< 1 Sama’ila 23 >

1 Sa’ad da aka ce wa Dawuda, “Duba ga Filistiyawa suna yaƙi da mutanen Keyila, suna kwashe musu hatsi a masussukai.”
And they told David, saying: Behold the Philistines fight against Ceila, and they rob the barns.
2 Sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya ce, “In tafi in fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi?” Ubangiji kuwa ya ce masa, “Jeka ka yi yaƙi da Filistiyawa, ka ceci Keyila.”
Therefore David consulted the Lord, saying: Shall I go and smite these Philistines? And the Lord said to David: Go, and thou shalt smite the Philistines, and shalt save Ceila.
3 Amma mutanen Dawuda suka ce masa, “Ga shi, a nan ma a Yahuda muna jin tsoro, balle mu tafi Keyila mu yi yaƙi da sojojin Filistiyawa!”
And the men that were with David, said to him: Behold we are in fear here in Judea, how much more if we go to Ceila against the hands of the Philistines?
4 Dawuda ya sāke nemi nufin Ubangiji, sai Ubangiji ya ce masa, “Tashi ka gangara zuwa Keyila, gama zan ba da Filistiyawa a hannunka.”
Therefore David consulted the Lord again. And he answered and said to him: Arise, and go to Ceila: for I will deliver the Philistines into thy hand.
5 Sa’an nan Dawuda da mutanensa suka tafi Keyila, suka yi yaƙi da Filistiyawa, suka kwashe musu shanunsu, suka jijji wa Filistiyawa ƙwarai, suka cece mutanen Keyila daga hannunsu.
David therefore, and his men, went to Ceila, and fought against the Philistines, and brought away their cattle, and made a great slaughter of them: and David saved the inhabitants of Ceila.
6 (Abiyatar ɗan Ahimelek ya zo da efod sa’ad da ya gudo zuwa wurin Dawuda a Keyila.)
Now at that time, when Abiathar the son of Achimelech fled to David to Ceila, he came down having an ephod with him.
7 Shawulu ya sami labari cewa Dawuda ya tafi Keyila, sai ya ce, “Allah ya bashe shi a hannuna, domin Dawuda ya kulle kansa ke nan da ya shiga birnin da yake da ƙofofin da ake kulle da ƙarafa.”
And it was told Saul that David was come to Ceila: and Saul said: The Lord hath delivered him into my hands, and he is shut up, being come into a city, that hath gates and bars.
8 Shawulu ya kira dukan sojojinsa don yaƙi, su gangaro zuwa Keyila su mamaye Dawuda da mutanensa.
And Saul commanded all the people to go down to fight against Ceila, and to besiege David, and his men.
9 Da Dawuda ya ji labari Shawulu yana shirya hanyar da zai kashe shi, sai ya ce wa Abiyatar firist, “Kawo mini efod a nan.”
Now when David understood, that Saul secretly prepared evil against him, he said to Abiathar the priest: Bring hither the ephod.
10 Dawuda ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bawanka ya sami labari cewa tabbatacce Shawulu yana shirin zuwa Keyila yă hallaka garin saboda ni.
And David said: O Lord God of Israel, thy servant hath heard a report, that Saul designeth to come to Ceila, to destroy the city for my sake:
11 Mutanen Keyila za su bashe ni a gare shi? Shawulu zai gangaro nan kamar yadda bawanka ya sami labari? Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka gaya wa bawanka.” Ubangiji ya ce, “Zai zo.”
Will the men of Ceila deliver me into his hands? and will Saul come down, as thy servant hath heard? O Lord God of Israel, tell thy servant. And the Lord said: He will come down.
12 Dawuda ya sāke cewa, “Mutanen Keyila za su bashe ni da mutanena ga Shawulu?” Ubangiji ya ce, “Za su yi.”
And David said: Will the men of Ceila deliver me, and my men, into the hands of Saul? And the Lord said: They will deliver thee up.
13 Saboda haka Dawuda da mutanensa wajen mutum ɗari shida suka bar Keyila, suka yi ta tafiya daga wannan wuri zuwa wancan. Sa’ad da aka gaya wa Shawulu cewa Dawuda ya tsere daga Keyila, sai ya fasa tafiya can.
Then David and his men, who were about six hundred, arose, and departing from Ceila, wandered up and down uncertain where they should stay: and it was told Saul that David was fled from Ceila, and had escaped: wherefore he forbore to go out.
14 Dawuda ya zauna a jeji cikin kogunan duwatsu da kuma tuddan jejin Zif. Kowace rana Shawulu ya yi ta neman Dawuda amma Allah bai bashe Dawuda a hannunsa ba.
But David abode in the desert in strong holds, and he remained in a mountain of the desert of Ziph, in a woody hill. And Saul sought him always: but the Lord delivered him not into his hands.
15 A lokacin da Dawuda yana zaune a Horesh cikin jejin Zif, ya sami labari cewa Shawulu ya fito don yă kashe shi.
And David saw that Saul was come out to seek his life. And David was in the desert of Ziph, in a wood.
16 Yonatan ɗan Shawulu kuwa ya tafi wurin Dawuda a Horesh, ya ƙarfafa shi yă dogara ga Allah.
And Jonathan the son of Saul arose, and went to David into the wood, and strengthened his hands in God: and he said to him:
17 Ya ce, “Kada ka ji tsoro, mahaifina Shawulu ba zai taɓa sa hannu a kanka ba. Za ka zama sarki a Isra’ila, ni kuma in zama na biyu gare ka. Kai, ko mahaifina Shawulu ma ya san da haka.”
Fear not: for the hand of my father Saul shall not find thee, and thou shalt reign over Israel, and I shall be next to thee, yea, and my father knoweth this.
18 Su biyunsu kuwa suka ɗaura yarjejjeniya a gaban Ubangiji. Sai Yonatan ya koma gida amma Dawuda ya zauna Horesh.
And the two made a covenant before the Lord: and David abode in the wood: but Jonathan returned to his house.
19 Zifawa suka tafi wurin Shawulu a Gibeya suka ce masa, “Ashe, ba Dawuda ne yake ɓuya a cikinmu a kogwannin duwatsu a Horesh a bisan tudun Hakila, kudu da Yeshimon ba?
And the Ziphites went up to Saul in Gabaa, saying: Lo, doth not David lie hid with us in the strong holds of the wood, in mount Hachila, which is on the right hand of the desert.
20 Yanzu, ya sarki, ka gangaro, ka zo a duk lokacin da ka ga ya yi maka, ka zo mu kuma hakkinmu ne mu bashe shi a hannun sarki.”
Now therefore come down, as thy soul hath desired to come down: and it shall be our business to deliver him into the king’s hands.
21 Shawulu ya ce, “Ubangiji ya yi muku albarka, gama kun damu da ni.
And Saul said: Blessed be ye of the Lord, for you have pitied my case.
22 Ku tafi ku ƙara shiri. Ku san inda yakan tafi, wane ne kuma ya gan shi a can. An gaya mini cewa shi mai wayo ne sosai.
Go therefore, I pray you, and use all diligence, and curiously inquire, and consider the place where his foot is, and who hath seen him there: for he thinketh of me, that I lie craftily in wait for him.
23 Ku binciko duk wuraren da yakan ɓuya, sai ku dawo ku gaya mini tabbataccen labari. Sa’an nan zan tafi tare da ku in yana can. Zan nemi shi ko’ina cikin dukan kabilar Yahuda.”
Consider and see all his lurking holes, wherein he is bid, and return to me with the certainty of the thing, that I may go with you. And if be should even go down into the earth to hide himself, I will search him out in all the thousands of Juda.
24 Sai suka tashi suka koma Zif, suka sha gaban Shawulu. Dawuda da mutanensa kuwa suna jejin Mawon cikin Araba, kudu da Yeshimon.
And they arose and went to Ziph before Saul: and David and his men were in the desert of Maon, in the plain at the right hand of Jesimon.
25 Shawulu da mutanensa suka tafi neman Dawuda. Da Dawuda ya ji labari, sai ya gangara cikin duwatsu ya zauna a cikin jejin Mawon. Sa’ad da Shawulu ya ji haka, sai ya tafi jejin Mawon yana fafaran Dawuda.
Then Saul and his men went to seek him: and it was told David, and forthwith he went down to the rock, and abode in the wilderness of Maon: and when Saul had heard of it he pursued after David in the wilderness of Maon.
26 Shawulu yana tafiya a gefe ɗaya na dutsen, Dawuda da mutanensa kuma suna a wancan gefe, suna hanzari su ɓace wa Shawulu. Sa’ad da Shawulu da sojojinsa suka kusa cimma Dawuda da mutanensa don su kama su,
And Saul went on this side of the mountain: and David and his men were on the other side of the mountain: and David despaired of being able to escape from the face of Saul: and Saul and his men encompassed David and his men round about to take them.
27 sai wani manzo ya zo wurin Shawulu yana cewa, “Ka koma da sauri, Filistiyawa sun kawo wa ƙasar hari.”
And a messenger came to Saul, saying: Make haste to come, for the Philistines have poured in themselves upon the land.
28 Shawulu kuwa ya janye daga fafaran Dawuda, ya tafi yă ƙara da Filistiyawa. Dalilin ke nan da ake kiran wannan wuri Sela Hammalekot, wato, dutsen tserewa.
Wherefore Saul returned, leaving the pursuit of David, and went to meet the Philistines. For this cause they called that place, the Rock of division.
29 Dawuda kuwa ya haura daga can ya zauna a kogwannin duwatsun En Gedi.
Then David went up from thence, and dwelt in strong holds of Engaddi.

< 1 Sama’ila 23 >