< 1 Sama’ila 24 >

1 Bayan da Shawulu ya komo daga fafaran Filistiyawa, sai aka gaya masa cewa, “Dawuda yana can a Jejin En Gedi.”
Et quand Saül fut revenu de la poursuite des Philistins, on lui fit ce rapport, disant: Voilà David au désert de Hen-guédi.
2 Saboda haka Shawulu ya zaɓi mutum dubu uku daga cikin dukan Isra’ila, suka fita neman Dawuda da mutanensa kusa da Duwatsun Awakin Jeji.
Alors Saül prit trois mille hommes d'élite de tout Israël, et il s'en alla chercher David et ses gens, jusques sur le haut des rochers des chamois.
3 Da Shawulu ya isa inda ake ajiye garken tumaki a bakin hanya inda akwai kogo, sai ya shiga ciki kogon don yă yi bayan gari. Dawuda da mutanensa kuwa suna can zaune a ƙurewar kogon.
Et Saül vint aux parcs des brebis auprès du chemin, où il y avait une caverne en laquelle il entra pour ses nécessités; et David et ses gens se tenaient au fond de la caverne.
4 Mutanen Dawuda suka ce, wannan rana ce Ubangiji ya yi magana ya ce maka, “Zan ba da maƙiyinka a hannunka domin ka yi abin da ka ga dama da shi.” Sai Dawuda ya tashi a hankali ya je ya yanke shafin rigar Shawulu.
Et les gens de David lui dirent: Voici le jour dont l'Eternel t'a dit: Voici, je te livre ton ennemi entre tes mains, afin que tu lui fasses selon qu'il te semblera bon. Et David se leva, et coupa tout doucement le pan du manteau de Saül.
5 Daga baya Dawuda ya damu domin ya yanke shafin rigar Shawulu.
Après cela David fut touché en son cœur de ce qu'il avait coupé le pan [du manteau] de Saül.
6 Ya ce wa mutanensa, “Ubangiji yă sawwaƙe in yi abu haka ga shugabana da Ubangiji ya shafe, ko in ɗaga hannuna in kashe shi, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.”
Et il dit à ses gens: Que l'Eternel me garde de commettre une telle action contre mon Seigneur, l'Oint de l'Eternel, en mettant ma main sur lui; car il est l'Oint de l'Eternel.
7 Da wannan magana Dawuda ya kwaɓi mutanensa, bai yarda su fāɗa wa Shawulu ba. Shawulu kuwa ya bar kogon ya yi tafiyarsa.
Ainsi David détourna ses gens par ses paroles, et il ne leur permit point de s'élever contre Saül. Puis Saül se leva de la caverne, et s'en alla son chemin.
8 Daga baya Dawuda ya fita daga kogon sai ya kira Shawulu ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki!” Da Shawulu ya waiwaya, sai Dawuda ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
Après cela David se leva, et sortit de la caverne, et cria après Saül, en disant: Mon Seigneur le Roi! et Saül regarda derrière lui, et David s'inclina le visage contre terre, et se prosterna.
9 Ya ce wa Shawulu, “Me ya sa kake saurari mutanen da suke cewa, ‘Dawuda ya dāge yă cuce ka’?
Et David dit à Saül: Pourquoi écouterais-tu les paroles des gens qui disent: Voilà, David cherche ton mal?
10 Yau ka ga da idonka yadda Ubangiji ya bashe ka a hannuna a cikin kogon nan. Waɗansu sun ce mini in kashe ka, amma na bar ka, na ce, ‘Ba zan sa hannuna a kan shugabana ba, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.’
Voici, aujourd'hui tes yeux ont vu que l'Eternel t'avait livré aujourd'hui en ma main dans la caverne, et on m'a dit que je te tuasse; mais je t'ai épargné, et j'ai dit: Je ne porterai point ma main sur mon Seigneur; car il est l'Oint de l'Eternel.
11 Babana, duba, ga shafin rigarka a hannuna, na yanke shafin rigarka amma ban kashe ka ba. Yanzu ka gane ka kuma sani cewa ba ni da laifin aikata kome ko tayarwa, ban yi maka laifi ba, amma kana farautar raina.
Regarde donc, mon père, regarde, dis-je, le pan de ton manteau qui est en ma main; car quand je coupais le pan de ton manteau, je ne t'ai point tué. Sache et connais qu'il n'y a point de mal ni d'injustice en ma main; et que je n'ai point péché contre toi; et cependant tu épies ma vie pour me l'ôter.
12 Ubangiji zai shari’anta tsakanina da kai. Ubangiji zai sāka mini laifin da ka yi mini, amma ni kam ba zan taɓa ka ba.
L'Eternel sera juge entre moi et toi, et l'Eternel me vengera de toi, mais ma main ne sera point sur toi.
13 Kamar yadda karin maganan nan na dā ya ce, ‘Daga cikin masu mugunta, mugunta ke fitowa,’ hannuna dai ba zai taɓa ka ba.
C'est des méchants que vient la méchanceté, comme dit le proverbe des anciens; c'est pourquoi ma main ne sera point sur toi.
14 “Wane ne sarkin Isra’ila, ka fito kake bi? Wa kake kora? Kana bin mataccen kare ko kuɗin cizo?
Après qui est sorti un Roi d'Israël? qui poursuis-tu? un chien mort, une puce?
15 Ubangiji yă zama alƙali, yă yi shari’a tsakanina da kai, bari Ubangiji yă duba, yă tsaya mini, yă nuna ba ni da laifi.”
L'Eternel donc sera juge, et jugera entre moi et toi; et il regardera et plaidera ma cause, et me garantira de ta main.
16 Da Dawuda ya gama wannan magana, sai Shawulu ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Sai ya fasa da kuka.
Or il arriva qu'aussitôt que David eut achevé de dire ces paroles à Saül, Saül dit: N'est-ce pas là ta voix, mon fils David? et Saül éleva sa voix, et pleura.
17 Ya ce, “Ka fi ni gaskiya, ka yi mini alheri, ni kuwa na yi maka mugunta.
Et il dit à David: Tu es plus juste que moi; car tu m'as rendu le bien pour le mal que je t'ai fait,
18 Ga shi yanzu ka faɗa mini alherin da ka yi mini. Ubangiji ya bashe ni a hannunka amma ba ka kashe ni ba.
Et tu m'as fait connaître aujourd'hui comment tu as usé de gratuité envers moi, car l'Eternel m'avait livré entre tes mains, et cependant tu ne m'as point tué.
19 In mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi yă tafi lafiya ba tare da yin masa rauni ba? Ubangiji yă sāka maka, gama ka nuna mini alheri a yau.
Or qui est-ce qui ayant trouvé son ennemi, le laisserait aller sans lui faire du mal? que l'Eternel donc te rende du bien, pour ce que tu m'as fait aujourd'hui.
20 Na sani tabbatacce za ka zama sarki. Masarautar Isra’ila za tă kahu a hannunka.
Et maintenant voici, je connais que certainement tu régneras et que le Royaume d'Israël sera ferme entre tes mains.
21 Yanzu ka rantse mini da Ubangiji cewa ba za ka hallaka zuriyarta ko ka share sunana daga iyalin mahaifina ba.”
C'est pourquoi maintenant jure-moi, par l'Eternel, que tu ne détruiras point ma race après moi, et que tu n'extermineras point mon nom de la maison de mon père.
22 Sai Dawuda ya rantse wa Shawulu. Sa’an nan Shawulu ya koma gida, amma Dawuda da mutanensa suka haura zuwa wurin ɓuya.
Et David le jura à Saül, et Saül s'en alla en sa maison; et David et ses gens montèrent dans le lieu fort.

< 1 Sama’ila 24 >