< 1 Sama’ila 23 >
1 Sa’ad da aka ce wa Dawuda, “Duba ga Filistiyawa suna yaƙi da mutanen Keyila, suna kwashe musu hatsi a masussukai.”
Davudus xabar abayle: – Filiştinar Qeilalqa k'yoptul, maadın attabı vod q'əra qa'a.
2 Sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya ce, “In tafi in fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi?” Ubangiji kuwa ya ce masa, “Jeka ka yi yaƙi da Filistiyawa, ka ceci Keyila.”
Davudee Rəbbike qiyghanan: – Hark'ın Filiştinaaşika səyxene? Rəbbee Davuduk'le eyhen: – Hudoora k'yootle, Filiştinaaşike Qeila g'attivxhan hee'e.
3 Amma mutanen Dawuda suka ce masa, “Ga shi, a nan ma a Yahuda muna jin tsoro, balle mu tafi Keyila mu yi yaƙi da sojojin Filistiyawa!”
Davudne insanaaşemee, Davuduk'le eyhen: – Şi inyaa'acab, Yahudayne cigabışeecab q'əvəyq'ən. Filiştinaaşde Qeilayeene g'oşunbışde ögeeqa şi nəxübne qığeepç'es?
4 Dawuda ya sāke nemi nufin Ubangiji, sai Ubangiji ya ce masa, “Tashi ka gangara zuwa Keyila, gama zan ba da Filistiyawa a hannunka.”
Davudee meed Rəbbike qiyghan, Rəbbeeyid mang'uk'le eyhen: – Oza qıxha Qeilayeeqa hak'ne. Zı Filiştinar yiğne xılyaqa qevles.
5 Sa’an nan Dawuda da mutanensa suka tafi Keyila, suka yi yaƙi da Filistiyawa, suka kwashe musu shanunsu, suka jijji wa Filistiyawa ƙwarai, suka cece mutanen Keyila daga hannunsu.
Davudun insanar Qeilayeeqa hapk'ın, maane Filiştinaaşilqa k'yoohar. Manbışin çavra-vəq'ə Davudee g'ahayşu qıkkekkan. Davudee Filiştınbışilqa ver ablyav'u, Qeilayn millet g'attixhan ha'an.
6 (Abiyatar ɗan Ahimelek ya zo da efod sa’ad da ya gudo zuwa wurin Dawuda a Keyila.)
(Mançile oğiylid Aximelekne dixee Evyataree Qeilayeeqa Davudne k'anyaqa g'adayxhvan qöömee, kaahinaaşin ileylığ adayle.)
7 Shawulu ya sami labari cewa Dawuda ya tafi Keyila, sai ya ce, “Allah ya bashe shi a hannuna, domin Dawuda ya kulle kansa ke nan da ya shiga birnin da yake da ƙofofin da ake kulle da ƙarafa.”
Davud Qeilayeeqa arıva Şaululqa hixhar ha'an. Şaulee eyhen: – Allaheecar mana yizde xılyaqa quvu. Mana ç'ak'ın akkabınaneyiy sat'ulbınane şahareeqa ikkeç'u, vucee cun ögü ı'xı'.
8 Shawulu ya kira dukan sojojinsa don yaƙi, su gangaro zuwa Keyila su mamaye Dawuda da mutanensa.
Şaulee Qeilayee Davudıy cukan insanar avqasva, gırgına g'oşun dəv'əys sa'a.
9 Da Dawuda ya ji labari Shawulu yana shirya hanyar da zai kashe shi, sai ya ce wa Abiyatar firist, “Kawo mini efod a nan.”
Davuduk'le Şaulee cuk qəlasın ha'as ıxhay ats'anniy. Mang'vee kaahin Evyatarık'le eyhen: – Kaahinaaşin ileylığ inyaqa qale.
10 Dawuda ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bawanka ya sami labari cewa tabbatacce Shawulu yana shirin zuwa Keyila yă hallaka garin saboda ni.
Davudeecad meed sak'ı, eyhen: – İzrailyna Allah eyxhena, Rəbb, zak'le g'ayxhiyn, zal-alla Şaulus Qeilayeeqa arı şahar q'əra qaa'asıb vukkan.
11 Mutanen Keyila za su bashe ni a gare shi? Shawulu zai gangaro nan kamar yadda bawanka ya sami labari? Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka gaya wa bawanka.” Ubangiji ya ce, “Zai zo.”
Qeilayne milletın zı mang'une xılyaqa qelesdaniyxan? Zak'le, Yiğne nukarık'le, g'ayxhiyn ixhesınne, Şaul inyaqa ayresdane? İzrailyna Allah eyxhena, Rəbb, hucoona ixhes, man zak'le eyhe. Rəbbee «Mana ayresdava» alidghıniy qele.
12 Dawuda ya sāke cewa, “Mutanen Keyila za su bashe ni da mutanena ga Shawulu?” Ubangiji ya ce, “Za su yi.”
Mane gahıl Davudee meed qiyghanan: – Qeilayne milletın, zınayiy yizın insanar mang'une xılyaqa qevlesınbıniyxan? Rəbbee «Qevlesınbıva» eyhe.
13 Saboda haka Dawuda da mutanensa wajen mutum ɗari shida suka bar Keyila, suka yi ta tafiya daga wannan wuri zuwa wancan. Sa’ad da aka gaya wa Shawulu cewa Dawuda ya tsere daga Keyila, sai ya fasa tafiya can.
Davud yixhıd vəşşılqa ələəne insanıka Qeilayeençe qığeç'u, inyaa-şa axva giyğal. Davud Qeilayeençe hixu ark'ınnava, Şaululqa hixhar hı'ımee, mang'vee cuna fıkır badal haa'ana, maqa hayk'an deş.
14 Dawuda ya zauna a jeji cikin kogunan duwatsu da kuma tuddan jejin Zif. Kowace rana Shawulu ya yi ta neman Dawuda amma Allah bai bashe Dawuda a hannunsa ba.
Davud xılyaqa gidexhasde xhinene cigabışee, Zif eyhene sahrayne tepabışee axva eyxhe. Şaulee mana yiğıscar t'abal ha'a ıxha, Allaheemee Davud mang'une xılyaqa gixhas haysar deş.
15 A lokacin da Dawuda yana zaune a Horesh cikin jejin Zif, ya sami labari cewa Shawulu ya fito don yă kashe shi.
Davud Zifne sahreene Xoreşnang'a mang'uk'le g'iyxhen, Şaulee vucur gik'asva t'abal ha'a.
16 Yonatan ɗan Shawulu kuwa ya tafi wurin Dawuda a Horesh, ya ƙarfafa shi yă dogara ga Allah.
Şaulna dix Yonatan Xoreşeeqa Davudne k'anyaqa arı, mang'us Allahne doyule yik'bı hele.
17 Ya ce, “Kada ka ji tsoro, mahaifina Shawulu ba zai taɓa sa hannu a kanka ba. Za ka zama sarki a Isra’ila, ni kuma in zama na biyu gare ka. Kai, ko mahaifina Shawulu ma ya san da haka.”
Davuduk'le mang'vee eyhen: – Qı'məyq'ən, yizde dekkıne Şaulne xılyaqa ğu gixhas deş. Ğu İzrailyna paççah ixhes, zınar vale qiyğiyna q'ör'esda insan. Man yizde dekkık'le Şauluk'led çikana ats'an.
18 Su biyunsu kuwa suka ɗaura yarjejjeniya a gaban Ubangiji. Sai Yonatan ya koma gida amma Dawuda ya zauna Horesh.
Qiyğa manbışde q'öng'eesana sana-sang'us Rəbbine ögil cuvab hele. Mançe Yonatan ayk'anna xaaqa, Davudur Xoreş axva.
19 Zifawa suka tafi wurin Shawulu a Gibeya suka ce masa, “Ashe, ba Dawuda ne yake ɓuya a cikinmu a kogwannin duwatsu a Horesh a bisan tudun Hakila, kudu da Yeshimon ba?
Zifğançenbı Giveayeeqa Şaulusqa abı, eyhen: – Davud yişde k'anene, Yeşimonne canubılyne Xakilayne tepalyne Xoreşee xıl hidixharasde cigabışee dyugulyxha vor.
20 Yanzu, ya sarki, ka gangaro, ka zo a duk lokacin da ka ga ya yi maka, ka zo mu kuma hakkinmu ne mu bashe shi a hannun sarki.”
Paççah, vas mısayiy ıkkan, maqa ayre, şicar aqqı mana yiğne xılyaqa qelesda.
21 Shawulu ya ce, “Ubangiji ya yi muku albarka, gama kun damu da ni.
Şaulee eyhen: – Zas yugvalla hav'uynçil-alla, Rəbbee şos barakat helecen.
22 Ku tafi ku ƙara shiri. Ku san inda yakan tafi, wane ne kuma ya gan shi a can. An gaya mini cewa shi mai wayo ne sosai.
Sayıb hapk'ın yugda ats'axhxhe, mang'vee g'el nyaqayiy gixhxhı, şavuk'leyiy mana maa'ar g'acu. Zak'le mana süvə xhinnena insan vorva g'ayxhı.
23 Ku binciko duk wuraren da yakan ɓuya, sai ku dawo ku gaya mini tabbataccen labari. Sa’an nan zan tafi tare da ku in yana can. Zan nemi shi ko’ina cikin dukan kabilar Yahuda.”
Mana dyugulexhen cigabı gırgınbı ats'axhxhe, yugda ats'axhxhad, zasqa savk'le. Zınar maqa şoka ı'qqəsda. Mana nimeletteyiy ine ölkee Yahudee, zı mana gırgınəəng'ə t'abal ha'asda. Mana inçeğana ixheene, mana zı Yahudavolle gırgınəəng'ə t'abal ha'asda.
24 Sai suka tashi suka koma Zif, suka sha gaban Shawulu. Dawuda da mutanensa kuwa suna jejin Mawon cikin Araba, kudu da Yeshimon.
Zifğançenbı oza qeepxha Şaulne ögee Zifqa avayk'an. Davudıy cun insanar Yeşimonne canubılyne, Arava eyhene cigayne Maonne sahree vuxha.
25 Shawulu da mutanensa suka tafi neman Dawuda. Da Dawuda ya ji labari, sai ya gangara cikin duwatsu ya zauna a cikin jejin Mawon. Sa’ad da Shawulu ya ji haka, sai ya tafi jejin Mawon yana fafaran Dawuda.
Şaulıy cun insanar mana t'abal ha'asva, mane cigeeqa havayk'an. Man Davudulqa hixhar hı'ımee, mana ganznane cigeeqa qarı, Maonne sahree ulyoyzar. Şauluk'le man ats'axhxhamee, Maonne sahree Davuduqar qihna gexha.
26 Shawulu yana tafiya a gefe ɗaya na dutsen, Dawuda da mutanensa kuma suna a wancan gefe, suna hanzari su ɓace wa Shawulu. Sa’ad da Shawulu da sojojinsa suka kusa cimma Dawuda da mutanensa don su kama su,
Şaul cune insanaaşika suvane ine surale, Davudur cune insanaaşika suvane şene surale əlyhəə vooxhe. Davudus, Şaulıle hixu, dyugulyxhes ıkkiykan. Şaulusmee mang'un ögü ı'xı', mana aqqas ıkkiykan.
27 sai wani manzo ya zo wurin Shawulu yana cewa, “Ka koma da sauri, Filistiyawa sun kawo wa ƙasar hari.”
Mane gahıl Şaulusqa xabar ana sa insan arı eyhen: – Zaara ixhe, yı'q'əlqa sak'le, yişde ölkalqa Filiştinar k'yoptul.
28 Shawulu kuwa ya janye daga fafaran Dawuda, ya tafi yă ƙara da Filistiyawa. Dalilin ke nan da ake kiran wannan wuri Sela Hammalekot, wato, dutsen tserewa.
Şaulee, Davuduqa qihna girxhuy g'aletçu, mançe ayk'anna Filiştinaaşika səyxəs. Mançil-alla mane cigays Sela-Hammaxleqotva (Curepxhayn Ganz) do giyxhe.
29 Dawuda kuwa ya haura daga can ya zauna a kogwannin duwatsun En Gedi.
Davud mançe En-Gedi eyhene cigeene xıl hidixharasde cigabışeeqa ayk'an.