< 1 Sama’ila 23 >

1 Sa’ad da aka ce wa Dawuda, “Duba ga Filistiyawa suna yaƙi da mutanen Keyila, suna kwashe musu hatsi a masussukai.”
One day someone told David, “You need to know that the Philistia army is attacking Keilah [town] and they are stealing grain from where men are threshing it.”
2 Sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya ce, “In tafi in fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi?” Ubangiji kuwa ya ce masa, “Jeka ka yi yaƙi da Filistiyawa, ka ceci Keyila.”
David asked Yahweh, “Should my men and I go to fight against those men from the Philistia people-group?” Yahweh answered, “Yes, go. Attack them, and rescue the people of Keilah.”
3 Amma mutanen Dawuda suka ce masa, “Ga shi, a nan ma a Yahuda muna jin tsoro, balle mu tafi Keyila mu yi yaƙi da sojojin Filistiyawa!”
But David’s men said to him, “We are afraid [that Saul will attack us] here in Judah. We will be more afraid if we go to Keilah where the Philistia army is!”
4 Dawuda ya sāke nemi nufin Ubangiji, sai Ubangiji ya ce masa, “Tashi ka gangara zuwa Keyila, gama zan ba da Filistiyawa a hannunka.”
So David asked Yahweh again [if they should go to Keilah]. Yahweh answered, “Yes, go down to Keilah. I will help you to defeat the men of the Philistia people-group.”
5 Sa’an nan Dawuda da mutanensa suka tafi Keyila, suka yi yaƙi da Filistiyawa, suka kwashe musu shanunsu, suka jijji wa Filistiyawa ƙwarai, suka cece mutanen Keyila daga hannunsu.
So David and his men went to Keilah. They fought against the men of the Philistia people-group and captured many of their cattle. David and his men killed many of the Philistia men and rescued the people of Keilah.
6 (Abiyatar ɗan Ahimelek ya zo da efod sa’ad da ya gudo zuwa wurin Dawuda a Keyila.)
Abiathar, the son of Ahimelech, fled to be with David at Keilah, and he brought the sacred vest with him [to use it to determine what God wanted to be done].
7 Shawulu ya sami labari cewa Dawuda ya tafi Keyila, sai ya ce, “Allah ya bashe shi a hannuna, domin Dawuda ya kulle kansa ke nan da ya shiga birnin da yake da ƙofofin da ake kulle da ƙarafa.”
Soon Saul found out that David was at Keilah. So he said, “That is good! God is enabling me to capture him! He has trapped himself in that town, because it has high walls with gates around it.”
8 Shawulu ya kira dukan sojojinsa don yaƙi, su gangaro zuwa Keyila su mamaye Dawuda da mutanensa.
So Saul summoned his army, and they prepared to go down to Keilah to attack David and his men.
9 Da Dawuda ya ji labari Shawulu yana shirya hanyar da zai kashe shi, sai ya ce wa Abiyatar firist, “Kawo mini efod a nan.”
But David found out that Saul was planning [for his army] to attack him. So he said to Abiathar the priest, “Bring [here] the sacred vest.”
10 Dawuda ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bawanka ya sami labari cewa tabbatacce Shawulu yana shirin zuwa Keyila yă hallaka garin saboda ni.
[So when Abiathar brought it, ] David prayed, “Yahweh, God of us Israelis, I have heard that Saul is planning to come here [with his army] and destroy Keilah because I am here.
11 Mutanen Keyila za su bashe ni a gare shi? Shawulu zai gangaro nan kamar yadda bawanka ya sami labari? Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka gaya wa bawanka.” Ubangiji ya ce, “Zai zo.”
Will Saul come down [here to Keilah], as people reported to me? Will the leaders of Keilah enable Saul to capture me? Yahweh, God of us Israelis, please tell me!” Yahweh answered, “Yes, Saul will come down.”
12 Dawuda ya sāke cewa, “Mutanen Keyila za su bashe ni da mutanena ga Shawulu?” Ubangiji ya ce, “Za su yi.”
Then David asked, “Will the leaders of Keilah enable Saul’s army to capture me and my men [if we stay here]?” [By means of the stones in the sacred vest], Yahweh replied, “Yes, they will.”
13 Saboda haka Dawuda da mutanensa wajen mutum ɗari shida suka bar Keyila, suka yi ta tafiya daga wannan wuri zuwa wancan. Sa’ad da aka gaya wa Shawulu cewa Dawuda ya tsere daga Keyila, sai ya fasa tafiya can.
So David and his 600 men left Keilah. They continued to move from one place to another, [wherever they thought that Saul would not find them]. And when Saul found out that David had escaped from Keilah, he did not go there.
14 Dawuda ya zauna a jeji cikin kogunan duwatsu da kuma tuddan jejin Zif. Kowace rana Shawulu ya yi ta neman Dawuda amma Allah bai bashe Dawuda a hannunsa ba.
David and his men stayed in hiding places in the desert and in the hills of Ziph Desert. Every day Saul [sent men to] search for David, but Yahweh did not allow them to capture David.
15 A lokacin da Dawuda yana zaune a Horesh cikin jejin Zif, ya sami labari cewa Shawulu ya fito don yă kashe shi.
While David and his men were at [a place named] Horesh in Ziph desert, he found out that Saul was coming there to kill him.
16 Yonatan ɗan Shawulu kuwa ya tafi wurin Dawuda a Horesh, ya ƙarfafa shi yă dogara ga Allah.
But Saul’s son Jonathan went to David at Horesh, and encouraged him to continue to trust [God].
17 Ya ce, “Kada ka ji tsoro, mahaifina Shawulu ba zai taɓa sa hannu a kanka ba. Za ka zama sarki a Isra’ila, ni kuma in zama na biyu gare ka. Kai, ko mahaifina Shawulu ma ya san da haka.”
Jonathan told him, “Do not be afraid, because my father will not be able to harm [IDM] you. [Some day] you will be the king of Israel, and I will be the second [most important man in Israel]. My father Saul also knows that.”
18 Su biyunsu kuwa suka ɗaura yarjejjeniya a gaban Ubangiji. Sai Yonatan ya koma gida amma Dawuda ya zauna Horesh.
Then the two of them repeated their solemn promise that Yahweh [had heard them make previously, that they would always be loyal to each other]. Then Jonathan went home, but David stayed at Horesh.
19 Zifawa suka tafi wurin Shawulu a Gibeya suka ce masa, “Ashe, ba Dawuda ne yake ɓuya a cikinmu a kogwannin duwatsu a Horesh a bisan tudun Hakila, kudu da Yeshimon ba?
Some people from Ziph went to Saul when he was at Gibeah, and they told him, “David [and his men] are hiding in our land [RHQ]! They are hiding in places at Horesh on Hakilah Hill, south of [a place named] Jeshimon.
20 Yanzu, ya sarki, ka gangaro, ka zo a duk lokacin da ka ga ya yi maka, ka zo mu kuma hakkinmu ne mu bashe shi a hannun sarki.”
So, O king, come down there any time that you want to. It is our duty to capture him and turn him over to you.”
21 Shawulu ya ce, “Ubangiji ya yi muku albarka, gama kun damu da ni.
Saul replied, “I hope/desire that Yahweh will bless you [for telling that to me].
22 Ku tafi ku ƙara shiri. Ku san inda yakan tafi, wane ne kuma ya gan shi a can. An gaya mini cewa shi mai wayo ne sosai.
Go back and find out more about him. Find out exactly where he is staying, and find out who has seen him there. People tell me that he is very clever, [so we need to be clever also to be able to capture him].
23 Ku binciko duk wuraren da yakan ɓuya, sai ku dawo ku gaya mini tabbataccen labari. Sa’an nan zan tafi tare da ku in yana can. Zan nemi shi ko’ina cikin dukan kabilar Yahuda.”
Find out all the places where he and his men hide. Then come back and tell me everything that you have found out. Then I will [take my army and] go there with you. If David is in any of the clans/caves of Judah, we will search for him [and find him]!”
24 Sai suka tashi suka koma Zif, suka sha gaban Shawulu. Dawuda da mutanensa kuwa suna jejin Mawon cikin Araba, kudu da Yeshimon.
So those people went back to Ziph before Saul went there. At that time David and his men were in Maon Desert, south of Jeshimon.
25 Shawulu da mutanensa suka tafi neman Dawuda. Da Dawuda ya ji labari, sai ya gangara cikin duwatsu ya zauna a cikin jejin Mawon. Sa’ad da Shawulu ya ji haka, sai ya tafi jejin Mawon yana fafaran Dawuda.
Saul and his soldiers went to search for David, but David heard about that. So he and his men went further [south] to a rocky hill/peak in the Maon Desert. When Saul heard about that, he and his men followed David and his men to the Maon Desert.
26 Shawulu yana tafiya a gefe ɗaya na dutsen, Dawuda da mutanensa kuma suna a wancan gefe, suna hanzari su ɓace wa Shawulu. Sa’ad da Shawulu da sojojinsa suka kusa cimma Dawuda da mutanensa don su kama su,
Saul and his soldiers were walking along one side of the hill/peak, and David and his men were on the other side. David and his men were hurrying to escape from Saul’s soldiers, because Saul and his soldiers were coming much closer.
27 sai wani manzo ya zo wurin Shawulu yana cewa, “Ka koma da sauri, Filistiyawa sun kawo wa ƙasar hari.”
But then a messenger came to Saul and said to him, “Come quickly! The Philistia army is attacking the people in our land!”
28 Shawulu kuwa ya janye daga fafaran Dawuda, ya tafi yă ƙara da Filistiyawa. Dalilin ke nan da ake kiran wannan wuri Sela Hammalekot, wato, dutsen tserewa.
So Saul stopped pursuing David, and he [and his soldiers] went to fight against the Philistia army. That is the reason that people call that place ‘Escape Rock’.
29 Dawuda kuwa ya haura daga can ya zauna a kogwannin duwatsun En Gedi.
David and his men also left the Maon Desert and went to places to hide safely at En-Gedi.

< 1 Sama’ila 23 >