< 1 Sama’ila 23 >

1 Sa’ad da aka ce wa Dawuda, “Duba ga Filistiyawa suna yaƙi da mutanen Keyila, suna kwashe musu hatsi a masussukai.”
Javiše onda Davidu: “Filistejci opsjedaju Keilu i pljačkaju gumna.”
2 Sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya ce, “In tafi in fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi?” Ubangiji kuwa ya ce masa, “Jeka ka yi yaƙi da Filistiyawa, ka ceci Keyila.”
David tada upita Jahvu: “Treba li da idem na Filistejce i hoću li ih potući?” A Jahve odgovori Davidu: “Idi, potući ćeš Filistejce i oslobodit ćeš Keilu.”
3 Amma mutanen Dawuda suka ce masa, “Ga shi, a nan ma a Yahuda muna jin tsoro, balle mu tafi Keyila mu yi yaƙi da sojojin Filistiyawa!”
Ali rekoše Davidu ljudi njegovi: “Gle, mi smo već ovdje, u Judi, u neprestanom strahu; što će tek biti ako odemo u Keilu protiv filistejskih četa!”
4 Dawuda ya sāke nemi nufin Ubangiji, sai Ubangiji ya ce masa, “Tashi ka gangara zuwa Keyila, gama zan ba da Filistiyawa a hannunka.”
Zato David još jednom upita Jahvu, a Jahve mu odgovori ovako: “Ustani i siđi u Keilu jer ću predati Filistejce u tvoje ruke!”
5 Sa’an nan Dawuda da mutanensa suka tafi Keyila, suka yi yaƙi da Filistiyawa, suka kwashe musu shanunsu, suka jijji wa Filistiyawa ƙwarai, suka cece mutanen Keyila daga hannunsu.
David onda krenu sa svojim ljudima u Keilu, udari na Filistejce, otjera njihovu stoku i zada im težak poraz. Tako je David oslobodio građane Keile. -
6 (Abiyatar ɗan Ahimelek ya zo da efod sa’ad da ya gudo zuwa wurin Dawuda a Keyila.)
Kad je ono Ebjatar, Ahimelekov sin, pobjegao k Davidu, on je došao u Keilu noseći u ruci oplećak.
7 Shawulu ya sami labari cewa Dawuda ya tafi Keyila, sai ya ce, “Allah ya bashe shi a hannuna, domin Dawuda ya kulle kansa ke nan da ya shiga birnin da yake da ƙofofin da ake kulle da ƙarafa.”
Kad su Šaulu javili da je David ušao u Keilu, reče Šaul: “Bog ga je predao u moje ruke jer se sam uhvatio u zamku kad je ušao u grad s vratima i prijevornicama.”
8 Shawulu ya kira dukan sojojinsa don yaƙi, su gangaro zuwa Keyila su mamaye Dawuda da mutanensa.
I Šaul sazva sav narod na oružje da ide na Keilu i da opkoli Davida i njegove ljude.
9 Da Dawuda ya ji labari Shawulu yana shirya hanyar da zai kashe shi, sai ya ce wa Abiyatar firist, “Kawo mini efod a nan.”
Kad je David doznao da mu Šaul snuje zlo, reče svećeniku Ebjataru: “Donesi oplećak!”
10 Dawuda ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bawanka ya sami labari cewa tabbatacce Shawulu yana shirin zuwa Keyila yă hallaka garin saboda ni.
Nato se David pomoli: “Jahve, Bože Izraelov, tvoj je sluga čuo da Šaul sprema navalu na Keilu da razori grad zbog mene.
11 Mutanen Keyila za su bashe ni a gare shi? Shawulu zai gangaro nan kamar yadda bawanka ya sami labari? Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka gaya wa bawanka.” Ubangiji ya ce, “Zai zo.”
Hoće li Šaul doći kao što je tvoj sluga čuo? Jahve, Bože Izraelov, odgovori svome sluzi!” A Jahve odgovori: “Doći će!”
12 Dawuda ya sāke cewa, “Mutanen Keyila za su bashe ni da mutanena ga Shawulu?” Ubangiji ya ce, “Za su yi.”
David opet upita: “Hoće li me prvaci Keile predati, mene i moje ljude, u Šaulove ruke?” A Jahve odgovori: “Predat će vas!”
13 Saboda haka Dawuda da mutanensa wajen mutum ɗari shida suka bar Keyila, suka yi ta tafiya daga wannan wuri zuwa wancan. Sa’ad da aka gaya wa Shawulu cewa Dawuda ya tsere daga Keyila, sai ya fasa tafiya can.
Tada David ustade sa svojim ljudima, bijaše ih oko šest stotina; iziđoše iz Keile te lutahu kojekuda. A kad su Šaulu javili da je David utekao iz Keile, odusta od vojnog pohoda.
14 Dawuda ya zauna a jeji cikin kogunan duwatsu da kuma tuddan jejin Zif. Kowace rana Shawulu ya yi ta neman Dawuda amma Allah bai bashe Dawuda a hannunsa ba.
David se skloni u pustinju u gorska skloništa; nastani se na gori u pustinji Zifu. Šaul ga je neprestano tražio, ali ga Bog ne predade u njegove ruke.
15 A lokacin da Dawuda yana zaune a Horesh cikin jejin Zif, ya sami labari cewa Shawulu ya fito don yă kashe shi.
David se bojao što je Šaul izišao na vojnu da napadne na njegov život. Zato je David ostao u pustinji Zifu, u Horši.
16 Yonatan ɗan Shawulu kuwa ya tafi wurin Dawuda a Horesh, ya ƙarfafa shi yă dogara ga Allah.
Tada Šaulov sin Jonatan krenu na put i dođe k Davidu u Horšu i ohrabri ga u ime Božje.
17 Ya ce, “Kada ka ji tsoro, mahaifina Shawulu ba zai taɓa sa hannu a kanka ba. Za ka zama sarki a Isra’ila, ni kuma in zama na biyu gare ka. Kai, ko mahaifina Shawulu ma ya san da haka.”
Reče mu: “Ne boj se, jer te neće stići ruka moga oca Šaula. Ti ćeš kraljevati nad Izraelom, a ja ću biti drugi do tebe; i moj otac Šaul zna to dobro.”
18 Su biyunsu kuwa suka ɗaura yarjejjeniya a gaban Ubangiji. Sai Yonatan ya koma gida amma Dawuda ya zauna Horesh.
I sklopiše njih dvojica savez pred Jahvom. David osta u Horši, a Jonatan ode svojoj kući.
19 Zifawa suka tafi wurin Shawulu a Gibeya suka ce masa, “Ashe, ba Dawuda ne yake ɓuya a cikinmu a kogwannin duwatsu a Horesh a bisan tudun Hakila, kudu da Yeshimon ba?
Jednoga dana dođoše Zifejci k Šaulu u Gibeu i javiše mu: “David se krije kod nas u gorskim skloništima u Horši, na brdu Hakili, što je južno od Ješimona.
20 Yanzu, ya sarki, ka gangaro, ka zo a duk lokacin da ka ga ya yi maka, ka zo mu kuma hakkinmu ne mu bashe shi a hannun sarki.”
Sada, kralju, kad god zaželiš sići, siđi, a naše je da ga predamo u ruke kralju.”
21 Shawulu ya ce, “Ubangiji ya yi muku albarka, gama kun damu da ni.
A Šaul odgovori: “Blagoslovio vas Jahve što ste me požalili!
22 Ku tafi ku ƙara shiri. Ku san inda yakan tafi, wane ne kuma ya gan shi a can. An gaya mini cewa shi mai wayo ne sosai.
Idite, dakle, raspitajte se još i dobro razvidite mjesto kamo ga donesu njegovi hitri koraci; rekli su mi da je vrlo lukav.
23 Ku binciko duk wuraren da yakan ɓuya, sai ku dawo ku gaya mini tabbataccen labari. Sa’an nan zan tafi tare da ku in yana can. Zan nemi shi ko’ina cikin dukan kabilar Yahuda.”
Zato pretražite sve rupe u koje se zavlači, pa se vratite k meni kad budete pouzdano znali. Tada ću ja poći s vama, pa ako bude gdje u zemlji, ići ću za njegovim tragom po svim Judinim rodovima.”
24 Sai suka tashi suka koma Zif, suka sha gaban Shawulu. Dawuda da mutanensa kuwa suna jejin Mawon cikin Araba, kudu da Yeshimon.
Tada krenuše na put i odoše u Zif, pred Šaulom. David je sa svojim ljudima bio u pustinji Maonu u Arabi, južno od Ješimona.
25 Shawulu da mutanensa suka tafi neman Dawuda. Da Dawuda ya ji labari, sai ya gangara cikin duwatsu ya zauna a cikin jejin Mawon. Sa’ad da Shawulu ya ji haka, sai ya tafi jejin Mawon yana fafaran Dawuda.
Potom i Šaul pođe sa svojim ljudima da traži Davida. Kad su to javili Davidu, siđe on u klanac koji leži u pustinji Maonu. Šaul to doznade i krenu u potjeru za Davidom u pustinju Maon.
26 Shawulu yana tafiya a gefe ɗaya na dutsen, Dawuda da mutanensa kuma suna a wancan gefe, suna hanzari su ɓace wa Shawulu. Sa’ad da Shawulu da sojojinsa suka kusa cimma Dawuda da mutanensa don su kama su,
Šaul je sa svojim ljudima išao jednom stranom planine, a David sa svojim ljudima drugom stranom planine. David se silno žurio da umakne Šaulu. Kad je Šaul sa svojim ljudima htio prijeći na drugu stranu da opkoli Davida i njegove ljude i da ih pohvata,
27 sai wani manzo ya zo wurin Shawulu yana cewa, “Ka koma da sauri, Filistiyawa sun kawo wa ƙasar hari.”
dođe glasnik Šaulu s porukom: “Dođi brže, Filistejci provališe u zemlju!”
28 Shawulu kuwa ya janye daga fafaran Dawuda, ya tafi yă ƙara da Filistiyawa. Dalilin ke nan da ake kiran wannan wuri Sela Hammalekot, wato, dutsen tserewa.
Tada Šaul odusta od potjere za Davidom i okrenu se protiv Filistejaca. Zato se prozvalo ono mjesto “Klanac razlaza”.
29 Dawuda kuwa ya haura daga can ya zauna a kogwannin duwatsun En Gedi.
David se odande uspe i nastani u engadskim gorskim skloništima.

< 1 Sama’ila 23 >