< 1 Sama’ila 24 >

1 Bayan da Shawulu ya komo daga fafaran Filistiyawa, sai aka gaya masa cewa, “Dawuda yana can a Jejin En Gedi.”
After Saul [and his soldiers] returned [home] after fighting against the Philistia army, someone reported to Saul that David [and his men] had gone into the desert near En-Gedi.
2 Saboda haka Shawulu ya zaɓi mutum dubu uku daga cikin dukan Isra’ila, suka fita neman Dawuda da mutanensa kusa da Duwatsun Awakin Jeji.
[When] Saul [heard that, he] chose 3,000 men from various areas in Israel, and they went to search for David and his men at a place named Rocks of Wild Goats.
3 Da Shawulu ya isa inda ake ajiye garken tumaki a bakin hanya inda akwai kogo, sai ya shiga ciki kogon don yă yi bayan gari. Dawuda da mutanensa kuwa suna can zaune a ƙurewar kogon.
At a place where the road was alongside some sheep pens, Saul [left the road and] entered a cave to defecate [EUP]. [He did not know that] David and his men were hiding further inside that same cave!
4 Mutanen Dawuda suka ce, wannan rana ce Ubangiji ya yi magana ya ce maka, “Zan ba da maƙiyinka a hannunka domin ka yi abin da ka ga dama da shi.” Sai Dawuda ya tashi a hankali ya je ya yanke shafin rigar Shawulu.
David’s men [saw Saul and] whispered to David, “Today is the day that Yahweh spoke about when he said, ‘I will enable you to defeat your enemy.’ You can do to him whatever you want to!” So David crept toward the entrance of the cave and [with his knife] he cut off a piece of Saul’s robe.
5 Daga baya Dawuda ya damu domin ya yanke shafin rigar Shawulu.
[And then he returned to his men]. But then David felt guilty for having cut off a piece of Saul’s robe.
6 Ya ce wa mutanensa, “Ubangiji yă sawwaƙe in yi abu haka ga shugabana da Ubangiji ya shafe, ko in ɗaga hannuna in kashe shi, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.”
He said to his men, “I should not have done that to the king! I hope/desire that Yahweh will never allow me to attack the one whom God has appointed, because Yahweh is the one who chose him [to be the king].”
7 Da wannan magana Dawuda ya kwaɓi mutanensa, bai yarda su fāɗa wa Shawulu ba. Shawulu kuwa ya bar kogon ya yi tafiyarsa.
By saying that, David restrained his men, and did not allow them to kill Saul.
8 Daga baya Dawuda ya fita daga kogon sai ya kira Shawulu ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki!” Da Shawulu ya waiwaya, sai Dawuda ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
After Saul left the cave and started to walk on the road again, David came out of the cave and shouted to Saul, “King Saul!” Saul turned around and looked, and David bowed down with his face touching the ground.
9 Ya ce wa Shawulu, “Me ya sa kake saurari mutanen da suke cewa, ‘Dawuda ya dāge yă cuce ka’?
Then he said to Saul, “(Why do you pay attention to people when they say ‘David wants to harm you’?/You should not pay attention to people when they say ‘David wants to harm you’.) [RHQ]
10 Yau ka ga da idonka yadda Ubangiji ya bashe ka a hannuna a cikin kogon nan. Waɗansu sun ce mini in kashe ka, amma na bar ka, na ce, ‘Ba zan sa hannuna a kan shugabana ba, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.’
Today you can see with your own eyes that [what they say is not true]. Yahweh put you in a place where my men and I could have killed you when you were in this cave. Some of my men told me that I should do that, but I did not do that. I said to them, ‘I will not harm my master, because he is the king whom Yahweh appointed.’
11 Babana, duba, ga shafin rigarka a hannuna, na yanke shafin rigarka amma ban kashe ka ba. Yanzu ka gane ka kuma sani cewa ba ni da laifin aikata kome ko tayarwa, ban yi maka laifi ba, amma kana farautar raina.
Your majesty, look at this piece of your robe that is in my hand! I cut it from your robe, but I did not kill you. So now you should be able to understand that I am not planning to do anything evil to you. I have not done anything wrong to you, but you are searching for me to kill me.
12 Ubangiji zai shari’anta tsakanina da kai. Ubangiji zai sāka mini laifin da ka yi mini, amma ni kam ba zan taɓa ka ba.
I hope/desire that Yahweh will judge and decide which of us ([is doing what is right/pleases him]). And I hope/desire that he will punish you for the wrong things that you have done to me. But I will not try to harm you.
13 Kamar yadda karin maganan nan na dā ya ce, ‘Daga cikin masu mugunta, mugunta ke fitowa,’ hannuna dai ba zai taɓa ka ba.
There is a proverb that has the words, ‘Evil things are done by evil people.’ But [I am not evil, so] I will not do evil things to you.
14 “Wane ne sarkin Isra’ila, ka fito kake bi? Wa kake kora? Kana bin mataccen kare ko kuɗin cizo?
“You are the king of Israel. So (why are you pursuing me?/you should not be pursuing me.) [RHQ] I am [as harmless as] [MET] a dead dog or a flea.
15 Ubangiji yă zama alƙali, yă yi shari’a tsakanina da kai, bari Ubangiji yă duba, yă tsaya mini, yă nuna ba ni da laifi.”
I hope/desire that Yahweh will judge which of us [is doing what (he wants/is right)]. I trust that he will [act like a lawyer and] judge (my case/what I have done), and that he will rescue me from your power [MTY].”
16 Da Dawuda ya gama wannan magana, sai Shawulu ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Sai ya fasa da kuka.
When David finished speaking, Saul [called out to him and] asked, “My son David, is that your voice [that I am hearing]?” Then he began to cry loudly.
17 Ya ce, “Ka fi ni gaskiya, ka yi mini alheri, ni kuwa na yi maka mugunta.
He said, “You are a better man than I am. You have done something very good to me when I tried to do something very bad to you.
18 Ga shi yanzu ka faɗa mini alherin da ka yi mini. Ubangiji ya bashe ni a hannunka amma ba ka kashe ni ba.
When Yahweh put me in a place [in that cave] where you could have easily killed me, you did not do that.
19 In mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi yă tafi lafiya ba tare da yin masa rauni ba? Ubangiji yă sāka maka, gama ka nuna mini alheri a yau.
(Who else would/No one else would) find his enemy and allow his enemy to escape [when he could kill him instead] [RHQ]. I hope/desire that Yahweh will reward you for being kindly to me today.
20 Na sani tabbatacce za ka zama sarki. Masarautar Isra’ila za tă kahu a hannunka.
I know that [some day] you will surely become the king, and that your kingdom will prosper as you rule the Israeli people.
21 Yanzu ka rantse mini da Ubangiji cewa ba za ka hallaka zuriyarta ko ka share sunana daga iyalin mahaifina ba.”
Now while Yahweh is listening, solemnly promise to me that you will not kill my family and get rid of all my descendants.”
22 Sai Dawuda ya rantse wa Shawulu. Sa’an nan Shawulu ya koma gida, amma Dawuda da mutanensa suka haura zuwa wurin ɓuya.
David solemnly promised Saul that he would not [harm Saul’s family]. Then Saul went back home, and David and his men went back up into the place where they had been hiding.

< 1 Sama’ila 24 >