawulu ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Sai ya fasa da kuka.
Davut söylediklerini bitirince, Saul, “Davut oğlum, bu senin sesin mi?” diye sordu ve hıçkıra hıçkıra ağlamaya başladı.
17 Ya ce, “Ka fi ni gaskiya, ka yi mini alheri, ni kuwa na yi maka mugunta.
Sonra, “Sen benden daha doğru bir adamsın” dedi, “Sana kötülük yaptığım halde sen bana iyilikle karşılık verdin.
18 Ga shi yanzu ka faɗa mini alherin da ka yi mini. Ubangiji ya bashe ni a hannunka amma ba ka kashe ni ba.
Bugün bana iyi davrandığını kanıtladın: RAB beni eline teslim ettiği halde beni öldürmedin.
19 In mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi yă tafi lafiya ba tare da yin masa rauni ba? Ubangiji yă sāka maka, gama ka nuna mini alheri a yau.
Düşmanını yakalayan biri onu güvenlik içinde salıverir mi? Bugün bana yaptığın iyiliğe karşılık RAB de seni iyilikle ödüllendirsin.
20 Na sani tabbatacce za ka zama sarki. Masarautar Isra’ila za tă kahu a hannunka.
Şimdi anladım ki, sen gerçekten kral olacaksın ve İsrail Krallığı senin egemenliğin altında sürecek.
21 Yanzu ka rantse mini da Ubangiji cewa ba za ka hallaka zuriyarta ko ka share sunana daga iyalin mahaifina ba.”
Benden sonra soyumu ortadan kaldırmayacağına, babamın ailesinden adımı silmeyeceğine dair RAB'bin önünde ant iç.”
22 Sai Dawuda ya rantse wa Shawulu. Sa’an nan Shawulu ya koma gida, amma Dawuda da mutanensa suka haura zuwa wurin ɓuya.
Davut Saul'un istediği gibi ant içti. Sonra Saul evine döndü. Davut'la adamları da sığınağa gittiler.

< 1 Sama’ila 24 >