< 1 Sama’ila 24 >

1 Bayan da Shawulu ya komo daga fafaran Filistiyawa, sai aka gaya masa cewa, “Dawuda yana can a Jejin En Gedi.”
And it came to pass, when Saul was returned from pursuing the Philistines, that it was told to him, saying, Behold, David is in the wilderness of 'En-gedi.
2 Saboda haka Shawulu ya zaɓi mutum dubu uku daga cikin dukan Isra’ila, suka fita neman Dawuda da mutanensa kusa da Duwatsun Awakin Jeji.
Then took Saul three thousand chosen men out of all Israel, and went to seek David and his men upon the rocks of the wild goats.
3 Da Shawulu ya isa inda ake ajiye garken tumaki a bakin hanya inda akwai kogo, sai ya shiga ciki kogon don yă yi bayan gari. Dawuda da mutanensa kuwa suna can zaune a ƙurewar kogon.
And he came to the sheepfolds by the way, and there was a cave; and Saul went in to cover his feet: and David and his men were sitting in the lower end of the cave.
4 Mutanen Dawuda suka ce, wannan rana ce Ubangiji ya yi magana ya ce maka, “Zan ba da maƙiyinka a hannunka domin ka yi abin da ka ga dama da shi.” Sai Dawuda ya tashi a hankali ya je ya yanke shafin rigar Shawulu.
And the men of David said unto him, Behold, this is the day of which the Lord hath said unto thee, Behold, I will deliver thy enemy into thy hand, that thou mayest do to him as it shall seem good in thy eyes. And David arose, and cut off the corner of the robe which Saul wore, unperceived.
5 Daga baya Dawuda ya damu domin ya yanke shafin rigar Shawulu.
And it came to pass afterward, that David's heart smote him, because he had cut off the corner of Saul's [robe].
6 Ya ce wa mutanensa, “Ubangiji yă sawwaƙe in yi abu haka ga shugabana da Ubangiji ya shafe, ko in ɗaga hannuna in kashe shi, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.”
And he said unto his men, Far be it from me for the Lord's sake, that I should do this thing unto my master, the Lord's anointed, to stretch forth my hand against him; because he is the anointed of the Lord.
7 Da wannan magana Dawuda ya kwaɓi mutanensa, bai yarda su fāɗa wa Shawulu ba. Shawulu kuwa ya bar kogon ya yi tafiyarsa.
So David restrained his servants with these words, and suffered them not to rise against Saul. But Saul rose up out of the cave, and went on his way.
8 Daga baya Dawuda ya fita daga kogon sai ya kira Shawulu ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki!” Da Shawulu ya waiwaya, sai Dawuda ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
David also arose afterward, and went forth out of the cave, and called after Saul, saying, My Lord, the king! And Saul then looked behind him, and David bowed his face to the earth, and prostrated himself.
9 Ya ce wa Shawulu, “Me ya sa kake saurari mutanen da suke cewa, ‘Dawuda ya dāge yă cuce ka’?
And David said to Saul, Wherefore wilt thou listen to men's words, saying, Behold, David seeketh thy injury?
10 Yau ka ga da idonka yadda Ubangiji ya bashe ka a hannuna a cikin kogon nan. Waɗansu sun ce mini in kashe ka, amma na bar ka, na ce, ‘Ba zan sa hannuna a kan shugabana ba, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.’
Behold, this day thy eyes have seen how that the Lord had delivered thee today into my hand in the cave, and some one said that I should kill thee: but my soul felt compassion for thee: and I said, I will not stretch forth my hand against my Lord; because he is the anointed of the Lord.
11 Babana, duba, ga shafin rigarka a hannuna, na yanke shafin rigarka amma ban kashe ka ba. Yanzu ka gane ka kuma sani cewa ba ni da laifin aikata kome ko tayarwa, ban yi maka laifi ba, amma kana farautar raina.
And now, my father, see, yea, see the corner of thy robe in my hand; for in that I cut off the corner of thy robe, and killed thee not, know thou and see that there is neither evil nor transgression in my hand, and that I have not sinned against thee: yet thou liest in wait for my soul to take it.
12 Ubangiji zai shari’anta tsakanina da kai. Ubangiji zai sāka mini laifin da ka yi mini, amma ni kam ba zan taɓa ka ba.
May the Lord judge between me and thee, and may the Lord avenge me on thee; but my hand shall not be against thee.
13 Kamar yadda karin maganan nan na dā ya ce, ‘Daga cikin masu mugunta, mugunta ke fitowa,’ hannuna dai ba zai taɓa ka ba.
As saith the proverb of the ancients, From the wicked proceedeth wickedness; but my hand shall not be against thee.
14 “Wane ne sarkin Isra’ila, ka fito kake bi? Wa kake kora? Kana bin mataccen kare ko kuɗin cizo?
After whom is the king of Israel gone out? after whom art thou pursuing? after a dead dog, after a single flea.
15 Ubangiji yă zama alƙali, yă yi shari’a tsakanina da kai, bari Ubangiji yă duba, yă tsaya mini, yă nuna ba ni da laifi.”
May the Lord therefore be judge, and decide between me and thee, and see, and plead my cause, and obtain me justice out of thy hand.
16 Da Dawuda ya gama wannan magana, sai Shawulu ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Sai ya fasa da kuka.
And it came to pass, When David had finished speaking these words unto Saul, that Saul said, Is this thy voice, my son David? And Saul lifted up his voice, and wept.
17 Ya ce, “Ka fi ni gaskiya, ka yi mini alheri, ni kuwa na yi maka mugunta.
And he said to David, Thou art more righteous than I; for thou hast done for me only what is good, whereas I have rewarded thee only with what is evil.
18 Ga shi yanzu ka faɗa mini alherin da ka yi mini. Ubangiji ya bashe ni a hannunka amma ba ka kashe ni ba.
And thou hast proved this day, that thou hast dealt well with me; forasmuch as when the Lord had surrendered me into thy hand, thou didst not kill me.
19 In mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi yă tafi lafiya ba tare da yin masa rauni ba? Ubangiji yă sāka maka, gama ka nuna mini alheri a yau.
For if a man find his enemy, will he let him go away on a good road? so may the Lord reward thee with good for what thou hast done unto me this day.
20 Na sani tabbatacce za ka zama sarki. Masarautar Isra’ila za tă kahu a hannunka.
And now, behold, I know that thou wilt surely become king, and that the kingdom of Israel will stand firmly in thy hand.
21 Yanzu ka rantse mini da Ubangiji cewa ba za ka hallaka zuriyarta ko ka share sunana daga iyalin mahaifina ba.”
And now swear unto me by the Lord, that thou wilt not cut off my seed after me, and that thou wilt not destroy my name out of my father's house.
22 Sai Dawuda ya rantse wa Shawulu. Sa’an nan Shawulu ya koma gida, amma Dawuda da mutanensa suka haura zuwa wurin ɓuya.
And David swore unto Saul; and Saul went to his house; but David and his men went up into the strong-hold.

< 1 Sama’ila 24 >