< 1 Sama’ila 23 >

1 Sa’ad da aka ce wa Dawuda, “Duba ga Filistiyawa suna yaƙi da mutanen Keyila, suna kwashe musu hatsi a masussukai.”
Then told they David, saying, —Lo! the Philistines are fighting against Keilah, and they are plundering the threshing-floors.
2 Sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya ce, “In tafi in fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi?” Ubangiji kuwa ya ce masa, “Jeka ka yi yaƙi da Filistiyawa, ka ceci Keyila.”
So David enquired of Yahweh, saying, Shall I go and smite these Philistines? And Yahweh said unto David—Go, and smite the Philistines, and save Keilah.
3 Amma mutanen Dawuda suka ce masa, “Ga shi, a nan ma a Yahuda muna jin tsoro, balle mu tafi Keyila mu yi yaƙi da sojojin Filistiyawa!”
But the men of David said unto him, Lo! we, here, in Judah, are afraid, —how much more, then, if we go to Keilah, against the ranks of the Philistines?
4 Dawuda ya sāke nemi nufin Ubangiji, sai Ubangiji ya ce masa, “Tashi ka gangara zuwa Keyila, gama zan ba da Filistiyawa a hannunka.”
So David yet again enquired if Yahweh, and Yahweh answered him, —and said—Arise, go down to Keilah, for I am about to deliver the Philistines into thy hand.
5 Sa’an nan Dawuda da mutanensa suka tafi Keyila, suka yi yaƙi da Filistiyawa, suka kwashe musu shanunsu, suka jijji wa Filistiyawa ƙwarai, suka cece mutanen Keyila daga hannunsu.
David therefore went, with his men, to Keilah, and fought with the Philistines, and drave forth their cattle, and smote them, with a great smiting, so David saved the inhabitants of Keilah.
6 (Abiyatar ɗan Ahimelek ya zo da efod sa’ad da ya gudo zuwa wurin Dawuda a Keyila.)
Now it came to pass, when Abiathar, son of Ahimelech, fled unto David to Keilah, that he came down with, an ephod, in his hand.
7 Shawulu ya sami labari cewa Dawuda ya tafi Keyila, sai ya ce, “Allah ya bashe shi a hannuna, domin Dawuda ya kulle kansa ke nan da ya shiga birnin da yake da ƙofofin da ake kulle da ƙarafa.”
And, when it was told Saul that David had entered Keilah, Saul said—God hath given him over into my hand, for he hath shut himself in by entering into a city with folding doors and bar.
8 Shawulu ya kira dukan sojojinsa don yaƙi, su gangaro zuwa Keyila su mamaye Dawuda da mutanensa.
So Saul summoned all the people to war, —to go down to Keilah, to besiege David, and his men.
9 Da Dawuda ya ji labari Shawulu yana shirya hanyar da zai kashe shi, sai ya ce wa Abiyatar firist, “Kawo mini efod a nan.”
And David ascertained that, against him, Saul was contriving mischief, —so he said unto Abiathar the priest, Bring hither the ephod.
10 Dawuda ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bawanka ya sami labari cewa tabbatacce Shawulu yana shirin zuwa Keyila yă hallaka garin saboda ni.
Then said David: O Yahweh, God of Israel, thy servant, hath heard, that Saul is seeking to come unto Keilah, —to destroy the city, for my sake:
11 Mutanen Keyila za su bashe ni a gare shi? Shawulu zai gangaro nan kamar yadda bawanka ya sami labari? Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka gaya wa bawanka.” Ubangiji ya ce, “Zai zo.”
Will the owners of Keilah surrender me into his hand? Will Saul come down, as thy servant hath heard? O Yahweh, God of Israel, I pray thee, tell thy servant. And Yahweh said—He will come down.
12 Dawuda ya sāke cewa, “Mutanen Keyila za su bashe ni da mutanena ga Shawulu?” Ubangiji ya ce, “Za su yi.”
Then said David, Will the owners of Keilah surrender me and my men, into the hand of Saul? And Yahweh said—They will surrender.
13 Saboda haka Dawuda da mutanensa wajen mutum ɗari shida suka bar Keyila, suka yi ta tafiya daga wannan wuri zuwa wancan. Sa’ad da aka gaya wa Shawulu cewa Dawuda ya tsere daga Keyila, sai ya fasa tafiya can.
Then arose David and his men, about six hundred, and went forth out of Keilah, and went to and fro, whithersoever they could, —and, unto Saul, it was told that David had escaped out of Keilah, so he forbare to go forth.
14 Dawuda ya zauna a jeji cikin kogunan duwatsu da kuma tuddan jejin Zif. Kowace rana Shawulu ya yi ta neman Dawuda amma Allah bai bashe Dawuda a hannunsa ba.
Then David abode in the wilderness, in the fortresses, and he abode in the hill country, in the wilderness of Ziph. And Saul sought him continually, but God delivered him not into his hand.
15 A lokacin da Dawuda yana zaune a Horesh cikin jejin Zif, ya sami labari cewa Shawulu ya fito don yă kashe shi.
Then David saw that Saul had come out to seek his life, David, being in the wilderness of Ziph, in the thicket.
16 Yonatan ɗan Shawulu kuwa ya tafi wurin Dawuda a Horesh, ya ƙarfafa shi yă dogara ga Allah.
So Jonathan, Saul’s son, arose and went unto David in the thicket, —and strengthened his hand in God;
17 Ya ce, “Kada ka ji tsoro, mahaifina Shawulu ba zai taɓa sa hannu a kanka ba. Za ka zama sarki a Isra’ila, ni kuma in zama na biyu gare ka. Kai, ko mahaifina Shawulu ma ya san da haka.”
and said unto him, —Do not fear, for the hand of Saul my father shall not find thee, but, thou, shalt become king over Israel, and, I, shall be, next, unto thee, yea and, Saul my father, knoweth this.
18 Su biyunsu kuwa suka ɗaura yarjejjeniya a gaban Ubangiji. Sai Yonatan ya koma gida amma Dawuda ya zauna Horesh.
And they two solemnised a covenant before Yahweh, —and David remained in the thicket, but, Jonathan, departed to his own house.
19 Zifawa suka tafi wurin Shawulu a Gibeya suka ce masa, “Ashe, ba Dawuda ne yake ɓuya a cikinmu a kogwannin duwatsu a Horesh a bisan tudun Hakila, kudu da Yeshimon ba?
Then came up the Ziphites unto Saul in Gibeah, saying, —Is not David hiding himself with us, in the strongholds in the thicket, in the hill of Hachilah, which is on the right of Jeshimon?
20 Yanzu, ya sarki, ka gangaro, ka zo a duk lokacin da ka ga ya yi maka, ka zo mu kuma hakkinmu ne mu bashe shi a hannun sarki.”
Now, therefore, according to all the desire of thy soul O king, to come down, come! and, ours, [will it be] to surrender him into the hand of the king.
21 Shawulu ya ce, “Ubangiji ya yi muku albarka, gama kun damu da ni.
Then said Saul, Blessed, be ye, of Yahweh, —because ye have taken pity upon me.
22 Ku tafi ku ƙara shiri. Ku san inda yakan tafi, wane ne kuma ya gan shi a can. An gaya mini cewa shi mai wayo ne sosai.
Go, I pray you, make ready yet further, and get to know and see his place, where may be his track, who hath seen him there, —for it hath been said unto me, Cunning indeed, is, he!
23 Ku binciko duk wuraren da yakan ɓuya, sai ku dawo ku gaya mini tabbataccen labari. Sa’an nan zan tafi tare da ku in yana can. Zan nemi shi ko’ina cikin dukan kabilar Yahuda.”
See, then, and get to know—of all the hiding places, where he hideth himself, and return unto me, for certainty, then will I go with you, —and it shall be, if he is in the land, that I will search him out, through all the thousands of Judah.
24 Sai suka tashi suka koma Zif, suka sha gaban Shawulu. Dawuda da mutanensa kuwa suna jejin Mawon cikin Araba, kudu da Yeshimon.
So they arose and departed to Ziph, before Saul, —but, David and his men, were in the wilderness of Maon, in the Arabah, to the right of Jeshimon.
25 Shawulu da mutanensa suka tafi neman Dawuda. Da Dawuda ya ji labari, sai ya gangara cikin duwatsu ya zauna a cikin jejin Mawon. Sa’ad da Shawulu ya ji haka, sai ya tafi jejin Mawon yana fafaran Dawuda.
Then Saul and his men departed, to seek [him]; but it had been told David, and he had gone down the cliff, and taken up his abode in the wilderness of Maon, —and when Saul had, heard it, he pursued David in the wilderness of Maon.
26 Shawulu yana tafiya a gefe ɗaya na dutsen, Dawuda da mutanensa kuma suna a wancan gefe, suna hanzari su ɓace wa Shawulu. Sa’ad da Shawulu da sojojinsa suka kusa cimma Dawuda da mutanensa don su kama su,
And Saul went on this side of the mountain, and, David and his men, on that side of the mountain, —wherefore David became hurried, to get away from the presence of Saul, but, Saul and his men, were surrounding David and his men, to capture then:
27 sai wani manzo ya zo wurin Shawulu yana cewa, “Ka koma da sauri, Filistiyawa sun kawo wa ƙasar hari.”
when, a messenger, came unto Saul, saying, —Haste thee and come! for the Philistines have spread over the land.
28 Shawulu kuwa ya janye daga fafaran Dawuda, ya tafi yă ƙara da Filistiyawa. Dalilin ke nan da ake kiran wannan wuri Sela Hammalekot, wato, dutsen tserewa.
Then returned Saul from pursuing David, and departed to meet the Philistines, —for which cause, they called that place Sela-hammahlekoth ["the Cliff of Separation"].
29 Dawuda kuwa ya haura daga can ya zauna a kogwannin duwatsun En Gedi.
And David went up from thence, —and abode in the strongholds of En-gedi.

< 1 Sama’ila 23 >