< 1 Sama’ila 23 >

1 Sa’ad da aka ce wa Dawuda, “Duba ga Filistiyawa suna yaƙi da mutanen Keyila, suna kwashe musu hatsi a masussukai.”
Ja Davidille ilmoitettiin, sanoen: katso, Philistealaiset sotivat Kegilaa vastaan ja ryöstävät heidän riihensä.
2 Sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya ce, “In tafi in fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi?” Ubangiji kuwa ya ce masa, “Jeka ka yi yaƙi da Filistiyawa, ka ceci Keyila.”
Niin David kysyi Herralta ja sanoi: pitääkö minun menemän ja lyömän näitä Philistealaisia? Ja Herra sanoi Davidille: mene, lyö Philistealaiset ja vapahda Kegila.
3 Amma mutanen Dawuda suka ce masa, “Ga shi, a nan ma a Yahuda muna jin tsoro, balle mu tafi Keyila mu yi yaƙi da sojojin Filistiyawa!”
Ja Davidin miehet sanoivat hänelle: katso, me pelkäämme täällä Juudassa, ja menemme vielä Kegilaan Philistealaisten sotajoukon tykö.
4 Dawuda ya sāke nemi nufin Ubangiji, sai Ubangiji ya ce masa, “Tashi ka gangara zuwa Keyila, gama zan ba da Filistiyawa a hannunka.”
Niin David taas kysyi Herralta, ja Herra vastasi häntä ja sanoi: nouse ja mene alas Kegilaan; sillä minä annan Philistealaiset sinun käsiis.
5 Sa’an nan Dawuda da mutanensa suka tafi Keyila, suka yi yaƙi da Filistiyawa, suka kwashe musu shanunsu, suka jijji wa Filistiyawa ƙwarai, suka cece mutanen Keyila daga hannunsu.
Niin David meni ja hänen miehensä Kegilaan, ja soti Philistealaisia vastaan, ja ajoi heidän karjansa pois, ja tappoi heitä suurella tapolla; ja niin David vapahti Kegilan asuvaiset.
6 (Abiyatar ɗan Ahimelek ya zo da efod sa’ad da ya gudo zuwa wurin Dawuda a Keyila.)
Mutta kuin Abjatar Ahimelekin poika pakeni Davidin tykö Kegilaan, vei hän sinne myötänsä päällisvaatteen.
7 Shawulu ya sami labari cewa Dawuda ya tafi Keyila, sai ya ce, “Allah ya bashe shi a hannuna, domin Dawuda ya kulle kansa ke nan da ya shiga birnin da yake da ƙofofin da ake kulle da ƙarafa.”
Niin sanottiin Saulille Davidin tulleeksi Kegilaan; ja Saul sanoi: Jumala on antanut hänen minun käsiini, että hän on salvattu, nyt hän on tullut kaupunkiin, joka on varustettu porteilla ja teljillä.
8 Shawulu ya kira dukan sojojinsa don yaƙi, su gangaro zuwa Keyila su mamaye Dawuda da mutanensa.
Ja Saul kuulutti kaiken kansan sotaan Kegilaan, piirittämään Davidia miehinensä.
9 Da Dawuda ya ji labari Shawulu yana shirya hanyar da zai kashe shi, sai ya ce wa Abiyatar firist, “Kawo mini efod a nan.”
Kuin David ymmärsi Saulin aikovan pahaa hänellensä, sanoi hän papille Abjatarille: ota päällisvaate.
10 Dawuda ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bawanka ya sami labari cewa tabbatacce Shawulu yana shirin zuwa Keyila yă hallaka garin saboda ni.
Ja David sanoi: Herra Israelin Jumala! sinun palvelias on tosin kuullut Saulin aikovan tulla Kegilaan, hävittämään minun tähteni kaupunkia;
11 Mutanen Keyila za su bashe ni a gare shi? Shawulu zai gangaro nan kamar yadda bawanka ya sami labari? Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka gaya wa bawanka.” Ubangiji ya ce, “Zai zo.”
Antanevatko Kegilan asuvaiset minun hänen käsiinsä? ja tulleeko Saul tänne niinkuin palvelias on kuullut? Herra Israelin Jumala, ilmoita se palvelialles! Ja Herra sanoi: hän tulee alas.
12 Dawuda ya sāke cewa, “Mutanen Keyila za su bashe ni da mutanena ga Shawulu?” Ubangiji ya ce, “Za su yi.”
Ja David sanoi: antanevatko Kegilan asuvaiset minun ja minun väkeni Saulin käsiin? Herra sanoi: antavat.
13 Saboda haka Dawuda da mutanensa wajen mutum ɗari shida suka bar Keyila, suka yi ta tafiya daga wannan wuri zuwa wancan. Sa’ad da aka gaya wa Shawulu cewa Dawuda ya tsere daga Keyila, sai ya fasa tafiya can.
Niin David nousi miehinensä, joita oli liki kuusisataa miestä, ja läksivät Kegilasta ja vaelsivat sinne mihinkä he vaaeltaa taisivat. Koska Saulille sanottiin Davidin paenneen Kegilasta, lakkasi hän sinne menemästä.
14 Dawuda ya zauna a jeji cikin kogunan duwatsu da kuma tuddan jejin Zif. Kowace rana Shawulu ya yi ta neman Dawuda amma Allah bai bashe Dawuda a hannunsa ba.
Ja David pysyi korvessa linnoissa, viipyi myös Siphin korven vuorella. Ja Saul etsi häntä joka aika, mutta ei Jumala antanut häntä hänen käsiinsä.
15 A lokacin da Dawuda yana zaune a Horesh cikin jejin Zif, ya sami labari cewa Shawulu ya fito don yă kashe shi.
Ja David näki Saulin lähteneeksi etsimään hänen henkensä perään, vaan David pysyi Siphin korvessa, yhdessä metsässä.
16 Yonatan ɗan Shawulu kuwa ya tafi wurin Dawuda a Horesh, ya ƙarfafa shi yă dogara ga Allah.
Niin Jonatan Saulin poika nousi ja meni Davidin tykö metsään, ja vahvisti hänen kätensä Jumalassa,
17 Ya ce, “Kada ka ji tsoro, mahaifina Shawulu ba zai taɓa sa hannu a kanka ba. Za ka zama sarki a Isra’ila, ni kuma in zama na biyu gare ka. Kai, ko mahaifina Shawulu ma ya san da haka.”
Ja sanoi hänelle: älä pelkää, sillä ei minun isäni Saulin käsi löydä sinua, ja sinä tule Israelin kuninkaaksi, ja minä olen likin sinua; ja sen myös Saul minun isäni kyllä tietää.
18 Su biyunsu kuwa suka ɗaura yarjejjeniya a gaban Ubangiji. Sai Yonatan ya koma gida amma Dawuda ya zauna Horesh.
Ja he molemmat tekivät liiton keskenänsä Herran edessä; ja David pysyi metsässä, mutta Jonatan palasi kotiansa.
19 Zifawa suka tafi wurin Shawulu a Gibeya suka ce masa, “Ashe, ba Dawuda ne yake ɓuya a cikinmu a kogwannin duwatsu a Horesh a bisan tudun Hakila, kudu da Yeshimon ba?
Mutta Siphiläiset menivät ylös Saulin tykö Gibeaan ja sanoivat: eikö David ole kätketty meidän tykönämme linnoissa metsässä, Hakilan kukkulalla, liki korpea oikialla puolella?
20 Yanzu, ya sarki, ka gangaro, ka zo a duk lokacin da ka ga ya yi maka, ka zo mu kuma hakkinmu ne mu bashe shi a hannun sarki.”
Niin tule nyt kuningas kiiruusti alas kaiken sydämes himon jälkeen: ja me annamme hänen kuninkaan käsiin.
21 Shawulu ya ce, “Ubangiji ya yi muku albarka, gama kun damu da ni.
Ja Saul sanoi: olkaat te siunatut Herrassa, että te armahditte minun päälleni.
22 Ku tafi ku ƙara shiri. Ku san inda yakan tafi, wane ne kuma ya gan shi a can. An gaya mini cewa shi mai wayo ne sosai.
Menkäät siis ja tutkikaat paremmin, että te saisitte tietää ja nähdä sen paikan, jossa hänen jalkansa ovat, ja kuka hänen siellä on nähnyt; sillä minulle on hän sanottu sangen kavalaksi.
23 Ku binciko duk wuraren da yakan ɓuya, sai ku dawo ku gaya mini tabbataccen labari. Sa’an nan zan tafi tare da ku in yana can. Zan nemi shi ko’ina cikin dukan kabilar Yahuda.”
Tutkistelkaat ja vaotkaat kaikki salaiset paikat, joihin hän lymyttää itsensä, ja tulkaat jälleen minun tyköni, kuin saatte vahvan tiedon; niin minä menen teidän kanssanne. Jos hän tällä maalla on, niin minä hänen etsin kaikkein tuhanten seasta Juudassa.
24 Sai suka tashi suka koma Zif, suka sha gaban Shawulu. Dawuda da mutanensa kuwa suna jejin Mawon cikin Araba, kudu da Yeshimon.
Ja he nousivat ja menivät Siphiin Saulin edellä. Mutta David ja hänen miehensä olivat Maonin korvessa, oikialla puolella korpea, kedolla.
25 Shawulu da mutanensa suka tafi neman Dawuda. Da Dawuda ya ji labari, sai ya gangara cikin duwatsu ya zauna a cikin jejin Mawon. Sa’ad da Shawulu ya ji haka, sai ya tafi jejin Mawon yana fafaran Dawuda.
Kuin Saul matkusti sinne väkinensä etsimään häntä, ja se ilmoitettiin Davidille, meni hän kukkulalta alas, ja oli Maonin korvessa. Ja kuin Saul sen kuuli, ajoi hän Davidia takaa Maonin korvessa.
26 Shawulu yana tafiya a gefe ɗaya na dutsen, Dawuda da mutanensa kuma suna a wancan gefe, suna hanzari su ɓace wa Shawulu. Sa’ad da Shawulu da sojojinsa suka kusa cimma Dawuda da mutanensa don su kama su,
Ja Saul meni yhdeltä puolelta vuorta, ja David väkinensä toiselta puolelta vuorta. Ja koska David riensi pakenemaan Saulin edestä, piiritti Saul väkinensä Davidin ja hänen väkensä, ottaaksensa heitä kiinni.
27 sai wani manzo ya zo wurin Shawulu yana cewa, “Ka koma da sauri, Filistiyawa sun kawo wa ƙasar hari.”
Mutta sanansaattaja tuli Saulin tykö ja sanoi: kiiruhda sinuas ja tule nopiasti; sillä Philistealaiset ovat maalle tulleet.
28 Shawulu kuwa ya janye daga fafaran Dawuda, ya tafi yă ƙara da Filistiyawa. Dalilin ke nan da ake kiran wannan wuri Sela Hammalekot, wato, dutsen tserewa.
Nin Saul palasi ajamasta Davidia takaa ja meni Philistealaisia vastaan; sentähden kutsutaan se paikka SelaMahelkot.
29 Dawuda kuwa ya haura daga can ya zauna a kogwannin duwatsun En Gedi.
Ja David meni sieltä ylös ja asui EnGedin linnoissa.

< 1 Sama’ila 23 >