< 1 Sama’ila 24 >
1 Bayan da Shawulu ya komo daga fafaran Filistiyawa, sai aka gaya masa cewa, “Dawuda yana can a Jejin En Gedi.”
Da Saul kom tilbake efterat han hadde forfulgt filistrene, fikk han spurt at David var i En-Gedis ørken.
2 Saboda haka Shawulu ya zaɓi mutum dubu uku daga cikin dukan Isra’ila, suka fita neman Dawuda da mutanensa kusa da Duwatsun Awakin Jeji.
Da tok Saul tre tusen mann, som han hadde valgt ut blandt hele Israel, og drog avsted for å lete efter David og hans menn på Stenbukk-klippene.
3 Da Shawulu ya isa inda ake ajiye garken tumaki a bakin hanya inda akwai kogo, sai ya shiga ciki kogon don yă yi bayan gari. Dawuda da mutanensa kuwa suna can zaune a ƙurewar kogon.
Han kom da til fårehegnene ved veien; der var en hule, og Saul gikk der inn i sine egne ærender; men David og hans menn satt innerst inne i hulen.
4 Mutanen Dawuda suka ce, wannan rana ce Ubangiji ya yi magana ya ce maka, “Zan ba da maƙiyinka a hannunka domin ka yi abin da ka ga dama da shi.” Sai Dawuda ya tashi a hankali ya je ya yanke shafin rigar Shawulu.
Da sa Davids menn til ham: Se, nu er den dag kommet om hvilken Herren sa til dig: Nu gir jeg din fiende i din hånd, så du kan gjøre med ham som du finner for godt! Så stod David op og skar hemmelig fliken av Sauls kappe.
5 Daga baya Dawuda ya damu domin ya yanke shafin rigar Shawulu.
Men derefter slo samvittigheten David, fordi han hadde skåret av fliken på Sauls kappe.
6 Ya ce wa mutanensa, “Ubangiji yă sawwaƙe in yi abu haka ga shugabana da Ubangiji ya shafe, ko in ɗaga hannuna in kashe shi, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.”
Og han sa til sine menn: Herren fri mig fra å gjøre slikt mot min herre, mot Herrens salvede, og legge hånd på ham! For Herrens salvede er han.
7 Da wannan magana Dawuda ya kwaɓi mutanensa, bai yarda su fāɗa wa Shawulu ba. Shawulu kuwa ya bar kogon ya yi tafiyarsa.
Og David irettesatte sine menn med hårde ord og lot dem ikke få lov til å overfalle Saul. Men Saul gikk ut av hulen og gav sig på veien.
8 Daga baya Dawuda ya fita daga kogon sai ya kira Shawulu ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki!” Da Shawulu ya waiwaya, sai Dawuda ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
Derefter stod David op og gikk ut av hulen og ropte efter Saul: Herre konge! Da så Saul sig tilbake, og David bøide sig med ansiktet mot jorden og kastet sig ned.
9 Ya ce wa Shawulu, “Me ya sa kake saurari mutanen da suke cewa, ‘Dawuda ya dāge yă cuce ka’?
Og David sa til Saul: Hvorfor hører du på folk som sier: David søker din ulykke?
10 Yau ka ga da idonka yadda Ubangiji ya bashe ka a hannuna a cikin kogon nan. Waɗansu sun ce mini in kashe ka, amma na bar ka, na ce, ‘Ba zan sa hannuna a kan shugabana ba, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.’
Idag har du jo med egne øine sett at Herren idag hadde gitt dig i min hånd i hulen, og det var tale om å drepe dig, men jeg hadde medynk med dig og sa: Jeg vil ikke legge hånd på min herre; for Herrens salvede er han.
11 Babana, duba, ga shafin rigarka a hannuna, na yanke shafin rigarka amma ban kashe ka ba. Yanzu ka gane ka kuma sani cewa ba ni da laifin aikata kome ko tayarwa, ban yi maka laifi ba, amma kana farautar raina.
Men se, min far, se, her er fliken av din kappe i min hånd! For når jeg skar fliken av din kappe og ikke drepte dig, så kan du vel skjønne og se at jeg ikke har hatt noget ondt eller nogen misgjerning i sinne og ikke har forsyndet mig mot dig, enda du efterstreber mig og vil ta mitt liv.
12 Ubangiji zai shari’anta tsakanina da kai. Ubangiji zai sāka mini laifin da ka yi mini, amma ni kam ba zan taɓa ka ba.
Herren skal dømme mellem mig og dig, og Herren skal hevne mig på dig, men min hånd skal ikke ramme dig;
13 Kamar yadda karin maganan nan na dā ya ce, ‘Daga cikin masu mugunta, mugunta ke fitowa,’ hannuna dai ba zai taɓa ka ba.
det er som det gamle ordsprog sier: Fra ugudelige kommer ugudelighet. Men min hånd skal ikke ramme dig.
14 “Wane ne sarkin Isra’ila, ka fito kake bi? Wa kake kora? Kana bin mataccen kare ko kuɗin cizo?
Hvem er det Israels konge har draget ut efter? Hvem er det du forfølger? En død hund, en loppe.
15 Ubangiji yă zama alƙali, yă yi shari’a tsakanina da kai, bari Ubangiji yă duba, yă tsaya mini, yă nuna ba ni da laifi.”
Så skal da Herren være dommer og dømme mellem mig og dig; han se til og føre min sak og dømme mig fri av din hånd!
16 Da Dawuda ya gama wannan magana, sai Shawulu ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Sai ya fasa da kuka.
Da nu David hadde talt disse ord til Saul, da sa Saul: Er det du som taler, min sønn David? Og Saul brast i gråt.
17 Ya ce, “Ka fi ni gaskiya, ka yi mini alheri, ni kuwa na yi maka mugunta.
Og han sa til David: Du er rettferdigere enn jeg; for du har gjort godt mot mig, men jeg har gjort ondt mot dig.
18 Ga shi yanzu ka faɗa mini alherin da ka yi mini. Ubangiji ya bashe ni a hannunka amma ba ka kashe ni ba.
Du har idag vist mig hvor god du har vært mot mig, idet du ikke drepte mig da Herren hadde gitt mig i din hånd.
19 In mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi yă tafi lafiya ba tare da yin masa rauni ba? Ubangiji yă sāka maka, gama ka nuna mini alheri a yau.
Når en mann treffer på sin fiende, lar han ham da gå sin vei i fred? Herren lønne dig for denne dag - for det du har gjort mot mig!
20 Na sani tabbatacce za ka zama sarki. Masarautar Isra’ila za tă kahu a hannunka.
Jeg vet jo alt at du skal bli konge, og at kongedømmet over Israel skal bli fast i din hånd.
21 Yanzu ka rantse mini da Ubangiji cewa ba za ka hallaka zuriyarta ko ka share sunana daga iyalin mahaifina ba.”
Så tilsverg mig da nu ved Herren at du ikke vil utrydde mine efterkommere og ikke utslette mitt navn av min fars hus!
22 Sai Dawuda ya rantse wa Shawulu. Sa’an nan Shawulu ya koma gida, amma Dawuda da mutanensa suka haura zuwa wurin ɓuya.
Og David tilsvor Saul det; og Saul drog hjem; men David og hans menn steg op til fjellborgen.