< 1 Sama’ila 24 >

1 Bayan da Shawulu ya komo daga fafaran Filistiyawa, sai aka gaya masa cewa, “Dawuda yana can a Jejin En Gedi.”
And it was just when he returned Saul from after [the] Philistines and people told to him saying there! David [is] in [the] wilderness of En Gedi.
2 Saboda haka Shawulu ya zaɓi mutum dubu uku daga cikin dukan Isra’ila, suka fita neman Dawuda da mutanensa kusa da Duwatsun Awakin Jeji.
And he took Saul three thousand man chosen from all Israel and he went to seek David and men his on [the] face of [the] rocks of the mountain goats.
3 Da Shawulu ya isa inda ake ajiye garken tumaki a bakin hanya inda akwai kogo, sai ya shiga ciki kogon don yă yi bayan gari. Dawuda da mutanensa kuwa suna can zaune a ƙurewar kogon.
And he came to [the] folds of the sheep on the way and [was] there a cave and he went Saul to cover feet his and David and men his in [the] innermost parts of the cave [were] sitting.
4 Mutanen Dawuda suka ce, wannan rana ce Ubangiji ya yi magana ya ce maka, “Zan ba da maƙiyinka a hannunka domin ka yi abin da ka ga dama da shi.” Sai Dawuda ya tashi a hankali ya je ya yanke shafin rigar Shawulu.
And they said [the] men of David to him here! the day which he said Yahweh to you here! I [am] about to give (enemy your *Q(K)*) in hand your and you will do to him just as it will be good in view your and he arose David and he cut off [the] skirt of the robe which [belonged] to Saul in secrecy.
5 Daga baya Dawuda ya damu domin ya yanke shafin rigar Shawulu.
And it was after thus and it struck [the] heart of David him on that he had cut off [the] skirt which [belonged] to Saul.
6 Ya ce wa mutanensa, “Ubangiji yă sawwaƙe in yi abu haka ga shugabana da Ubangiji ya shafe, ko in ɗaga hannuna in kashe shi, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.”
And he said to men his far be it to me from Yahweh if I will do the thing this to lord my to [the] [one] anointed of Yahweh by stretching out hand my on him for [is] [the] [one] anointed of Yahweh he.
7 Da wannan magana Dawuda ya kwaɓi mutanensa, bai yarda su fāɗa wa Shawulu ba. Shawulu kuwa ya bar kogon ya yi tafiyarsa.
And he reprimanded David men his by the words and not he permitted them to rise up against Saul and Saul he arose from the cave and he went on the way.
8 Daga baya Dawuda ya fita daga kogon sai ya kira Shawulu ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki!” Da Shawulu ya waiwaya, sai Dawuda ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
And he arose David after thus and he went out (from from the cave *Q(K)*) and he called out after Saul saying O lord my the king and he looked Saul behind him and he bowed low David face [the] ground towards and he bowed down.
9 Ya ce wa Shawulu, “Me ya sa kake saurari mutanen da suke cewa, ‘Dawuda ya dāge yă cuce ka’?
And he said David to Saul why? do you listen to [the] words of someone saying there! David [is] seeking harm your.
10 Yau ka ga da idonka yadda Ubangiji ya bashe ka a hannuna a cikin kogon nan. Waɗansu sun ce mini in kashe ka, amma na bar ka, na ce, ‘Ba zan sa hannuna a kan shugabana ba, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.’
Here! the day this they have seen eyes your this: he gave you Yahweh - this day - in hand my in the cave and someone said to kill you and it looked with compassion on you and I said not I will stretch out hand my on lord my for [is] [the] [one] anointed of Yahweh he.
11 Babana, duba, ga shafin rigarka a hannuna, na yanke shafin rigarka amma ban kashe ka ba. Yanzu ka gane ka kuma sani cewa ba ni da laifin aikata kome ko tayarwa, ban yi maka laifi ba, amma kana farautar raina.
And O father my see also see [the] skirt of robe your in hand my for when cut off I [the] skirt of robe your and not I killed you know and see that there not in hand my [is] evil and transgression and not I have sinned to you and you [are] lying in wait for life my to take it.
12 Ubangiji zai shari’anta tsakanina da kai. Ubangiji zai sāka mini laifin da ka yi mini, amma ni kam ba zan taɓa ka ba.
May he judge Yahweh between me and between you and he will avenge me Yahweh from you and hand my not it will be on you.
13 Kamar yadda karin maganan nan na dā ya ce, ‘Daga cikin masu mugunta, mugunta ke fitowa,’ hannuna dai ba zai taɓa ka ba.
Just as it says [the] proverb of the ancient[s] from wicked [people] it comes forth wickedness and hand my not it will be on you.
14 “Wane ne sarkin Isra’ila, ka fito kake bi? Wa kake kora? Kana bin mataccen kare ko kuɗin cizo?
After whom? has he come out [the] king of Israel after whom? [are] you pursuing after a dog dead after a flea one.
15 Ubangiji yă zama alƙali, yă yi shari’a tsakanina da kai, bari Ubangiji yă duba, yă tsaya mini, yă nuna ba ni da laifi.”
And he will become Yahweh a judge and he will judge between me and between you and may he see and may he conduct case my and may he vindicate me from hand your.
16 Da Dawuda ya gama wannan magana, sai Shawulu ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Sai ya fasa da kuka.
And it was - when finished David to speak the words these to Saul and he said Saul ¿ voice your [is] this O son my David and he lifted up Saul voice his and he wept.
17 Ya ce, “Ka fi ni gaskiya, ka yi mini alheri, ni kuwa na yi maka mugunta.
And he said to David [are] righteous you more than I for you you have dealt out to me good and I I have dealt out to you evil.
18 Ga shi yanzu ka faɗa mini alherin da ka yi mini. Ubangiji ya bashe ni a hannunka amma ba ka kashe ni ba.
(And you *Q(K)*) you have told this day this: you have done with me good [and] this: he delivered up me Yahweh in hand your and not you killed me.
19 In mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi yă tafi lafiya ba tare da yin masa rauni ba? Ubangiji yă sāka maka, gama ka nuna mini alheri a yau.
And if he will find anyone enemy his and will he send away? him on a journey good and Yahweh may he reward you good in place of the day this [that] which you have done to me.
20 Na sani tabbatacce za ka zama sarki. Masarautar Isra’ila za tă kahu a hannunka.
And therefore here! I know that certainly you will reign and it will be established in hand your [the] kingdom of Israel.
21 Yanzu ka rantse mini da Ubangiji cewa ba za ka hallaka zuriyarta ko ka share sunana daga iyalin mahaifina ba.”
And therefore swear an oath! to me by Yahweh if you will cut off offspring my after me and if you will destroy name my from [the] house of father my.
22 Sai Dawuda ya rantse wa Shawulu. Sa’an nan Shawulu ya koma gida, amma Dawuda da mutanensa suka haura zuwa wurin ɓuya.
And he swore an oath David to Saul and he went Saul to house his and David and men his they went up to the stronghold.

< 1 Sama’ila 24 >